< Ƙidaya 12 >
1 Miriyam da Haruna suka fara zargin Musa saboda matarsa’yar ƙasar Kush da ya aura.
And Miriam and Aaron spake against Moses, on account of the Cushite woman whom he had taken, —for, a Cushite woman, had he taken.
2 Suka ce, “Ubangiji ya yi magana ta wurin Musa ne kaɗai? Ashe, bai yi magana ta wurinmu mu ma ba?” Ubangiji kuwa ya ji wannan.
And they said: Is it only and solely with Moses, that Yahweh hath spoken? With us also, hath he not spoken? And Yahweh heard it.
3 (Musa kuwa mutum ne mai tawali’u ƙwarai, mafi tawali’u fiye da kowane mutum a duniya.)
Now, the man Moses, was patient, exceedingly, —above all the sons of earth, who were on the face of the ground.
4 Nan da nan Ubangiji ya ce wa Musa, da Haruna da kuma Miriyam, “Ku fita ku tafi Tentin Sujada, dukanku uku.” Sai dukansu uku suka tafi.
Then said Yahweh suddenly, unto Moses, and unto Aaron, and unto Miriam, Come out ye three unto the tent of meeting. And they three went out.
5 Sai Ubangiji ya sauko a cikin ginshiƙin girgije; ya tsaya a bakin ƙofar Tenti, ya kira Haruna da Miriyam. Sa’ad da su biyu suka gusa gaba,
Then Yahweh came down in a pillar of cloud, and stood at the entrance of the tent, —and called Aaron and Miriam, and they both went forth.
6 sai ya ce, “Ku ji abin da zan faɗa, “Duk lokacin da akwai annabin Ubangiji a cikinku, nakan bayyana kaina gare shi cikin wahayi, in yi magana da shi cikin mafarkai.
Then said he Hear, I beseech you my words. When ye have your prophet, As Yahweh in a vision, will I make myself known, unto him; In a dream, will I speak with him.
7 Amma ba haka nake magana da Musa bawana ba; na sa shi yă lura da dukan jama’ata Isra’ila.
Not so, my servant Moses, —In all my house, trusty, is he:
8 Da shi nake magana fuska da fuska, a fili kuma, ba a kacici-kacici ba; yakan ga siffar Ubangiji. To, me ya sa ba ku ji tsoro ku yi magana a kan bawana Musa ba?”
Mouth to mouth, do I speak with him And plainly—not in dark sayings, And the form of Yahweh, doth he discern, —Wherefore then, were ye not afraid to speak against my servant—against Moses?
9 Sai fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kansu, ya kuma rabu da su.
And the anger of Yahweh kindled upon them and he departed.
10 Da girgijen ya tashi daga bisa Tentin, sai ga Miriyam tsaye, kuturwa, fari fat. Haruna kuwa ya juya wajenta ya ga ta kuturce;
And, when, the cloud, removed from off the tent, —lo! Miriam, leprous, like snow! And Aaron turned unto Miriam and lo! …leprous!
11 sai Haruna ya ce wa Musa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka hukunta mu, gama zunubin da muka yi, mun yi ne cikin wauta.
Then said Aaron unto Moses, —Oh my lord, do not I beseech thee lay upon us sin, although we have made ourselves foolish, and although we have sinned.
12 Kada ka sa ta zama kamar haifaffen mataccen jariri daga cikin mahaifiya wanda rabin jikin ruɓaɓɓe ne.”
Let her not, I beseech thee, remain like the still-born, —which when it is born of its mother, the half of its flesh is consumed.
13 Saboda haka sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Allah, ina roƙonka ka warkar da ita!”
Then Moses made outcry unto Yahweh, saying, —O GOD, I beseech thee grant healing. I beseech thee unto her.
14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Da a ce mahaifinta ne ya tofa mata miyau a fuskarta, ashe, ba za tă ji kunya har kwana bakwai ba? A fitar da ita bayan sansani kwana bakwai; bayan haka za a iya dawo da ita.”
And Yahweh said unto Moses: If, her own father, had, but spat, in her face, would she not, have acknowledged the shame for seven days? Let her shut herself up for seven days, outside the camp, and afterwards, let her be received back.
15 Haka aka fitar da Miriyam bayan sansani kwana bakwai, mutane kuwa ba su ci gaba da tafiya ba sai da aka dawo da ita.
So Miriam shut herself up, outside the camp, for seven days, —and, the people, set not forward, until Miriam had been received back.
16 Bayan haka sai mutane suka bar Hazerot suka sauka a Hamadan Faran.
Then afterwards, did the people set forward from Hazeroth, and encamped in the desert of Paran.