< Ƙidaya 12 >

1 Miriyam da Haruna suka fara zargin Musa saboda matarsa’yar ƙasar Kush da ya aura.
Miriam and Aaron were critical of Moses because of his Ethiopian wife—he'd married an Ethiopian woman.
2 Suka ce, “Ubangiji ya yi magana ta wurin Musa ne kaɗai? Ashe, bai yi magana ta wurinmu mu ma ba?” Ubangiji kuwa ya ji wannan.
“Is it only through Moses that the Lord speaks?” they asked. “Doesn't he speak through us too?” The Lord heard all this.
3 (Musa kuwa mutum ne mai tawali’u ƙwarai, mafi tawali’u fiye da kowane mutum a duniya.)
Moses was a very humble man, more than anyone else on earth.
4 Nan da nan Ubangiji ya ce wa Musa, da Haruna da kuma Miriyam, “Ku fita ku tafi Tentin Sujada, dukanku uku.” Sai dukansu uku suka tafi.
All of a sudden the Lord called for Moses, Aaron, and Miriam, telling them, “The three of you, come to the Tent of Meeting.” The three of them did so.
5 Sai Ubangiji ya sauko a cikin ginshiƙin girgije; ya tsaya a bakin ƙofar Tenti, ya kira Haruna da Miriyam. Sa’ad da su biyu suka gusa gaba,
The Lord came down in a pillar of cloud and stood in the entrance to the Tent. He called Aaron and Miriam and they came forward.
6 sai ya ce, “Ku ji abin da zan faɗa, “Duk lokacin da akwai annabin Ubangiji a cikinku, nakan bayyana kaina gare shi cikin wahayi, in yi magana da shi cikin mafarkai.
“Now listen to my words, he told them. If you had prophets, I the Lord would reveal myself to them in visions; I would communicate with them in dreams.
7 Amma ba haka nake magana da Musa bawana ba; na sa shi yă lura da dukan jama’ata Isra’ila.
But it's not like this with my servant Moses, who of all my people is the one who is faithful.
8 Da shi nake magana fuska da fuska, a fili kuma, ba a kacici-kacici ba; yakan ga siffar Ubangiji. To, me ya sa ba ku ji tsoro ku yi magana a kan bawana Musa ba?”
I talk to him personally, face to face. I speak plainly, not in riddles. He sees the likeness of the Lord. So why weren't you afraid when you criticized my servant Moses?”
9 Sai fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kansu, ya kuma rabu da su.
The Lord was angry with them, and he left.
10 Da girgijen ya tashi daga bisa Tentin, sai ga Miriyam tsaye, kuturwa, fari fat. Haruna kuwa ya juya wajenta ya ga ta kuturce;
As the cloud rose above the Tent, Miriam's skin suddenly turned white with leprosy. Aaron turned to look and saw that she had leprosy.
11 sai Haruna ya ce wa Musa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka hukunta mu, gama zunubin da muka yi, mun yi ne cikin wauta.
He said to Moses, “My lord, please don't punish us for this sin that we've so stupidly committed.
12 Kada ka sa ta zama kamar haifaffen mataccen jariri daga cikin mahaifiya wanda rabin jikin ruɓaɓɓe ne.”
Please don't let her become like a stillborn baby whose flesh is already decaying when they're born!”
13 Saboda haka sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Allah, ina roƙonka ka warkar da ita!”
Moses called out to the Lord, “God, please heal her!”
14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Da a ce mahaifinta ne ya tofa mata miyau a fuskarta, ashe, ba za tă ji kunya har kwana bakwai ba? A fitar da ita bayan sansani kwana bakwai; bayan haka za a iya dawo da ita.”
But the Lord replied to Moses, “If her father had spit in her face wouldn't she have been disgraced for seven days? Keep her in isolation outside the camp for seven days, and then she can be taken back in.”
15 Haka aka fitar da Miriyam bayan sansani kwana bakwai, mutane kuwa ba su ci gaba da tafiya ba sai da aka dawo da ita.
Miriam was kept in isolation outside the camp for seven days, and the people did not move on until she was taken back in.
16 Bayan haka sai mutane suka bar Hazerot suka sauka a Hamadan Faran.
Then the people left Hazeroth and set up camp in the Desert of Paran.

< Ƙidaya 12 >