< Ƙidaya 12 >
1 Miriyam da Haruna suka fara zargin Musa saboda matarsa’yar ƙasar Kush da ya aura.
Mirjam og Aron tog til Orde mod Moses i Anledning af den kusjitiske Kvinde, han havde ægtet — han havde nemlig ægtet en kusjitisk Kvinde —
2 Suka ce, “Ubangiji ya yi magana ta wurin Musa ne kaɗai? Ashe, bai yi magana ta wurinmu mu ma ba?” Ubangiji kuwa ya ji wannan.
og sagde: »Har HERREN kun talet til Moses? Mon han ikke ogsaa har talet til os?« Og HERREN hørte det.
3 (Musa kuwa mutum ne mai tawali’u ƙwarai, mafi tawali’u fiye da kowane mutum a duniya.)
Men den Mand Moses var saare sagtmodig, sagtmodigere end noget andet Menneske paa Jorden.
4 Nan da nan Ubangiji ya ce wa Musa, da Haruna da kuma Miriyam, “Ku fita ku tafi Tentin Sujada, dukanku uku.” Sai dukansu uku suka tafi.
Da sagde HERREN i det samme til Moses, Aron og Mirjam: »Gaa alle tre ud til Aabenbaringsteltet!« Og de gik alle tre derud.
5 Sai Ubangiji ya sauko a cikin ginshiƙin girgije; ya tsaya a bakin ƙofar Tenti, ya kira Haruna da Miriyam. Sa’ad da su biyu suka gusa gaba,
Men HERREN steg ned i Skystøtten og stillede sig ved Indgangen til Teltet og kaldte paa Aron og Mirjam, og de gik begge derud.
6 sai ya ce, “Ku ji abin da zan faɗa, “Duk lokacin da akwai annabin Ubangiji a cikinku, nakan bayyana kaina gare shi cikin wahayi, in yi magana da shi cikin mafarkai.
Da sagde han: »Hør, hvad jeg siger: Naar der ellers er en Profet iblandt eder, giver jeg mig til Kende for ham i Syner eller taler med ham i Drømme.
7 Amma ba haka nake magana da Musa bawana ba; na sa shi yă lura da dukan jama’ata Isra’ila.
Anderledes er det med min Tjener Moses: han er tro i hele mit Hus;
8 Da shi nake magana fuska da fuska, a fili kuma, ba a kacici-kacici ba; yakan ga siffar Ubangiji. To, me ya sa ba ku ji tsoro ku yi magana a kan bawana Musa ba?”
med ham taler jeg Ansigt til Ansigt, ikke i Syner eller Gaader, han skuer HERRENS Skikkelse; hvor tør I da tage til Orde mod min Tjener Moses?«
9 Sai fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kansu, ya kuma rabu da su.
Og HERRENS Vrede blussede op imod dem, og han gik bort.
10 Da girgijen ya tashi daga bisa Tentin, sai ga Miriyam tsaye, kuturwa, fari fat. Haruna kuwa ya juya wajenta ya ga ta kuturce;
Da saa Skyen trak sig bort fra Teltet, se, da var Mirjam hvid som Sne af Spedalskhed, og da Aron vendte sig mod Mirjam, se, da var hun spedalsk.
11 sai Haruna ya ce wa Musa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka hukunta mu, gama zunubin da muka yi, mun yi ne cikin wauta.
Da sagde Aron til Moses: »Ak, Herre, lad os dog ikke undgælde for den Synd, vi i Daarskab begik!
12 Kada ka sa ta zama kamar haifaffen mataccen jariri daga cikin mahaifiya wanda rabin jikin ruɓaɓɓe ne.”
Lad hende dog ikke blive som et dødfødt Barn, hvis Kød er halvt fortæret, naar det kommer ud af Moders Liv!«
13 Saboda haka sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Allah, ina roƙonka ka warkar da ita!”
Moses raabte da til HERREN og sagde: »Ak, gør hende dog rask igen!«
14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Da a ce mahaifinta ne ya tofa mata miyau a fuskarta, ashe, ba za tă ji kunya har kwana bakwai ba? A fitar da ita bayan sansani kwana bakwai; bayan haka za a iya dawo da ita.”
Og HERREN svarede Moses: »Hvis hendes Fader havde spyttet hende i Ansigtet, maatte hun da ikke have baaret sin Skam i syv Dage? Derfor skal hun i syv Dage være udelukket fra Lejren; saa kan hun atter optages.«
15 Haka aka fitar da Miriyam bayan sansani kwana bakwai, mutane kuwa ba su ci gaba da tafiya ba sai da aka dawo da ita.
Da blev Mirjam udelukket fra Lejren i syv Dage, og Folket brød ikke op, før Mirjam atter var optaget.
16 Bayan haka sai mutane suka bar Hazerot suka sauka a Hamadan Faran.
Saa brød Folket op fra Hazerot og slog Lejr i Parans Ørken.