< Ƙidaya 12 >

1 Miriyam da Haruna suka fara zargin Musa saboda matarsa’yar ƙasar Kush da ya aura.
A mluvila Maria i Aron proti Mojžíšovi příčinou manželky Madianky, kterouž sobě vzal; nebo byl pojal manželku Madianku.
2 Suka ce, “Ubangiji ya yi magana ta wurin Musa ne kaɗai? Ashe, bai yi magana ta wurinmu mu ma ba?” Ubangiji kuwa ya ji wannan.
A řekli: Zdaliž jen toliko skrze Mojžíše mluvil Hospodin? Zdaž také nemluvil skrze nás? I slyšel to Hospodin.
3 (Musa kuwa mutum ne mai tawali’u ƙwarai, mafi tawali’u fiye da kowane mutum a duniya.)
(Byl pak Mojžíš člověk nejtišší ze všech lidí, kteříž byli na tváři země.)
4 Nan da nan Ubangiji ya ce wa Musa, da Haruna da kuma Miriyam, “Ku fita ku tafi Tentin Sujada, dukanku uku.” Sai dukansu uku suka tafi.
A i hned řekl Hospodin Mojžíšovi a Aronovi i Marii: Vyjděte vy tři k stánku úmluvy. I vyšli toliko oni tři.
5 Sai Ubangiji ya sauko a cikin ginshiƙin girgije; ya tsaya a bakin ƙofar Tenti, ya kira Haruna da Miriyam. Sa’ad da su biyu suka gusa gaba,
Tedy sstoupil Hospodin v sloupu oblakovém, a stál u dveří stánku. I zavolal Arona a Marie, a vyšli oba dva.
6 sai ya ce, “Ku ji abin da zan faɗa, “Duk lokacin da akwai annabin Ubangiji a cikinku, nakan bayyana kaina gare shi cikin wahayi, in yi magana da shi cikin mafarkai.
Jimž řekl: Slyšte nyní slova má: Prorok když jest mezi vámi, já Hospodin u vidění ukáži se jemu, ve snách mluviti budu s ním.
7 Amma ba haka nake magana da Musa bawana ba; na sa shi yă lura da dukan jama’ata Isra’ila.
Ale není takový služebník můj Mojžíš, kterýž ve všem domě mém věrný jest.
8 Da shi nake magana fuska da fuska, a fili kuma, ba a kacici-kacici ba; yakan ga siffar Ubangiji. To, me ya sa ba ku ji tsoro ku yi magana a kan bawana Musa ba?”
Ústy k ústům mluvím s ním, ne u vidění, ani v zavinutí, a podobnost Hospodinovu spatřuje. Pročež jste tedy neostýchali se mluviti proti služebníku mému Mojžíšovi?
9 Sai fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kansu, ya kuma rabu da su.
I roznícena jest prchlivost Hospodinova na ně, a odšel.
10 Da girgijen ya tashi daga bisa Tentin, sai ga Miriyam tsaye, kuturwa, fari fat. Haruna kuwa ya juya wajenta ya ga ta kuturce;
Oblak také zdvihl se s stánku. A aj, Maria byla malomocná, bílá jako sníh. A pohleděl Aron na Marii, ana malomocná.
11 sai Haruna ya ce wa Musa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka hukunta mu, gama zunubin da muka yi, mun yi ne cikin wauta.
Tedy řekl Aron Mojžíšovi: Poslyš mne, pane můj, prosím, nevzkládej na nás té pokuty za hřích ten, jehož jsme se bláznivě dopustili, a jímž jsme zhřešili.
12 Kada ka sa ta zama kamar haifaffen mataccen jariri daga cikin mahaifiya wanda rabin jikin ruɓaɓɓe ne.”
Prosím, ať není tato jako mrtvý plod, kterýž když vychází z života matky své, polovici těla jeho zkaženého bývá.
13 Saboda haka sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Allah, ina roƙonka ka warkar da ita!”
I volal Mojžíš k Hospodinu, řka: Ó Bože silný, prosím, uzdraviž ji.
14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Da a ce mahaifinta ne ya tofa mata miyau a fuskarta, ashe, ba za tă ji kunya har kwana bakwai ba? A fitar da ita bayan sansani kwana bakwai; bayan haka za a iya dawo da ita.”
Odpověděl Hospodin Mojžíšovi: Kdyby otec její plinul jí na tvář, zdaž by se nemusila styděti za sedm dní? Protož ať jest vyobcována ven z stanů za sedm dní, a potom zase uvedena bude.
15 Haka aka fitar da Miriyam bayan sansani kwana bakwai, mutane kuwa ba su ci gaba da tafiya ba sai da aka dawo da ita.
Tedy vyloučena jest Maria ven z stanů za sedm dní; a lid nehnul se odtud, až zase uvedena jest Maria.
16 Bayan haka sai mutane suka bar Hazerot suka sauka a Hamadan Faran.
Potom pak bral se lid z Hazerot, a položil se na poušti Fáran.

< Ƙidaya 12 >