< Ƙidaya 11 >
1 Da Ubangiji ya ji gunagunin da mutanen suke yi saboda wahalarsu, sai ya husata ƙwarai. Sai wuta daga Ubangiji ta yi ta ci a cikinsu har ta ƙone waɗansu wurare na sansanin.
Yn the meene tyme the grutchyng of the puple, as of men sorewynge for trauel, roos ayens the Lord. And whanne Moises hadde herd this thing, he was wrooth; and the fier of the Lord was kyndelid on hem, and deuouride the laste part of the tentis.
2 Da jama’ar suka yi wa Musa kuka, sai ya yi addu’a ga Ubangiji, wutar kuwa ta mutu.
And whanne the puple hadde cried to Moises, Moises preiede the Lord, and the fier was quenchid.
3 Saboda haka aka kira wannan wuri Tabera, gama a wurin ne wuta daga Ubangiji ta ƙuna a cikinsu.
And he clepid the name of that place Brennyng, for the fier of the Lord was kyndlid ayens hem.
4 Wata rana, baƙin da suke cikinsu, suka fara kwaɗayin waɗansu abinci, har suka sa Isra’ilawa suka fara kuka, suna cewa, “Da mun sami nama mun ci mana!
And the comyn puple of `malis and femalis, that hadde stied with hem, brent with desire of fleischis, and sat, and wepte with the sones of Israel ioyned togidere to hem, and seide, Who schal yyue to vs fleischis to ete?
5 Mun tuna da kifin da muka ci kyauta a Masar, haka ma kayan lambu irin su kukumba, guna, safa, albasa da kuma tafarnuwa.
We thenken on the fischis whiche we eten in Egipt freli; gourdis, and melouns, and lekis, and oyniouns, and garlekis comen in to mynde `to vs;
6 Amma ga shi yanzu ba mu da wani abin marmari; in ba wannan Manna ba!”
oure soule is drie; oure iyen byholden noon other thing `no but manna.
7 Manna kuwa kamar tsabar riɗi take, kamanninta kuma kamar ƙaro ne.
Forsothe manna was as the seed of coriaundre, of the colour of bdellyum, which is whijt and briyt as cristal.
8 Mutane sukan fita su tattara ta, su niƙa a dutsen niƙa, ko kuwa su daka a turmi. Su dafa, ko su yi waina da ita. Ɗanɗanonta yakan yi kamar abin da aka yi da man zaitun.
And the puple yede aboute, and gaderide it, and brak with a queerne stoon, ether pownede in a morter, and sethide in a pot; and made therof litle cakis of the sauour, as of breed maad with oile.
9 Sa’ad da raɓa tana saukowa da dad dare a kan sansani, Manna ma takan sauko.
And whanne dew cam doun in the niyt on the tentis, also manna cam doun togidere.
10 Musa ya ji mutanen suna ta gunaguni ko’ina a cikin iyalansu, kowane mutum a ƙofar tentinsa. Ubangiji kuwa ya husata ƙwarai, sai Musa ya damu.
Therfor Moises herde the puple wepynge bi meynees, and `alle bi hem silf bi the doris of her tentis; and the woodnesse of the Lord was wrooth greetli, but also the thing was seyn vnsuffrable to Moises.
11 Sai ya ce wa Ubangiji, “Me ya sa ka kawo wannan damuwar a kan bawanka? Me na yi da ya ɓata maka rai har ka ɗora dukan nauyin mutanen nan a kaina?
And he seide to the Lord, Whi hast thou turmentid thi seruaunt? whi fynde Y not grace bifor thee? and whi hast thou put on me the burthun of al this puple?
12 Ni ne na yi cikin dukan mutanen nan? Ni ne na haife su? To, me ya sa ka ce in ɗauke su a ƙirjina kamar yadda mai reno yake rungume jariri, zuwa ƙasa wadda ka yi alkawari da rantsuwa za ka ba wa kakanninsu?
whethir Y conseyuede al this multitude, ethir gendride it, that thou seie to me, Bere thou hem in thi bosum as a nurise is wont to bere a litil yong child, and bere thou in to the lond for which thou hast swore to the fadris `of hem.
13 Ina ne zan sami nama in waɗannan mutane? Sun dinga yin mini kuka suna cewa ‘Ka ba mu nama mu ci!’
wherof ben fleischis to me, that Y `yyue to so greet multitude? Thei wepen bifore me, and seyn, `Yyue thou fleischis to vs that we ete;
14 Ba zan iya ɗaukan dukan mutanen nan ni kaɗai ba, nauyin ya yi mini yawa.
I mai not aloone suffre al this puple, for it is greuouse to me.
15 In haka za ka yi da ni, ka kashe ni yanzu, in na sami tagomashi daga gare ka, kada ka bar ni in rayu in ga wannan baƙin ciki.”
If in other maner it semeth to thee, Y biseche that thou sle me, and that Y fynde grace in thin iyen, that Y be not punyschid bi so grete yuelis.
16 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattaro mini dattawa saba’in daga cikin mutanen Isra’ila, waɗanda aka sani su ne dattawa da kuma shugabanni a cikin jama’a. Ka sa su zo Tentin Sujada, su tsaya a can tare da kai.
And the Lord seide to Moises, Gadere thou to me seuenti men of the eldre men of Israel, whiche thou knowist, `that thei ben the elde men and maistris of the puple; and thou schalt lede hem to the dore of the tabernacle of boond of pees, and thou schalt make to stonde there with thee,
17 Zan sauko in yi magana da kai a can, zan kuma ɗauki Ruhun da yake kanka in mai da shi wajensu. Za su taimake ka ɗaukan nauyin mutane, don yă zama ba kai kaɗai ba ne mai ɗaukan kaya.
that Y come doun, and speke to thee; and Y schal take awey of thi spirit, and Y schal yyue to hem, that thei susteyne with thee the birthun of the puple, and not thou aloone be greuyd.
18 “Ka gaya wa mutane, ‘Ku tsarkake kanku don gobe, za ku ci nama. Ubangiji ya ji ku sa’ad da kuka yi kuka cewa, “Da mun sami nama mun ci mana! Ai, da ba mu da damuwa, gama lokacin da muke zama cikin Masar ba mu da damuwa!” Yanzu Ubangiji zai ba ku nama, za ku kuma ci.
And thou schalt seie to the puple, Be ye halewid; to morew ye schulen ete fleischis; for Y herde you seie, Who schal yyue to vs the metis of fleischis? it was wel to vs in Egipt; that the Lord yyue `fleischis to you,
19 Ba za ku ci shi na kwana ɗaya, ko biyu, ko biyar, ko goma, ko kuma kwana ashirin kaɗai ba,
and that ye ete not o dai, ethir tweyne, ethir fyue, ethir ten, sotheli nether twenti,
20 amma za ku ci har na wata guda cur, sai ya gundure ku a hanci har ku yi ƙyamarsa, domin kun ƙi Ubangiji wanda yake cikinku, kuka yi kuka a gabansa, kuna cewa, “Don me ma muka bar ƙasar Masar?”’”
but `til to a monethe of daies, til it go out bi youre nosethirlis, and turne in to wlatyng; for ye han put awei the Lord, which is in the myddis of you, and ye wepten bifor hym, and seiden, Whi yeden we out of Egipt?
21 Amma Musa ya ce, “Ga ni a cikin mutane dubu ɗari shida tafe tare da ni, kana kuma cewa, ‘Zan ba su nama su ci har wata guda cur!’
And Moises seide to the Lord, Sixe hundrid thousynde of foot men ben of this puple, and thou seist, Y schal yyue to hem `mete of fleischis an hool monethe.
22 Za su ma sami isashe in har aka yanka musu garkuna tumaki da na shanu? Za su sami isashe in aka kama musu dukan kifin teku?”
Whether the multitude of scheep and of oxun schal be slayn, that it may suffice to mete, ethir alle the fischis of the see schulen be gaderid to gidere, that tho fille hem?
23 Ubangiji ya ce wa Musa, “Akwai abin da ya fi ƙarfina ne? Bari ka gani ko abin da na ce zan yi, zai faru ko babu.”
To whom the Lord answeride, Whether the `hond of the Lord is vnmyyti? riyt now thou schalt se, wher my word schal be fillid in werk.
24 Saboda haka Musa ya fita ya gaya wa jama’a abin da Ubangiji ya faɗa. Ya tattaro dattawansu saba’in, ya sa suka tsaya kewaye da Tentin Sujada.
Therfor Moises cam, and telde to the puple the wordis of the Lord; and he gaderide seuenti men of the eldere of Israel, whiche he made stonde aboute the tabernacle.
25 Sa’an nan Ubangiji ya sauko daga girgije, ya yi magana da shi, ya kuma ɗauke Ruhun da yake kan Musa ya ɗora shi a kan dattawa saba’in nan. Sa’ad da Ruhun ya zauna a kansu, sai suka yi annabci, amma daga wannan ba su ƙara yin haka kuma ba.
And the Lord cam doun bi a cloude, and spak to Moises, and took a weye of the spirit that was in Moises, and yaf to the seuenti men; and whanne the spirit hadde restid in hem, thei profesieden, and ceessiden not `aftirward.
26 To, fa, akwai dattawa biyu da suka kasance a sansani, wato, Eldad da Medad. Su ma an lasafta su cikin dattawan, amma ba su fita zuwa Tentin Sujada ba. Duk da haka Ruhun ya sauka a kansu, suka kuma yi annabci a cikin sansanin.
Forsothe twei men dwelliden stille in the tentis, of whiche men oon was clepid Heldad, and the tothir Medad, on whiche the spirit restide; for also thei weren descryued, and thei yeden not out to the tabernacle.
27 Wani saurayi ya sheƙa a guje zuwa wajen Musa ya ce, “Eldad da Medad suna can suna annabci a sansani.”
And whanne thei profesieden in the tentis, a child ran, and teld to Moises, and seide, Heldad and Medad profecien in the tentis.
28 Sai Yoshuwa ɗan Nun, wanda yake mataimakin Musa tun yana saurayi, ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, Musa, ka hana su!”
Anoon Josue, the sone of Nun, the `mynystre of Moises, and chosun of manye, seide, My lord Moises, forbede thou hem.
29 Amma Musa ya amsa ya ce, “Kana kishi domina ne? Da ma a ce dukan mutanen Ubangiji annabawa ne, da ma a kuma ce Ubangiji ya sa Ruhunsa a kansu mana!”
And he seide, What hast thou enuye for me? who yyueth that al the puple profesie, and that God yyue his spirit to hem?
30 Sai Musa da dattawan Isra’ila suka koma sansani.
And Moises turnede ayen, and the eldre men in birthe of Israel in to the tentis.
31 Ana nan, sai Ubangiji ya kawo wata iska mai tsanani ta koro makware daga teku. Ta bar su birjik kewaye da sansani, tsayinsu daga ƙasa ya kai kamu biyu, misalin tafiyar nisan yini guda ta kowace fuska.
Forsothe a wynde yede forth fro the Lord, and took curlewis, and bar ouer the see, and lefte in to the tentis, in the iurney, as myche as mai be parformed in o day, bi ech part of the tentis bi cumpas; and tho flowen in the eir bi twei cubitis in `hiynesse ouer the erthe.
32 Dukan yini da dukan dare da kuma kashegari, mutane suka fito suka tattara makware. Ba wanda ya kāsa tara ƙasa da garwa goma. Sai suka shanya abinsu kewaye da sansanin.
Therfor the puple roos in al that dai and nyyt and in to the tothir dai, and gaderide the multitude of curlewis; he that gaderide litil, gaderide ten `mesuris clepid chorus; `and o chorus conteyneth ten buschels; and thei drieden tho curlewis bi the cumpas of the tentis.
33 Amma da suna cikin cin naman, tun ba su ma haɗiye ba, sai Ubangiji ya husata sosai a kan jama’ar, ya buge su da annoba mai zafi.
Yit `fleischis weren in the teeth `of hem, and siche mete failide not; and lo! the woodnesse of the Lord was reisid ayens the puple, and smoot it with a ful greet veniaunce.
34 Saboda haka aka kira wannan wuri Kibrot Hatta’awa, gama a can ne aka binne mutanen nan makwaɗaita.
And thilke place was clepid The sepulcris of coueitise, for there thei birieden the puple that desiride fleischis.
35 Daga Kibrot Hatta’awa, mutane suka yi tafiya zuwa Hazerot, a can suka sauka.
Sotheli thei yeden `out of the sepulcris of coueitise, and camen in to Asseroth, and dwelliden there.