< Ƙidaya 11 >

1 Da Ubangiji ya ji gunagunin da mutanen suke yi saboda wahalarsu, sai ya husata ƙwarai. Sai wuta daga Ubangiji ta yi ta ci a cikinsu har ta ƙone waɗansu wurare na sansanin.
And it came to pass that as the people complained in a manner displeasing in the ears of the Lord, the Lord heard it, and his anger was kindled, and the fire of the Lord burnt among them, and consumed at the uttermost part of the camp.
2 Da jama’ar suka yi wa Musa kuka, sai ya yi addu’a ga Ubangiji, wutar kuwa ta mutu.
And the people then cried unto Moses; and Moses prayed unto the Lord, and the fire disappeared.
3 Saboda haka aka kira wannan wuri Tabera, gama a wurin ne wuta daga Ubangiji ta ƙuna a cikinsu.
And he called the name of the place Tab'erah; because the fire of the Lord had burnt among them.
4 Wata rana, baƙin da suke cikinsu, suka fara kwaɗayin waɗansu abinci, har suka sa Isra’ilawa suka fara kuka, suna cewa, “Da mun sami nama mun ci mana!
And the mixed multitude that was among them felt a lustful longing: and the children of Israel also wept again, and said, Who will give us flesh to eat?
5 Mun tuna da kifin da muka ci kyauta a Masar, haka ma kayan lambu irin su kukumba, guna, safa, albasa da kuma tafarnuwa.
We remember the fish, which we could eat in Egypt for naught; the cucumbers, and the melons, and the leeks, and the onions, and the garlic;
6 Amma ga shi yanzu ba mu da wani abin marmari; in ba wannan Manna ba!”
But now our soul is faint: there is nothing at all, only to the manna are our eyes [directed].
7 Manna kuwa kamar tsabar riɗi take, kamanninta kuma kamar ƙaro ne.
But the manna was like coriander-seed, and its color as the color of the bdellium.
8 Mutane sukan fita su tattara ta, su niƙa a dutsen niƙa, ko kuwa su daka a turmi. Su dafa, ko su yi waina da ita. Ɗanɗanonta yakan yi kamar abin da aka yi da man zaitun.
The people went about and gathered it, and ground it in a mill, or pounded it in a mortar, and boiled it in a pot, or made cakes of it: and its taste was as the taste of cakes mixed with oil.
9 Sa’ad da raɓa tana saukowa da dad dare a kan sansani, Manna ma takan sauko.
And when the dew fell upon the camp in the night, the manna fell upon it.
10 Musa ya ji mutanen suna ta gunaguni ko’ina a cikin iyalansu, kowane mutum a ƙofar tentinsa. Ubangiji kuwa ya husata ƙwarai, sai Musa ya damu.
And Moses heard the people weep according to their families, every man at the door of his tent: and the anger of the Lord was kindled greatly; and in the eyes of Moses also was it displeasing.
11 Sai ya ce wa Ubangiji, “Me ya sa ka kawo wannan damuwar a kan bawanka? Me na yi da ya ɓata maka rai har ka ɗora dukan nauyin mutanen nan a kaina?
And Moses said unto the Lord, Wherefore hast thou done evil to thy servant? and wherefore have I not found favor in thy eyes, that thou layest the burden of all this people upon me?
12 Ni ne na yi cikin dukan mutanen nan? Ni ne na haife su? To, me ya sa ka ce in ɗauke su a ƙirjina kamar yadda mai reno yake rungume jariri, zuwa ƙasa wadda ka yi alkawari da rantsuwa za ka ba wa kakanninsu?
Was it I who have conceived all this people? or was it I who have begotten them? that thou shouldst say unto me, Carry them in thy bosom, as a nursing father beareth the sucking child, unto the land which thou hast sworn unto their fathers?
13 Ina ne zan sami nama in waɗannan mutane? Sun dinga yin mini kuka suna cewa ‘Ka ba mu nama mu ci!’
Whence shall I obtain flesh to give unto all this people? for they weep around me, saying, Give us flesh, that we may eat.
14 Ba zan iya ɗaukan dukan mutanen nan ni kaɗai ba, nauyin ya yi mini yawa.
I am not able by myself alone to bear all this people, because it is too heavy for me.
15 In haka za ka yi da ni, ka kashe ni yanzu, in na sami tagomashi daga gare ka, kada ka bar ni in rayu in ga wannan baƙin ciki.”
And if thou wilt thus deal with me, then slay me, I pray thee, at once, if I have found favor in thy eyes: that I may not see my wretchedness.
16 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattaro mini dattawa saba’in daga cikin mutanen Isra’ila, waɗanda aka sani su ne dattawa da kuma shugabanni a cikin jama’a. Ka sa su zo Tentin Sujada, su tsaya a can tare da kai.
And the Lord said unto Moses, Gather unto me seventy men of the elders of Israel, whom thou knowest to be the elders of the people, and its officers; and take them unto the tabernacle of the congregation, and they shall stand there with thee.
17 Zan sauko in yi magana da kai a can, zan kuma ɗauki Ruhun da yake kanka in mai da shi wajensu. Za su taimake ka ɗaukan nauyin mutane, don yă zama ba kai kaɗai ba ne mai ɗaukan kaya.
And I will come down and speak with thee there: and I will take some of the spirit which is upon thee, and I will put it upon them; and they shall bear with thee the burden of the people, and thou shalt not bear it by thyself alone.
18 “Ka gaya wa mutane, ‘Ku tsarkake kanku don gobe, za ku ci nama. Ubangiji ya ji ku sa’ad da kuka yi kuka cewa, “Da mun sami nama mun ci mana! Ai, da ba mu da damuwa, gama lokacin da muke zama cikin Masar ba mu da damuwa!” Yanzu Ubangiji zai ba ku nama, za ku kuma ci.
And unto the people shalt thou say, Hold yourselves ready against tomorrow, that ye may eat flesh; for ye have wept in the ears of the Lord, saying, Who shall give us flesh to eat? for it was better with us in Egypt: thus will the Lord give you flesh, and ye shall eat.
19 Ba za ku ci shi na kwana ɗaya, ko biyu, ko biyar, ko goma, ko kuma kwana ashirin kaɗai ba,
Not one day shall ye eat, nor two days, nor five days, nor ten days, nor twenty days;
20 amma za ku ci har na wata guda cur, sai ya gundure ku a hanci har ku yi ƙyamarsa, domin kun ƙi Ubangiji wanda yake cikinku, kuka yi kuka a gabansa, kuna cewa, “Don me ma muka bar ƙasar Masar?”’”
But up to a full month, until it come out at your nostrils, and it become loathsome unto you; because that ye have despised the Lord who is in the midst of you, and ye have wept before him, saying, Why did we come forth out of Egypt?
21 Amma Musa ya ce, “Ga ni a cikin mutane dubu ɗari shida tafe tare da ni, kana kuma cewa, ‘Zan ba su nama su ci har wata guda cur!’
And Moses said, Six hundred thousand men on foot is the people, in the midst of whom I am; and yet thou hast said, Flesh will I give them, that they may eat a whole month.
22 Za su ma sami isashe in har aka yanka musu garkuna tumaki da na shanu? Za su sami isashe in aka kama musu dukan kifin teku?”
Shall flocks and herds be slain for them, that they may suffice for them? or shall all the fish of the sea be gathered together for them, that they may suffice for them?
23 Ubangiji ya ce wa Musa, “Akwai abin da ya fi ƙarfina ne? Bari ka gani ko abin da na ce zan yi, zai faru ko babu.”
And the Lord said unto Moses, Should the Lord's hand be too short? now shalt thou see whether my word shall come to pass unto thee or not.
24 Saboda haka Musa ya fita ya gaya wa jama’a abin da Ubangiji ya faɗa. Ya tattaro dattawansu saba’in, ya sa suka tsaya kewaye da Tentin Sujada.
And Moses went out, and spoke to the people the words of the Lord; and he assembled seventy men from the elders of the people, and placed them round about the tabernacle.
25 Sa’an nan Ubangiji ya sauko daga girgije, ya yi magana da shi, ya kuma ɗauke Ruhun da yake kan Musa ya ɗora shi a kan dattawa saba’in nan. Sa’ad da Ruhun ya zauna a kansu, sai suka yi annabci, amma daga wannan ba su ƙara yin haka kuma ba.
And the Lord came down in a cloud and spoke unto him; and he took some of the spirit that was upon him, and put it upon the seventy men, the elders: and it came to pass, that, when the spirit rested upon them, they prophesied, but they did not so any more.
26 To, fa, akwai dattawa biyu da suka kasance a sansani, wato, Eldad da Medad. Su ma an lasafta su cikin dattawan, amma ba su fita zuwa Tentin Sujada ba. Duk da haka Ruhun ya sauka a kansu, suka kuma yi annabci a cikin sansanin.
And there remained two men in the camp, the name of the one was Eldad, and the name of the other Medad; and the spirit rested upon them; and they were of those that were written down, but they had not gone out unto the tabernacle: and they prophesied in the camp.
27 Wani saurayi ya sheƙa a guje zuwa wajen Musa ya ce, “Eldad da Medad suna can suna annabci a sansani.”
And there ran a young man, and told to Moses, and said, Eldad and Medad are prophesying in the camp.
28 Sai Yoshuwa ɗan Nun, wanda yake mataimakin Musa tun yana saurayi, ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, Musa, ka hana su!”
And Joshua the son of Nun, the servant of Moses from his youth, answered and said, My Lord Moses, forbid them.
29 Amma Musa ya amsa ya ce, “Kana kishi domina ne? Da ma a ce dukan mutanen Ubangiji annabawa ne, da ma a kuma ce Ubangiji ya sa Ruhunsa a kansu mana!”
And Moses said unto him, Art thou zealous for my sake? And oh that one might render all the people of the Lord prophets, that the Lord would put his spirit upon them!
30 Sai Musa da dattawan Isra’ila suka koma sansani.
And Moses retired back into thy camp, he with the elders of Israel.
31 Ana nan, sai Ubangiji ya kawo wata iska mai tsanani ta koro makware daga teku. Ta bar su birjik kewaye da sansani, tsayinsu daga ƙasa ya kai kamu biyu, misalin tafiyar nisan yini guda ta kowace fuska.
And a wind went forth from the Lord, and drove up quails from the sea, and scattered them over the camp, about a day's journey on this side, and about a day's journey on the other side, round about the camp, and about two cubits high over the face of the earth.
32 Dukan yini da dukan dare da kuma kashegari, mutane suka fito suka tattara makware. Ba wanda ya kāsa tara ƙasa da garwa goma. Sai suka shanya abinsu kewaye da sansanin.
And the people arose all that day, and all that night, and all the following day, and they gathered the quails; he that had taken the least, had gathered ten chomers: and they spread them out for themselves round about the camp.
33 Amma da suna cikin cin naman, tun ba su ma haɗiye ba, sai Ubangiji ya husata sosai a kan jama’ar, ya buge su da annoba mai zafi.
The flesh was yet between their teeth, it was not yet chewed: when the wrath of the Lord was kindled against the people, and the Lord smote among the people a very great plague.
34 Saboda haka aka kira wannan wuri Kibrot Hatta’awa, gama a can ne aka binne mutanen nan makwaɗaita.
And he called the name of that place Kibroth-hattaavah; because there they buried the people that had lustfully craved.
35 Daga Kibrot Hatta’awa, mutane suka yi tafiya zuwa Hazerot, a can suka sauka.
From Kibroth-hattaavah the people journeyed unto Chazeroth; and they remained at Chazeroth.

< Ƙidaya 11 >