< Ƙidaya 10 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Och Herren talade med Mose, och sade:
2 “Ka ƙera kakaki guda biyu na azurfa, ka kuma yi amfani da su don kira taron jama’a wuri ɗaya, don kuma ka riƙa sanar da su lokacin tashi daga sansani.
Gör dig två trummeter af tätt silfver, att du brukar dem till att kalla tillhopa menighetena, och när hären af stad skall.
3 Sa’ad da aka busa su biyu, dukan jama’a za su taru a gabanka a ƙofar Tentin Sujada.
När man blås slätt med dem båda, skall församla sig till dig hela menigheten inför dörrena af vittnesbördsens tabernakel.
4 In ɗaya ne kaɗai aka busa, sai shugabannin kabilan Isra’ila, su taru a gabanka.
När man slätt blås med enom, så skola höfvitsmännerna församla sig till dig; de öfverste öfver tusende i Israel.
5 Sa’ad da aka ji karar busar kakaki, sai sansanin da yake a gabashi, su kama hanya.
Men när I trummeten, så skola de lägren draga af stad, som ligga österut.
6 A kara ta biyu, sansanin da yake a kudanci, su kama hanya. Busan kakaki zai zama alama ta kama hanya.
Och när I trummeten annan gång, då skola de lägren draga af stad, som ligga söderut; förty, när de resa skola, så skolen I trummeta.
7 In don a tara jama’a ne, sai a busa kakaki, amma ba da irin alama ɗaya ba.
Men när menigheten skall församlas, skolen I slätt blåsa, och icke trummeta.
8 “’Ya’yan Haruna, firistoci ne, za su busa kakaki. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla gare ku da kuma tsararraki masu zuwa.
Och det blåsandet med trummeterna skola Prestens Aarons söner göra. Och det skall vara eder ett evigt sätt till edra efterkommande.
9 Duk lokacin da za ku tafi yaƙi a ƙasarku, in akwai waɗansu da suke matsa muku, za ku yi amfani da waɗannan kakaki ta wurin hura su, alama ce, cewa za a je yaƙi. Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, yă cece ku daga maƙiyanku.
När I dragen till någon strid uti edro lande emot edra fiendar, som strida på eder, så skolen I trummeta med trummeterna, att uppå eder skall tänkt varda för Herranom edrom Gud, och I mågen löste varda ifrån edra fiendar.
10 Haka ma in kuna cikin jin daɗinku, musamman lokacin da kuke bukukkuwanku, kamar Bikin Sabon Wata da dai kowane Bikinku, za ku hura waɗannan kakaki lokacin da kuke miƙa hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama, za su kuma zama muku abin tunawa a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Sammalunda ock, när I ären glade, på edra högtider och edra nymånader, skolen I blåsa med trummeterna öfver edor bränneoffer och tackoffer; att det skall vara eder till åminnelse för edrom Gud. Jag är Herren edar Gud.
11 A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
På tjugonde dagen i dem andra månadenom, i de andra årena, gaf molnskyn sig upp af vittnesbördsens tabernakel.
12 Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
Och Israels barn drogo i deras skarar utu Sinai öken; och molnskyn blef uti den öknene Paran.
13 Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
Och de förste drogo af stad, efter Herrans ord genom Mose;
14 Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
Nämliga det baneret af Juda barnas lägre drog först åstad med deras här; och öfver deras här var Nahesson, Amminadabs son.
15 Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
Och öfver den hären af Isaschars barnas slägte var Nathaneel, Zuars son.
16 Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
Och öfver den hären af Sebulons barnas slägte var Eliab, Helons son.
17 Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
Då lade man tillsamman tabernaklet; och Gersons och Merari barn drogo åstad, och båro tabernaklet.
18 Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
Dernäst följde det baneret af Rubens lägre med deras här; och öfver deras här var Elizur, Sedeurs son.
19 Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
Och öfver den hären af Simeons barnas slägte var Selumiel, ZuriSadai son.
20 Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
Och Eliasaph, Deguels son, öfver Gads barnas slägtes här.
21 Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
Så drogo ock de Kehatiter åstad, och båro helgedomen; och hine uppsatte tabernaklet tilldess denne kommo efter.
22 Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
Dernäst drog det baneret åstad af Ephraims barnas lägre med deras här; och öfver dem var Elisama, Ammihuds son.
23 Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
Och Gamliel, Pedahzurs son, öfver den hären af Manasse barnas slägte.
24 Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
Och Abidan, Gideoni son, öfver den hären af BenJamins barnas slägte.
25 A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
Dernäst följde det baneret af Dans barnas lägre med deras här; och så voro all lägren uppe; och Ahieser, AmmiSadai son, var öfver deras här;
26 Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
Och Pagiel, Ochrans son, öfver den hären af Assers barnas slägte;
27 Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
Och Ahira, Enans son, öfver den hären af Naphthali barnas slägte.
28 Wannan shi ne tsarin tafiyar ɓangarorin Isra’ilawa, sa’ad da sukan kama hanya.
Så foro Israels barn med deras härar.
29 Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
Och Mose sade till sin svåger Hobab, Reguels son, af Midian: Vi drage till de rum, om hvilka Herren sagt hafver: Jag skall gifva eder dem; så kom nu med oss, vi vilje göra det bästa med dig; ty Herren hafver Israel godt tillsagt.
30 Ya amsa, ya ce “A’a, ba zan tafi ba; zan koma ƙasata da kuma wurin mutanena.”
Han svarade: Jag vill icke med eder, utan fara i mitt land till mina slägt.
31 Amma Musa ya ce, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu. Ka san inda ya kamata mu kafa sansani a hamada, za ka kuma zama idanunmu.
Han sade: Käre, öfvergif oss icke; förty du vetst hvar vi skole lägra oss i öknene, och skall vara vårt öga.
32 In ka zo tare da mu, za mu raba duk abin alherin Ubangiji ya ba mu tare da kai.”
Och om du far med oss, det goda, som Herren gör med oss, det vilje vi göra med dig.
33 Saboda haka suka kama hanya daga dutsen Ubangiji, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji ya ja gabansu a waɗannan kwanaki uku, don yă samo musu masauƙi.
Så drogo de ifrå Herrans berg tre dagsresor; och Herrans förbunds ark drog för dem tre dagsresor, till att visa dem hvar de hvila skulle.
34 A duk lokacin da suka tashi daga sansani, girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
Och Herrans molnsky var öfver dem om dagen, när de drogo utu lägret.
35 Duk kuma sa’ad da akwatin ya kama hanya, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji! Ka sa maƙiyanka su warwatse; masu ƙinka kuma su gudu a gabanka.”
Och när arken for, så sade Mose: Herre, statt upp, att dine fiender måga förströs; och de som dig hata, måga flyktige varda för dig.
36 Duk sa’ad da akwatin ya sauka kuma, sai Musa ya ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubban da ba a iya ƙidayawa na iyalan Isra’ila.”
Och när han sattes ned, sade han: Kom igen, Herre, till de många Israels tusend.