< Ƙidaya 10 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Gospod je spregovoril Mojzesu, rekoč:
2 “Ka ƙera kakaki guda biyu na azurfa, ka kuma yi amfani da su don kira taron jama’a wuri ɗaya, don kuma ka riƙa sanar da su lokacin tashi daga sansani.
»Naredi si dve srebrni trobenti. Iz celega kosa ju boš izdelal, da ju boste lahko uporabljali za sklic zbora in za potovanje taborov.
3 Sa’ad da aka busa su biyu, dukan jama’a za su taru a gabanka a ƙofar Tentin Sujada.
Ko bodo z njima zatrobili, se bo ves zbor zbral k tebi pri vratih šotorskega svetišča skupnosti.
4 In ɗaya ne kaɗai aka busa, sai shugabannin kabilan Isra’ila, su taru a gabanka.
Če bodo trobili samo z eno trobento, potem se bodo princi, ki so poglavarji tisočerih Izraelovih, skupaj zbrali k tebi.
5 Sa’ad da aka ji karar busar kakaki, sai sansanin da yake a gabashi, su kama hanya.
Kadar zatrobite alarm, potem bodo tabori, ki taborijo na vzhodnih delih, odšli naprej.
6 A kara ta biyu, sansanin da yake a kudanci, su kama hanya. Busan kakaki zai zama alama ta kama hanya.
Kadar drugič zatrobite alarm, potem se bodo tabori, ki taborijo na južni strani, odpravili na svoje potovanje; zaradi njihovih potovanj bodo trobili alarm.
7 In don a tara jama’a ne, sai a busa kakaki, amma ba da irin alama ɗaya ba.
Toda ko naj bi se skupnost zbrala skupaj, boste trobili, toda ne boste razglasili alarma.
8 “’Ya’yan Haruna, firistoci ne, za su busa kakaki. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla gare ku da kuma tsararraki masu zuwa.
Aronovi sinovi, duhovniki, bodo trobili s trobentami in oni vam bodo za odredbo na veke skozi vaše rodove.
9 Duk lokacin da za ku tafi yaƙi a ƙasarku, in akwai waɗansu da suke matsa muku, za ku yi amfani da waɗannan kakaki ta wurin hura su, alama ce, cewa za a je yaƙi. Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, yă cece ku daga maƙiyanku.
Če greste v svoji deželi na vojno zoper sovražnika, ki vas zatira, potem boste s trobentami trobili alarm in Gospod, vaš Bog, se vas bo spomnil in rešeni boste pred svojimi sovražniki.
10 Haka ma in kuna cikin jin daɗinku, musamman lokacin da kuke bukukkuwanku, kamar Bikin Sabon Wata da dai kowane Bikinku, za ku hura waɗannan kakaki lokacin da kuke miƙa hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama, za su kuma zama muku abin tunawa a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Tudi na dan vašega veselja in na vaše slovesne dneve in ob začetkih mesecev boste s trobentami trobili nad svojimi žgalnimi daritvami in nad žrtvovanji svojih mirovnih daritev, da vam bodo za spomin pred vašim Bogom. Jaz sem Gospod, vaš Bog.«
11 A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
Pripetilo se je na dvajseti dan drugega meseca, v drugem letu, da je bil oblak dvignjen iznad šotorskega svetišča pričevanja.
12 Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
Izraelovi otroci so se odpravili na svoja potovanja iz Sinajske divjine in oblak je obstal v Paránski divjini.
13 Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
Prvič so se odpravili na svoje potovanje glede na Gospodovo zapoved, po Mojzesovi roki.
14 Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
Prvi je odšel prapor tabora Judovih otrok, glede na njihove vojske in nad njegovo vojsko je bil Aminadábov sin Nahšón.
15 Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
Nad vojsko rodu Isahárjevih otrok je bil Cuárjev sin Netanél.
16 Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
Nad vojsko rodu Zábulonovih otrok je bil Helónov sin Eliáb.
17 Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
Šotorsko svetišče je bilo podrto, in Geršónovi sinovi in Meraríjevi sinovi so se odpravili naprej, noseč šotorsko svetišče.
18 Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
Prapor Rubenovega tabora se je odpravil naprej, glede na njihove vojske in nad njegovo vojsko je bil Šedeúrjev sin Elicúr.
19 Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
Nad vojsko rodu Simeonovih otrok je bil Curišadájev sin Šelumiél.
20 Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
Nad vojsko rodu Gadovih otrok je bil Deguélov sin Eljasáf.
21 Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
Kehátovci so se odpravili naprej, noseč svetišče, drugi pa so postavili šotorsko svetišče preden so ti prišli.
22 Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
Prapor tabora Efrájimovih otrok se je odpravil naprej glede na njihove vojske in nad njegovo vojsko je bil Amihúdov sin Elišamá.
23 Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
Nad vojsko rodu Manásejevih otrok je bil Pedacúrjev sin Gamliél.
24 Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
Nad vojsko rodu Benjaminovih otrok je bil Gideoníjev sin Abidán.
25 A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
Prapor tabora Danovih otrok se je odpravil naprej, ki je bil zadnja straža vseh taborov po njihovih vojskah. In nad njegovo vojsko je bil Amišadájev sin Ahiézer.
26 Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
Nad vojsko rodu Aserjevih otrok je bil Ohránov sin Pagiél.
27 Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
Nad vojsko rodu Neftálijevih otrok je bil Enánov sin Ahirá.
28 Wannan shi ne tsarin tafiyar ɓangarorin Isra’ilawa, sa’ad da sukan kama hanya.
Takšna so bila potovanja Izraelovih otrok glede na njihove vojske, ko so se odpravili naprej.
29 Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
Mojzes je rekel Hobábu, sinu Midjánca Reguéla, Mojzesovega tasta: »Potujemo proti kraju, o katerem je Gospod rekel: ›Jaz vam ga bom dal.‹ Pridi z nami in mi ti bomo storili dobro, kajti Gospod je dobro govoril glede Izraela.«
30 Ya amsa, ya ce “A’a, ba zan tafi ba; zan koma ƙasata da kuma wurin mutanena.”
Ta pa mu je rekel: »Ne bom šel, temveč bom odšel k svoji lastni deželi in k svojemu sorodstvu.«
31 Amma Musa ya ce, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu. Ka san inda ya kamata mu kafa sansani a hamada, za ka kuma zama idanunmu.
Rekel je: »Ne zapusti nas, prosim te, ker veš kako naj taborimo v divjini in ti si nam lahko namesto oči.
32 In ka zo tare da mu, za mu raba duk abin alherin Ubangiji ya ba mu tare da kai.”
In zgodilo se bo, če greš z nami, da, zgodilo se bo, da kakršna bo Gospodova dobrota do nas, isto bomo mi storili tebi.«
33 Saboda haka suka kama hanya daga dutsen Ubangiji, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji ya ja gabansu a waɗannan kwanaki uku, don yă samo musu masauƙi.
Odpravili so se od Gospodove gore tri dni potovanja in skrinja Gospodove zaveze je šla pred njimi na tridnevno potovanje, da zanje poišče počivališče.
34 A duk lokacin da suka tashi daga sansani, girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
Gospodov oblak je bil nad njimi podnevi, ko so odšli iz tabora.
35 Duk kuma sa’ad da akwatin ya kama hanya, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji! Ka sa maƙiyanka su warwatse; masu ƙinka kuma su gudu a gabanka.”
Kadar je skrinja krenila na pot, se je pripetilo, da je Mojzes rekel: »Vstani, Gospod in razkrope naj se tvoji sovražniki in tisti, ki te sovražijo, naj zbežijo pred teboj.«
36 Duk sa’ad da akwatin ya sauka kuma, sai Musa ya ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubban da ba a iya ƙidayawa na iyalan Isra’ila.”
Ko pa je ta počivala, je rekel: »Vrni se, oh Gospod, k mnogim Izraelovim tisočerim.«