< Ƙidaya 10 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Још рече Господ Мојсију говорећи:
2 “Ka ƙera kakaki guda biyu na azurfa, ka kuma yi amfani da su don kira taron jama’a wuri ɗaya, don kuma ka riƙa sanar da su lokacin tashi daga sansani.
Начини себи две трубе од сребра, коване да буду; њима ћеш сазивати збор и заповедати да полази војска.
3 Sa’ad da aka busa su biyu, dukan jama’a za su taru a gabanka a ƙofar Tentin Sujada.
Кад обе затрубе, тада нека се скупља к теби сав збор на врата шатора од састанка.
4 In ɗaya ne kaɗai aka busa, sai shugabannin kabilan Isra’ila, su taru a gabanka.
А кад једна затруби, тада нека се скупљају к теби кнезови, главари од хиљада Израиљевих.
5 Sa’ad da aka ji karar busar kakaki, sai sansanin da yake a gabashi, su kama hanya.
А кад затрубе потресајући, тада нека се креће логор који лежи према истоку.
6 A kara ta biyu, sansanin da yake a kudanci, su kama hanya. Busan kakaki zai zama alama ta kama hanya.
А кад затрубите други пут потресајући, онда нека се креће логор који је на југу; потресајући нека се труби кад треба да пођу.
7 In don a tara jama’a ne, sai a busa kakaki, amma ba da irin alama ɗaya ba.
А кад сазивате збор, трубите, али не потресајући.
8 “’Ya’yan Haruna, firistoci ne, za su busa kakaki. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla gare ku da kuma tsararraki masu zuwa.
А нека трубе у трубе синови Аронови свештеници; то да вам је уредба вечна од колена до колена.
9 Duk lokacin da za ku tafi yaƙi a ƙasarku, in akwai waɗansu da suke matsa muku, za ku yi amfani da waɗannan kakaki ta wurin hura su, alama ce, cewa za a je yaƙi. Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, yă cece ku daga maƙiyanku.
И кад пођете на војску у земљи својој на непријатеља који удари на вас, трубите у трубе потресајући; и Господ Бог ваш опоменуће вас се, и сачуваћете се од непријатеља својих.
10 Haka ma in kuna cikin jin daɗinku, musamman lokacin da kuke bukukkuwanku, kamar Bikin Sabon Wata da dai kowane Bikinku, za ku hura waɗannan kakaki lokacin da kuke miƙa hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama, za su kuma zama muku abin tunawa a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Тако и у дан весеља свог и на празнике своје и почетке месеца својих трубите у трубе приносећи жртве своје паљенице и жртве своје захвалне, и биће вам спомен пред Богом вашим. Ја сам Господ Бог ваш.
11 A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
И у двадесети дан другог месеца друге године подиже се облак изнад шатора од сведочанства.
12 Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
И пођоше синови Израиљеви својим редом из пустиње Синајске, и устави се облак у пустињи Фаранској.
13 Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
Тако пођоше први пут, као што Господ заповеди преко Мојсија.
14 Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
И пође напред застава војске синова Јудиних у четама својим; и над војском њиховом беше Насон, син Аминадавов;
15 Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
А над војском племена синова Исахарових Натанаило, син Согаров;
16 Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
А над војском племена синова Завулонових Елијав, син Хелонов.
17 Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
И сложише шатор, па пођоше синови Гирсонови и синови Мераријеви носећи шатор.
18 Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
Потом пође застава војске синова Рувимових, а над њиховом војском беше Елисур, син Седијуров,
19 Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
А над војском племена синова Симеунових Саламило, син Сурисадајев,
20 Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
А над војском племена синова Гадових Елисаф син Рагуилов.
21 Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
И пођоше синови Катови носећи светињу, да би они подигли шатор докле ови дођу.
22 Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
Потом пође застава војске синова Јефремових у четама својим, а над војском њиховом беше Елисама, син Емијудов,
23 Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
А над војском племена синова Манасијиних Гамалило син Фадасуров,
24 Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
А над војском племена синова Венијаминових Авидан син Гадеонијев.
25 A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
Најпосле пође застава војске синова Данових у четама својим, задња војска, и над војском њиховом беше Ахијезер, син Амисадајев,
26 Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
А над војском племена синова Асирових Фагаило, син Ехранов,
27 Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
А над војском племена синова Нефталимових Ахиреј, син Енанов.
28 Wannan shi ne tsarin tafiyar ɓangarorin Isra’ilawa, sa’ad da sukan kama hanya.
Тим редом пођоше синови Израиљеви у четама својим, и тако иђаху.
29 Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
А Мојсије рече Јоваву, сину Рагуиловом Мадијанину тасту свом: Идемо на место за које рече Господ: Вама ћу га дати. Хајде с нама, и добро ћемо ти учинити, јер је Господ обећао Израиљу много добра.
30 Ya amsa, ya ce “A’a, ba zan tafi ba; zan koma ƙasata da kuma wurin mutanena.”
А он му рече: Нећу ићи, него идем у своју земљу и у род свој.
31 Amma Musa ya ce, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu. Ka san inda ya kamata mu kafa sansani a hamada, za ka kuma zama idanunmu.
А Мојсије рече: Немој нас оставити, јер знаш места у пустињи где бисмо могли стајати, па нам буди вођ.
32 In ka zo tare da mu, za mu raba duk abin alherin Ubangiji ya ba mu tare da kai.”
И ако пођеш с нама кад дође добро које ће нам учинити Господ, учинићемо ти добро.
33 Saboda haka suka kama hanya daga dutsen Ubangiji, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji ya ja gabansu a waɗannan kwanaki uku, don yă samo musu masauƙi.
И тако пођоше од горе Господње, и иђаху три дана, и ковчег завета Господњег иђаше пред њима три дана тражећи место где би починули.
34 A duk lokacin da suka tashi daga sansani, girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
И облак Господњи беше над њима сваки дан кад полажаху с места, где беху у логору.
35 Duk kuma sa’ad da akwatin ya kama hanya, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji! Ka sa maƙiyanka su warwatse; masu ƙinka kuma su gudu a gabanka.”
И кад полажаше ковчег, говораше Мојсије: Устани Господе, и нека се разаспу непријатељи Твоји, и нека беже испред Тебе који мрзе на Те.
36 Duk sa’ad da akwatin ya sauka kuma, sai Musa ya ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubban da ba a iya ƙidayawa na iyalan Isra’ila.”
А кад се устављаше, говораше: Уврати се, Господе, к мноштву хиљада Израиљевих.