< Ƙidaya 10 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
INkosi yasikhuluma kuMozisi isithi:
2 “Ka ƙera kakaki guda biyu na azurfa, ka kuma yi amfani da su don kira taron jama’a wuri ɗaya, don kuma ka riƙa sanar da su lokacin tashi daga sansani.
Zenzele impondo ezimbili zesiliva, uzenze zibe ngumsebenzi okhandiweyo; njalo zizakuba ngezakho ekubizeni inhlangano lekusukeni kwezinkamba.
3 Sa’ad da aka busa su biyu, dukan jama’a za su taru a gabanka a ƙofar Tentin Sujada.
Uba bezivuthela inhlangano yonke izabuthana kuwe emnyango wethente lenhlangano.
4 In ɗaya ne kaɗai aka busa, sai shugabannin kabilan Isra’ila, su taru a gabanka.
Kodwa uba bevuthela olulodwa, iziphathamandla, inhloko zezinkulungwane zakoIsrayeli zizabuthana kuwe.
5 Sa’ad da aka ji karar busar kakaki, sai sansanin da yake a gabashi, su kama hanya.
Lapho lihlaba umkhosi, izinkamba ezimise ngempumalanga zizasuka.
6 A kara ta biyu, sansanin da yake a kudanci, su kama hanya. Busan kakaki zai zama alama ta kama hanya.
Lalapho lihlaba umkhosi ngokwesibili, izinkamba ezimise ngeningizimu zizasuka. Bazahlaba umkhosi ukuze zisuke.
7 In don a tara jama’a ne, sai a busa kakaki, amma ba da irin alama ɗaya ba.
Kodwa ekubuthaniseni ibandla lizavuthela impondo, kodwa lingahlabi umkhosi.
8 “’Ya’yan Haruna, firistoci ne, za su busa kakaki. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla gare ku da kuma tsararraki masu zuwa.
Njalo amadodana kaAroni, abapristi, azavuthela izimpondo. Zizakuba kini yisimiso esilaphakade ezizukulwaneni zenu.
9 Duk lokacin da za ku tafi yaƙi a ƙasarku, in akwai waɗansu da suke matsa muku, za ku yi amfani da waɗannan kakaki ta wurin hura su, alama ce, cewa za a je yaƙi. Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, yă cece ku daga maƙiyanku.
Njalo lapho liphuma impi elizweni lakini ukuyakulwa lesitha esilicindezelayo, lihlabe umkhosi ngezimpondo, njalo likhunjulwe phambi kweNkosi uNkulunkulu wenu, lisindiswe ezitheni zenu.
10 Haka ma in kuna cikin jin daɗinku, musamman lokacin da kuke bukukkuwanku, kamar Bikin Sabon Wata da dai kowane Bikinku, za ku hura waɗannan kakaki lokacin da kuke miƙa hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama, za su kuma zama muku abin tunawa a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Langosuku lwentokozo yenu, lemikhosini yenu emisiweyo, lekuthwaseni kwenyanga zenu, lizavuthela izimpondo phezu kweminikelo yenu yokutshiswa laphezu kwemihlatshelo yeminikelo yenu yokuthula, ukuze ibe kini yisikhumbuzo phambi kukaNkulunkulu wenu. NgiyiNkosi uNkulunkulu wenu.
11 A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
Kwasekusithi ngomnyaka wesibili, ngenyanga yesibili, ngolwamatshumi amabili lwenyanga, iyezi laphakanyiswa lisuka phezu kwethabhanekele lobufakazi.
12 Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
Abantwana bakoIsrayeli basebesuka enkangala yeSinayi ngokwenhambo zabo; leyezi lema enkangala yeParani.
13 Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
Basebesuka okokuqala ngokomlayo weNkosi ngesandla sikaMozisi.
14 Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
Kwasekusuka uphawu lwenkamba yabantwana bakoJuda kuqala ngamabutho abo; laphezu kwebutho lakhe kwakunguNashoni indodana kaAminadaba.
15 Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
Laphezu kwebutho lesizwe sabantwana bakoIsakari kwakunguNethaneli indodana kaZuwari.
16 Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
Laphezu kwebutho lesizwe sabantwana bakoZebuluni kwakunguEliyabi indodana kaHeloni.
17 Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
Ithabhanekele laselidilizwa; amadodana kaGerishoni lamadodana kaMerari asesuka, ethwele ithabhanekele.
18 Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
Kwasekusuka uphawu lwenkamba yakoRubeni ngamabutho abo; laphezu kwebutho lakhe kwakunguElizuri indodana kaShedewuri.
19 Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
Laphezu kwebutho lesizwe sabantwana bakoSimeyoni kwakunguShelumiyeli indodana kaZurishadayi.
20 Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
Laphezu kwebutho lesizwe sabantwana bakoGadi kwakunguEliyasafi indodana kaDehuweli.
21 Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
Kwasekusuka amaKohathi ethwele indlu engcwele, labanye bamisa ithabhanekele, engakafiki.
22 Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
Kwasekusuka uphawu lwenkamba yabantwana bakoEfrayimi ngamabutho abo; laphezu kwebutho lakhe kwakunguElishama indodana kaAmihudi.
23 Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
Laphezu kwebutho lesizwe sabantwana bakoManase kwakunguGamaliyeli indodana kaPedazuri.
24 Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
Laphezu kwebutho lesizwe sabantwana bakoBhenjamini kwakunguAbidani indodana kaGideyoni.
25 A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
Kwasekusuka uphawu lwenkamba yabantwana bakoDani; babengabokucina ezinkambeni zonke ngamabutho abo; laphezu kwebutho lakhe kwakunguAhiyezeri indodana kaAmishadayi.
26 Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
Laphezu kwebutho lesizwe sabantwana bakoAsheri kwakunguPagiyeli indodana kaOkirani.
27 Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
Laphezu kwebutho lesizwe sabantwana bakoNafithali kwakunguAhira indodana kaEnani.
28 Wannan shi ne tsarin tafiyar ɓangarorin Isra’ilawa, sa’ad da sukan kama hanya.
Lokhu yikusuka kwabantwana bakoIsrayeli ngamabutho abo, ekusukeni kwabo.
29 Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
UMozisi wasesithi kuHobabi indodana kaRehuweli umMidiyani, uyisezala kaMozisi: Thina siyasuka siya endaweni iNkosi eyathi ngayo: Ngizalipha yona. Hamba lathi; sizakwenzela okuhle, ngoba iNkosi ikhulume okuhle ngoIsrayeli.
30 Ya amsa, ya ce “A’a, ba zan tafi ba; zan koma ƙasata da kuma wurin mutanena.”
Wasesithi kuye: Kangiyikuhamba, kodwa-ke ngizakuya elizweni lakithi lezihlotsheni zami.
31 Amma Musa ya ce, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu. Ka san inda ya kamata mu kafa sansani a hamada, za ka kuma zama idanunmu.
Wasesithi: Ake ungasitshiyi, ngoba uyazi lapho esingamisa khona inkamba enkangala, uzakuba ngamehlo ethu.
32 In ka zo tare da mu, za mu raba duk abin alherin Ubangiji ya ba mu tare da kai.”
Kuzakuthi-ke, uba uhamba lathi, yebo, kuzakwenzeka lokho okuhle okungakho iNkosi ezasenzela okuhle, sizakwenzela okuhle.
33 Saboda haka suka kama hanya daga dutsen Ubangiji, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji ya ja gabansu a waɗannan kwanaki uku, don yă samo musu masauƙi.
Basuka-ke entabeni yeNkosi, uhambo lwensuku ezintathu; lomtshokotsho wesivumelwano seNkosi wahamba phambi kwabo uhambo lwensuku ezintathu, ukuze ubadingele indawo yokuphumula.
34 A duk lokacin da suka tashi daga sansani, girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
Leyezi leNkosi laliphezu kwabo emini, ekusukeni kwabo enkambeni.
35 Duk kuma sa’ad da akwatin ya kama hanya, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji! Ka sa maƙiyanka su warwatse; masu ƙinka kuma su gudu a gabanka.”
Kwasekusithi ekusukeni komtshokotsho, uMozisi wathi: Vuka, Nkosi, kazichitheke-ke izitha zakho, lalabo abakuzondayo kababaleke phambi kwakho.
36 Duk sa’ad da akwatin ya sauka kuma, sai Musa ya ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubban da ba a iya ƙidayawa na iyalan Isra’ila.”
Ekumisweni kwawo wathi: Buyela, Nkosi, kuzinkulungwane ezilitshumi zezinkulungwane zakoIsrayeli.

< Ƙidaya 10 >