< Ƙidaya 10 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Yahvé parla à Moïse, et dit:
2 “Ka ƙera kakaki guda biyu na azurfa, ka kuma yi amfani da su don kira taron jama’a wuri ɗaya, don kuma ka riƙa sanar da su lokacin tashi daga sansani.
« Fais deux trompettes d'argent. Tu les feras en travail battu. Tu t'en serviras pour appeler l'assemblée et pour la marche des camps.
3 Sa’ad da aka busa su biyu, dukan jama’a za su taru a gabanka a ƙofar Tentin Sujada.
Lorsqu'on en soufflera, toute l'assemblée se rassemblera auprès de toi à l'entrée de la tente de la Rencontre.
4 In ɗaya ne kaɗai aka busa, sai shugabannin kabilan Isra’ila, su taru a gabanka.
Si l'on n'en fait retentir qu'une seule, les princes, les chefs des milliers d'Israël, se rassembleront auprès de toi.
5 Sa’ad da aka ji karar busar kakaki, sai sansanin da yake a gabashi, su kama hanya.
Lorsque tu sonneras l'alarme, les camps qui se trouvent à l'est avanceront.
6 A kara ta biyu, sansanin da yake a kudanci, su kama hanya. Busan kakaki zai zama alama ta kama hanya.
Lorsque tu sonneras une seconde fois, les camps qui se trouvent au sud avanceront. Ils sonneront l'alarme pour leurs déplacements.
7 In don a tara jama’a ne, sai a busa kakaki, amma ba da irin alama ɗaya ba.
Mais quand l'assemblée se réunira, tu sonneras, mais tu ne sonneras pas.
8 “’Ya’yan Haruna, firistoci ne, za su busa kakaki. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla gare ku da kuma tsararraki masu zuwa.
« Les fils d'Aaron, les prêtres, sonneront des trompettes. Ce sera pour vous une loi à perpétuité, de génération en génération.
9 Duk lokacin da za ku tafi yaƙi a ƙasarku, in akwai waɗansu da suke matsa muku, za ku yi amfani da waɗannan kakaki ta wurin hura su, alama ce, cewa za a je yaƙi. Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, yă cece ku daga maƙiyanku.
Lorsque tu iras à la guerre dans ton pays contre l'adversaire qui t'opprime, tu sonneras des trompettes. Alors on se souviendra de toi devant Yahvé ton Dieu, et tu seras sauvé de tes ennemis.
10 Haka ma in kuna cikin jin daɗinku, musamman lokacin da kuke bukukkuwanku, kamar Bikin Sabon Wata da dai kowane Bikinku, za ku hura waɗannan kakaki lokacin da kuke miƙa hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama, za su kuma zama muku abin tunawa a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
« Au jour de ta joie, à tes fêtes et aux débuts de tes mois, tu sonneras des trompettes sur tes holocaustes et sur les sacrifices d'actions de grâces, et ils seront pour toi un mémorial devant ton Dieu. Je suis Yahvé ton Dieu. »
11 A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
La deuxième année, au deuxième mois, le vingtième jour du mois, la nuée se retira de dessus le tabernacle de l'alliance.
12 Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
Les enfants d'Israël partirent du désert du Sinaï, et la nuée resta dans le désert de Paran.
13 Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
Ils s'avancèrent d'abord selon le commandement de Yahvé par Moïse.
14 Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
D'abord, l'étendard du camp des fils de Juda s'avança selon leurs armées. Nachshon, fils d'Amminadab, était à la tête de son armée.
15 Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
Nethaneel, fils de Zuar, était à la tête de l'armée de la tribu des fils d'Issacar.
16 Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
Eliab, fils de Hélon, était à la tête de l'armée de la tribu des fils de Zabulon.
17 Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
Le tabernacle fut démonté; les fils de Gershon et les fils de Merari, qui portaient le tabernacle, partirent en avant.
18 Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
La bannière du camp de Ruben s'avança, selon leurs armées. Elizur, fils de Shedeur, était à la tête de son armée.
19 Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
Shelumiel, fils de Zurishaddai, commandait l'armée de la tribu des fils de Siméon.
20 Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
Eliasaph, fils de Deuel, était à la tête de l'armée de la tribu des fils de Gad.
21 Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
Les Kehathites s'avancèrent, portant le sanctuaire. Les autres ont monté le tabernacle avant leur arrivée.
22 Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
L'étendard du camp des fils d'Éphraïm s'avançait selon leurs armées. Élischama, fils d'Ammihud, était à la tête de son armée.
23 Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
Gamaliel, fils de Pedahzur, était à la tête de l'armée de la tribu des fils de Manassé.
24 Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
Abidan, fils de Gideoni, était à la tête de l'armée de la tribu des fils de Benjamin.
25 A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
L'étendard du camp des fils de Dan, qui était l'arrière-garde de tous les camps, se mit en marche selon leurs armées. Ahiezer, fils d'Ammishaddai, était à la tête de son armée.
26 Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
Pagiel, fils d'Ochran, commandait l'armée de la tribu des fils d'Aser.
27 Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
Ahira, fils d'Enan, était à la tête de l'armée de la tribu des fils de Nephtali.
28 Wannan shi ne tsarin tafiyar ɓangarorin Isra’ilawa, sa’ad da sukan kama hanya.
Tels furent les déplacements des enfants d'Israël, selon leurs armées, et ils partirent.
29 Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
Moïse dit à Hobab, fils de Réuel, le Madianite, beau-père de Moïse: « Nous sommes en route pour le lieu dont Yahvé a dit: « Je te le donnerai ». Viens avec nous, et nous te traiterons bien, car Yahvé a dit du bien d'Israël. »
30 Ya amsa, ya ce “A’a, ba zan tafi ba; zan koma ƙasata da kuma wurin mutanena.”
Il lui dit: « Je n'irai pas, mais je m'en irai dans mon pays et dans ma famille. »
31 Amma Musa ya ce, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu. Ka san inda ya kamata mu kafa sansani a hamada, za ka kuma zama idanunmu.
Moïse dit: « Ne nous quitte pas, je t'en prie, car tu sais comment nous devons camper dans le désert, et tu peux être nos yeux.
32 In ka zo tare da mu, za mu raba duk abin alherin Ubangiji ya ba mu tare da kai.”
Il en sera, si tu pars avec nous - oui, il en sera ainsi - que tout le bien que Yahvé nous fera, nous vous en ferons autant. »
33 Saboda haka suka kama hanya daga dutsen Ubangiji, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji ya ja gabansu a waɗannan kwanaki uku, don yă samo musu masauƙi.
Ils partirent de la montagne de Yahvé pour trois jours de marche. L'arche de l'alliance de l'Éternel les précéda de trois jours de marche, pour leur chercher un lieu de repos.
34 A duk lokacin da suka tashi daga sansani, girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
La nuée de l'Éternel était sur eux pendant le jour, lorsqu'ils quittèrent le camp.
35 Duk kuma sa’ad da akwatin ya kama hanya, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji! Ka sa maƙiyanka su warwatse; masu ƙinka kuma su gudu a gabanka.”
Lorsque l'arche s'avança, Moïse dit: « Lève-toi, Yahvé, et que tes ennemis soient dispersés! Que ceux qui te haïssent fuient devant toi! »
36 Duk sa’ad da akwatin ya sauka kuma, sai Musa ya ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubban da ba a iya ƙidayawa na iyalan Isra’ila.”
Quand elle s'est reposée, il a dit: « Reviens, Yahvé, vers les dix mille des milliers d'Israël. »

< Ƙidaya 10 >