< Ƙidaya 10 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And YHWH speaks to Moses, saying,
2 “Ka ƙera kakaki guda biyu na azurfa, ka kuma yi amfani da su don kira taron jama’a wuri ɗaya, don kuma ka riƙa sanar da su lokacin tashi daga sansani.
“Make two trumpets of silver for yourself; you make them of beaten work, and they have been for you for the convocation of the congregation, and for the journeying of the camps;
3 Sa’ad da aka busa su biyu, dukan jama’a za su taru a gabanka a ƙofar Tentin Sujada.
and they have blown with them, and all the congregation has assembled to you at the opening of the Tent of Meeting.
4 In ɗaya ne kaɗai aka busa, sai shugabannin kabilan Isra’ila, su taru a gabanka.
And if they blow with one, then the princes, heads of the thousands of Israel, have assembled to you;
5 Sa’ad da aka ji karar busar kakaki, sai sansanin da yake a gabashi, su kama hanya.
and you have blown—a shout, and the camps which are encamping eastward have journeyed.
6 A kara ta biyu, sansanin da yake a kudanci, su kama hanya. Busan kakaki zai zama alama ta kama hanya.
And you have blown—a second shout, and the camps which are encamping southward have journeyed; they blow a shout for their journeys.
7 In don a tara jama’a ne, sai a busa kakaki, amma ba da irin alama ɗaya ba.
And in the assembling of the assembly you blow, and do not shout;
8 “’Ya’yan Haruna, firistoci ne, za su busa kakaki. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla gare ku da kuma tsararraki masu zuwa.
and sons of Aaron, the priests, blow with the trumpets; and they have been for a continuous statute to you throughout your generations.
9 Duk lokacin da za ku tafi yaƙi a ƙasarku, in akwai waɗansu da suke matsa muku, za ku yi amfani da waɗannan kakaki ta wurin hura su, alama ce, cewa za a je yaƙi. Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, yă cece ku daga maƙiyanku.
And when you go into battle in your land against the adversary who is distressing you, then you have shouted with the trumpets, and you have been remembered before your God YHWH, and you have been saved from your enemies.
10 Haka ma in kuna cikin jin daɗinku, musamman lokacin da kuke bukukkuwanku, kamar Bikin Sabon Wata da dai kowane Bikinku, za ku hura waɗannan kakaki lokacin da kuke miƙa hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama, za su kuma zama muku abin tunawa a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
And in the day of your gladness, and in your appointed times, and in the beginnings of your months, you have also blown with the trumpets over your burnt-offerings, and over the sacrifices of your peace-offerings, and they have been for a memorial to you before your God; I [am] your God YHWH.”
11 A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
And it comes to pass, in the second year, in the second month, on the twentieth of the month, the cloud has gone up from off the Dwelling Place of the Testimony,
12 Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
and the sons of Israel journey in their journeys from the wilderness of Sinai, and the cloud dwells in the wilderness of Paran;
13 Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
and they journey at first by the command of YHWH in the hand of Moses.
14 Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
And the standard of the camp of the sons of Judah journeys in the first [place], by their hosts, and over its host [is] Nahshon son of Amminadab.
15 Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
And over the host of the tribe of the sons of Issachar [is] Nathaneel son of Zuar.
16 Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
And over the host of the tribe of the sons of Zebulun [is] Eliab son of Helon.
17 Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
And the Dwelling Place has been taken down, and the sons of Gershon and the sons of Merari have journeyed, carrying the Dwelling Place.
18 Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
And the standard of the camp of Reuben has journeyed, by their hosts, and over its host [is] Elizur son of Shedeur.
19 Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
And over the host of the tribe of the sons of Simeon [is] Shelumiel son of Zurishaddai.
20 Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
And over the host of the tribe of the sons of Gad [is] Eliasaph son of Deuel.
21 Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
And the Kohathites have journeyed, carrying the Dwelling Place, and the [others] have raised up the Dwelling Place until their coming in.
22 Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
And the standard of the camp of the sons of Ephraim has journeyed, by their hosts, and over its host [is] Elishama son of Ammihud.
23 Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
And over the host of the tribe of the sons of Manasseh [is] Gamalial son of Pedahzur.
24 Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
And over the host of the tribe of the sons of Benjamin [is] Abidan son of Gideoni.
25 A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
And the standard of the camp of the sons of Dan has journeyed (rearward to all the camps), by their hosts, and over its host [is] Ahiezer son of Ammishaddai.
26 Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
And over the host of the tribe of the sons of Asher [is] Pagiel son of Ocran.
27 Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
And over the host of the tribe of the sons of Naphtali [is] Ahira son of Enan.
28 Wannan shi ne tsarin tafiyar ɓangarorin Isra’ilawa, sa’ad da sukan kama hanya.
These [are] the journeys of the sons of Israel by their hosts when they journey.
29 Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
And Moses says to Hobab son of Raguel the Midianite, father-in-law of Moses, “We are journeying to the place of which YHWH has said, I give it to you; go with us, and we have done good to you, for YHWH has spoken good concerning Israel.”
30 Ya amsa, ya ce “A’a, ba zan tafi ba; zan koma ƙasata da kuma wurin mutanena.”
And he says to him, “I do not go; but I go to my land and to my family.”
31 Amma Musa ya ce, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu. Ka san inda ya kamata mu kafa sansani a hamada, za ka kuma zama idanunmu.
And he says, “Please do not forsake us, because you have known our encamping in the wilderness, and you have been to us for eyes;
32 In ka zo tare da mu, za mu raba duk abin alherin Ubangiji ya ba mu tare da kai.”
and it has come to pass, when you go with us—indeed, it has come to pass—that good which YHWH does kindly with us, we have done it kindly to you.”
33 Saboda haka suka kama hanya daga dutsen Ubangiji, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji ya ja gabansu a waɗannan kwanaki uku, don yă samo musu masauƙi.
And they journey from the mountain of YHWH a journey of three days; and the Ark of the Covenant of YHWH is journeying before them [for] the journey of three days, to spy out a resting place for them;
34 A duk lokacin da suka tashi daga sansani, girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
and the cloud of YHWH [is] on them by day, in their journeying from the camp.
35 Duk kuma sa’ad da akwatin ya kama hanya, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji! Ka sa maƙiyanka su warwatse; masu ƙinka kuma su gudu a gabanka.”
And it comes to pass in the journeying of the Ark, that Moses says, “Rise, O YHWH, and Your enemies are scattered, and those hating You flee from Your presence.”
36 Duk sa’ad da akwatin ya sauka kuma, sai Musa ya ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubban da ba a iya ƙidayawa na iyalan Isra’ila.”
And in its resting he says, “Return, O YHWH, [to] the myriads, the thousands of Israel.”