< Ƙidaya 10 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
Jahve reče Mojsiju:
2 “Ka ƙera kakaki guda biyu na azurfa, ka kuma yi amfani da su don kira taron jama’a wuri ɗaya, don kuma ka riƙa sanar da su lokacin tashi daga sansani.
“Napravi sebi dvije trube; napravi ih od kovana srebra. Neka ti služe za sazivanje zajednice i za pokretanje tabora.
3 Sa’ad da aka busa su biyu, dukan jama’a za su taru a gabanka a ƙofar Tentin Sujada.
Kad se u njih zatrubi, neka se sva zajednica skupi k tebi na ulazu u Šator sastanka.
4 In ɗaya ne kaɗai aka busa, sai shugabannin kabilan Isra’ila, su taru a gabanka.
Ako li se zatrubi u jednu, neka se k tebi skupe glavari izraelski, tisućnici.
5 Sa’ad da aka ji karar busar kakaki, sai sansanin da yake a gabashi, su kama hanya.
Kad popratite trubljenje bojnim poklikom, neka krenu logori utaboreni na istočnoj strani.
6 A kara ta biyu, sansanin da yake a kudanci, su kama hanya. Busan kakaki zai zama alama ta kama hanya.
Kad popratite trubljenje bojnim poklikom po drugi put, neka krenu logori utaboreni s južne strane: neka se trubljenje poprati bojnim poklikom da oni krenu.
7 In don a tara jama’a ne, sai a busa kakaki, amma ba da irin alama ɗaya ba.
Trubite i da skupite zajednicu, ali bez bojnog poklika.
8 “’Ya’yan Haruna, firistoci ne, za su busa kakaki. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla gare ku da kuma tsararraki masu zuwa.
Neka u trube trube svećenici, sinovi Aronovi. Neka vam to bude trajnom uredbom za vaše naraštaje.
9 Duk lokacin da za ku tafi yaƙi a ƙasarku, in akwai waɗansu da suke matsa muku, za ku yi amfani da waɗannan kakaki ta wurin hura su, alama ce, cewa za a je yaƙi. Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, yă cece ku daga maƙiyanku.
Kad u svojoj zemlji pođete u rat na neprijatelja koji vas pritisne, zaorite na trube s bojnim poklikom, i Jahve, Bog vaš, sjetit će se vas i bit ćete izbavljeni od svojih neprijatelja.
10 Haka ma in kuna cikin jin daɗinku, musamman lokacin da kuke bukukkuwanku, kamar Bikin Sabon Wata da dai kowane Bikinku, za ku hura waɗannan kakaki lokacin da kuke miƙa hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama, za su kuma zama muku abin tunawa a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
Na dan svoje svečanosti, svojih blagdana ili svojih mjesečevih mlađaka, dok prinosite svoje paljenice i pričesnice, trubite u trube. Neka to za vas bude spomen pred Bogom vašim. Ja sam Jahve, Bog vaš.”
11 A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
Druge godine drugoga mjeseca dvadesetog dana u mjesecu diže se oblak iznad Prebivališta svjedočanstva.
12 Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
Tada se Izraelci zapute iz Sinajske pustinje na svoja putovanja. Oblak se zaustavi u pustinji Paranu.
13 Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
Tako na Jahvinu zapovijed danu Mojsiju krenuše prvi put.
14 Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
Prva je krenula zastava tabora Judinih sinova u svojim četama. Nad njihovom vojskom bijaše Nahšon, sin Aminadabov;
15 Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
nad vojskom plemena Jisakarovaca stajaše Netanel, sin Suarov,
16 Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
a nad vojskom plemena Zebulunovaca bijaše Eliab, sin Helonov.
17 Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
Zatim, pošto je rastavljeno Prebivalište, krenuše Geršonovci i Merarijevci noseći Prebivalište.
18 Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
Potom krenu zastava tabora Rubenova u svojim četama. Nad njihovom vojskom bijaše Elisur, sin Šedeurov;
19 Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
nad vojskom plemena Šimunovaca stajao je Šelumiel, sin Surišadajev;
20 Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
nad vojskom plemena Gadovaca bio je Elijasaf, sin Deuelov.
21 Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
Potom krenuše Kehatovci noseći posvećene predmete. Tako je Prebivalište bilo podignuto prije njihova dolaska.
22 Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
Onda krenu zastava tabora Efrajimovaca u svojim četama. Nad njihovom vojskom bijaše Elišama, sin Amihudov,
23 Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
nad vojskom plemena Manašeovaca stajaše Gamliel, sin Pedahsurov;
24 Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
nad vojskom plemena Benjaminovaca bijaše Abidan, sin Gidonijev.
25 A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
A kao zalazna straža za sve tabore krenu, u svojim četama, zastava tabora Danovaca. Nad njihovom je vojskom stajao Ahiezer, sin Amišadajev.
26 Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
Nad vojskom plemena Ašerovaca bio je Pagiel, sin Okranov;
27 Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
a nad vojskom plemena Naftalijevaca bio je Ahira, sin Enanov.
28 Wannan shi ne tsarin tafiyar ɓangarorin Isra’ilawa, sa’ad da sukan kama hanya.
Takav je bio red putovanja Izraelaca svrstanih u svoje čete. Tako su putovali.
29 Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
Mojsije reče Hobabu, sinu Midjanca Reuela, Mojsijeva tasta: “Zaputili smo se u kraj o kojemu je Jahve rekao: 'Dat ću vam ga!' Pođi s nama i dobro ćemo ti činiti, jer je Jahve obećao sreću Izraelu.”
30 Ya amsa, ya ce “A’a, ba zan tafi ba; zan koma ƙasata da kuma wurin mutanena.”
“Ne idem”, odgovori mu, “nego se vraćam u svoju zemlju; k svojima se vraćam.”
31 Amma Musa ya ce, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu. Ka san inda ya kamata mu kafa sansani a hamada, za ka kuma zama idanunmu.
“Molim te, ne ostavljaj nas!” - reče. “Budući da znaš gdje nam se treba u pustinji utaboriti, valjat ćeš nam kao oči.
32 In ka zo tare da mu, za mu raba duk abin alherin Ubangiji ya ba mu tare da kai.”
Ako s nama pođeš, dobročinstva koja nam Jahve bude udijelio s tobom ćemo dijeliti.”
33 Saboda haka suka kama hanya daga dutsen Ubangiji, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji ya ja gabansu a waɗannan kwanaki uku, don yă samo musu masauƙi.
Od Jahvina brda putovali su tri dana hoda. Kovčeg Jahvina saveza išao je pred njima ta tri dana hoda da im potraži mjesto odmora.
34 A duk lokacin da suka tashi daga sansani, girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
Danju je opet Jahvin oblak bio nad njima, kako bi se iz tabora zaputili.
35 Duk kuma sa’ad da akwatin ya kama hanya, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji! Ka sa maƙiyanka su warwatse; masu ƙinka kuma su gudu a gabanka.”
Kad bi Kovčeg polazio, Mojsije bi rekao: “Ustani, Jahve! Neprijatelji tvoji neka se rasprše! Koji tebe mrze nek' bježe pred tobom!”
36 Duk sa’ad da akwatin ya sauka kuma, sai Musa ya ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubban da ba a iya ƙidayawa na iyalan Isra’ila.”
A kad bi se zaustavljao, popratio bi: “Vrati se, o Jahve! Izraelu ti si tisuće bezbrojne!”