< Ƙidaya 10 >
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
耶和华晓谕摩西说:
2 “Ka ƙera kakaki guda biyu na azurfa, ka kuma yi amfani da su don kira taron jama’a wuri ɗaya, don kuma ka riƙa sanar da su lokacin tashi daga sansani.
“你要用银子做两枝号,都要锤出来的,用以招聚会众,并叫众营起行。
3 Sa’ad da aka busa su biyu, dukan jama’a za su taru a gabanka a ƙofar Tentin Sujada.
吹这号的时候,全会众要到你那里,聚集在会幕门口。
4 In ɗaya ne kaɗai aka busa, sai shugabannin kabilan Isra’ila, su taru a gabanka.
若单吹一枝,众首领,就是以色列军中的统领,要聚集到你那里。
5 Sa’ad da aka ji karar busar kakaki, sai sansanin da yake a gabashi, su kama hanya.
吹出大声的时候,东边安的营都要起行。
6 A kara ta biyu, sansanin da yake a kudanci, su kama hanya. Busan kakaki zai zama alama ta kama hanya.
二次吹出大声的时候,南边安的营都要起行。他们将起行,必吹出大声。
7 In don a tara jama’a ne, sai a busa kakaki, amma ba da irin alama ɗaya ba.
但招聚会众的时候,你们要吹号,却不要吹出大声。
8 “’Ya’yan Haruna, firistoci ne, za su busa kakaki. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla gare ku da kuma tsararraki masu zuwa.
亚伦子孙作祭司的要吹这号;这要作你们世世代代永远的定例。
9 Duk lokacin da za ku tafi yaƙi a ƙasarku, in akwai waɗansu da suke matsa muku, za ku yi amfani da waɗannan kakaki ta wurin hura su, alama ce, cewa za a je yaƙi. Sa’an nan Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, yă cece ku daga maƙiyanku.
你们在自己的地,与欺压你们的敌人打仗,就要用号吹出大声,便在耶和华—你们的 神面前得蒙纪念,也蒙拯救脱离仇敌。
10 Haka ma in kuna cikin jin daɗinku, musamman lokacin da kuke bukukkuwanku, kamar Bikin Sabon Wata da dai kowane Bikinku, za ku hura waɗannan kakaki lokacin da kuke miƙa hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama, za su kuma zama muku abin tunawa a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
在你们快乐的日子和节期,并月朔,献燔祭和平安祭,也要吹号,这都要在你们的 神面前作为纪念。我是耶和华—你们的 神。”
11 A rana ta ashirin ga wata na biyu, a shekara ta biyu, sai girgijen ya tashi daga tabanakul na Shaida.
第二年二月二十日,云彩从法柜的帐幕收上去。
12 Sai Isra’ilawa suka tashi daki-daki daga Hamadar Sinai, suna tafiya daga wuri zuwa wuri, har sai da girgijen ya tsaya a Hamadar Faran.
以色列人就按站往前行,离开西奈的旷野,云彩停住在巴兰的旷野。
13 Suka kama hanya, a wannan lokaci, bisa umarnin Ubangiji, ta wurin Musa.
这是他们照耶和华借摩西所吩咐的,初次往前行。
14 Ɓangarorin sansanin Yahuda suka fara tashi, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Nashon ɗan Amminadab ne shugaba.
按着军队首先往前行的是犹大营的纛。统领军队的是亚米拿达的儿子拿顺。
15 Netanel ɗan Zuwar ne shugaban ɓangaren kabilar Issakar,
统领以萨迦支派军队的是苏押的儿子拿坦业。
16 Eliyab ɗan Helon kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Zebulun.
统领西布伦支派军队的是希伦的儿子以利押。
17 Sa’an nan aka saukar da tabanakul ƙasa, Gershonawa da mutanen Merari da suke ɗauke da shi suka kama hanya.
帐幕拆卸,革顺的子孙和米拉利的子孙就抬着帐幕先往前行。
18 Sai ɓangarori sansanin Ruben suka biyo, bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Elizur ɗan Shedeyur ne shugaba.
按着军队往前行的是吕便营的纛。统领军队的是示丢珥的儿子以利蓿。
19 Shelumiyel ɗan Zurishaddai ne shugaban ɓangaren kabilar Simeyon,
统领西缅支派军队的是苏利沙代的儿子示路蔑。
20 Eliyasaf ɗan Deyuwel kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Gad.
统领迦得支派军队的是丢珥的儿子以利雅萨。
21 Sai Kohatawa suka kama hanya, ɗauke da kayayyaki masu tsarki, domin kafin su kai wurin da za a kafa sansani, a riga an kafa tabanakul.
哥辖人抬着圣物先往前行。他们未到以前,抬帐幕的已经把帐幕支好。
22 Biye da waɗannan kuma sai ɓangaren sansanin kabilar Efraim suka biyo bisa ga ƙa’ida da aka yi, aka kuma umarta. Elishama ɗan Ammihud ne shugaba.
按着军队往前行的是以法莲营的纛,统领军队的是亚米忽的儿子以利沙玛。
23 Gamaliyel ɗan Fedazur ne shugaban ɓangaren kabilar Manasse,
统领玛拿西支派军队的是比大蓿的儿子迦玛列。
24 Abidan ɗan Gideyoni kuma shi ne shugaban ɓangaren kabilar Benyamin.
统领便雅悯支派军队的是基多尼的儿子亚比但。
25 A ƙarshe, a matsayi masu gadin bayan dukan ɓangarori, sai ɓangaren sansanin Dan suka tashi bisa ga ƙa’idar da aka yi, aka kuma umarta. Ahiyezer ɗan Ammishaddai ne shugaba.
在诸营末后的是但营的纛,按着军队往前行。统领军队的是亚米沙代的儿子亚希以谢。
26 Fagiyel ɗan Okran ne shugaban ɓangaren kabilan Asher,
统领亚设支派军队的是俄兰的儿子帕结。
27 Ahira ɗan Enan kuma shi ne shugaban kabilar Naftali.
统领拿弗他利支派军队的是以南的儿子亚希拉。
28 Wannan shi ne tsarin tafiyar ɓangarorin Isra’ilawa, sa’ad da sukan kama hanya.
以色列人按着军队往前行,就是这样。
29 Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamidiyane surukinsa, “Yanzu fa, muna shirin tashi ne daga nan, domin mu tafi inda Ubangiji ya ce, ‘Zan ba ku.’ Ka zo tare da mu, za mu kuwa yi maka alheri, gama Ubangiji ya yi wa Isra’ilawa alkawari abubuwa masu kyau.”
摩西对他岳父—米甸人流珥的儿子何巴—说:“我们要行路,往耶和华所应许之地去;他曾说:‘我要将这地赐给你们。’现在求你和我们同去,我们必厚待你,因为耶和华指着以色列人已经应许给好处。”
30 Ya amsa, ya ce “A’a, ba zan tafi ba; zan koma ƙasata da kuma wurin mutanena.”
何巴回答说:“我不去;我要回本地本族那里去。”
31 Amma Musa ya ce, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu. Ka san inda ya kamata mu kafa sansani a hamada, za ka kuma zama idanunmu.
摩西说:“求你不要离开我们;因为你知道我们要在旷野安营,你可以当作我们的眼目。
32 In ka zo tare da mu, za mu raba duk abin alherin Ubangiji ya ba mu tare da kai.”
你若和我们同去,将来耶和华有什么好处待我们,我们也必以什么好处待你。”
33 Saboda haka suka kama hanya daga dutsen Ubangiji, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji ya ja gabansu a waɗannan kwanaki uku, don yă samo musu masauƙi.
以色列人离开耶和华的山,往前行了三天的路程;耶和华的约柜在前头行了三天的路程,为他们寻找安歇的地方。
34 A duk lokacin da suka tashi daga sansani, girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana.
他们拔营往前行,日间有耶和华的云彩在他们以上。
35 Duk kuma sa’ad da akwatin ya kama hanya, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji! Ka sa maƙiyanka su warwatse; masu ƙinka kuma su gudu a gabanka.”
约柜往前行的时候,摩西就说:“耶和华啊,求你兴起!愿你的仇敌四散!愿恨你的人从你面前逃跑!”
36 Duk sa’ad da akwatin ya sauka kuma, sai Musa ya ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubban da ba a iya ƙidayawa na iyalan Isra’ila.”
约柜停住的时候,他就说:“耶和华啊,求你回到以色列的千万人中!”