< Nehemiya 1 >

1 Kalmomin Nehemiya ɗan Hakaliya. A cikin watan Kisleb a shekara ta ashirin, yayinda nake a fadar Shusha.
Les faits de Néhémie, fils de Hacalia. Il arriva au mois de Kisleu, en la vingtième année, comme j'étais à Susan, la ville capitale,
2 Hanani, ɗaya daga cikin’yan’uwana, ya zo daga Yahuda tare da waɗansu mutane. Na kuwa tambaye shi game da raguwar Yahudawan da suka tsira daga kwasan zuwa zaman bauta, da kuma game da Urushalima.
Que Hanani, l'un de mes frères, et quelques gens, arrivèrent de Juda; et je m'enquis d'eux touchant les Juifs réchappés, qui étaient de reste de la captivité, et touchant Jérusalem.
3 Suka ce mini, “Waɗanda suka tsira daga kwasan zuwa zaman bauta da kuma suka komo cikin yankin suna cikin babban damuwa da wulaƙanci. An rushe katangar Urushalima aka kuma ƙone ƙofofin da wuta.”
Et ils me dirent: Ceux qui sont restés de la captivité, sont là dans la province, dans une grande misère et en opprobre; et la muraille de Jérusalem demeure renversée, et ses portes brûlées par feu.
4 Da na ji waɗannan abubuwa, sai na zauna na yi kuka. Na yi kwanaki ina makoki da azumi, na kuma yi addu’a a gaban Allah na sama.
Or il arriva que dès que j'eus entendu ces paroles, je m'assis, je pleurai, je menai deuil quelques jours, je jeûnai, et je fis ma prière devant le Dieu des cieux;
5 Na ce, “Ya Ubangiji Allah na sama, Allah mai girma da mai banrazana, wanda yake kiyaye alkawarinsa na ƙauna da waɗanda suke ƙaunarsa, suke kuma yin biyayya da umarnansa,
Et je dis: Je te prie, ô Eternel! Dieu des cieux, qui es le Fort, le Grand et le Terrible, qui gardes l'alliance et la gratuité à ceux qui t'aiment et qui observent tes commandements!
6 ka sa kunne ka kuma buɗe idanunka ka ji addu’ar da bawanka yake yi a gabanka dare da rana saboda bayinka, mutanen Isra’ila. Na furta zunuban da mu Isra’ilawa, har da ni da kuma gidan mahaifina muka yi maka.
Je te prie, que ton oreille soit attentive, et que tes yeux soient ouverts pour entendre la prière de ton serviteur, laquelle je te présente en ce temps-ci, jour et nuit, pour les enfants d'Israël tes serviteurs, en faisant confession des péchés des enfants d'Israël, lesquels nous avons commis contre toi; même moi et la maison de mon père, nous avons péché.
7 Mun yi mugunta gare ka. Ba mu yi biyayya da umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da ka ba wa bawanka Musa ba.
Certainement nous sommes coupables devant toi, et nous n'avons point gardé les commandements, ni les ordonnances, ni les jugements que tu as prescrits à Moïse, ton serviteur.
8 “Ka tuna da umarnan da ka ba wa bawanka Musa, kana cewa, ‘In kun yi rashin aminci, zan warwatsar da ku a cikin al’ummai,
[Mais] je te prie, souviens-toi de la parole dont tu donnas charge à Moïse, ton serviteur, en disant: Vous commettrez des crimes, et je vous disperserai parmi les peuples;
9 amma in kuka dawo gare ni kuka kuma yi biyayya da umarnaina, to, ko mutanenku da aka kwasa zuwa zaman bauta suna can wuri mafi nisa, zan tattara su daga can in kawo su wurin da na zaɓa yă zama wurin zama don Sunana.’
Puis vous retournerez à moi, et vous garderez mes commandements, et les ferez; et s'il y en a d'entre vous qui aient été chassés jusqu'à un bout des cieux, je vous rassemblerai de là, et je vous ramènerai au lieu que j'aurai choisi pour y faire habiter mon Nom.
10 “Su bayinka ne da kuma mutanenka da ka fansa ta wurin ƙarfinka mai girma da kuma hannunka mai iko.
Or ceux-ci sont tes serviteurs et ton peuple, que tu as racheté par ta grande puissance et par ta main forte.
11 Ya Ubangiji, ka kasa kunne ga addu’ar wannan bawanka da kuma ga addu’ar bayinka waɗanda suke farin cikin girmama sunanka. Ka ba wa bawanka nasara a yau ta wurinsa yă sami tagomashi a gaban wannan mutum.” Ni ne mai riƙon kwaf sarki.
Je te prie [donc], Seigneur! que ton oreille soit maintenant attentive à la prière de ton serviteur, et à la supplication de tes serviteurs, qui prennent plaisir à craindre ton Nom; et fais, je te prie, prospérer aujourd'hui ton serviteur, et fais qu'il trouve grâce envers cet homme-ci; car j'étais échanson du Roi.

< Nehemiya 1 >