< Nehemiya 9 >

1 A rana ta ashirin da huɗu ga watan nan, Isra’ilawa suka taru, suna yin azumi, suna sa rigunan makoki, suna kuma zuba toka a kansu.
Torej na štiriindvajseti dan tega meseca so se Izraelovi otroci zbrali s postom in z vrečevinami in prstjo na sebi.
2 Waɗanda suke zuriyar Isra’ilawa suka ware kansu daga dukan baƙi. Suka tsaya, suka kuma furta zunubansu da muguntar kakanninsu.
Izraelovo seme se je ločilo od vseh tujcev in stali so ter priznavali svoje grehe in krivičnosti svojih očetov.
3 Sa’ad da suke nan a tsaye, aka ɗauki awa uku ana karanta Littafin Dokar Ubangiji Allahnsu. Aka kuma ɗauki awa uku ana sujada ga Ubangiji Allahnsu.
Vstali so na svojem kraju in brali v knjigi postave Gospoda, svojega Boga, eno četrtino dneva. Drugo četrtino pa so priznavali in oboževali Gospoda, svojega Boga.
4 A kan dakalin kuwa akwai Lawiyawa, wato, Yeshuwa, Bani, Kadmiyel, Shebaniya, Bunni, Sherebiya, Bani da Kenani tsaye, waɗanda suka kira da babbar murya ga Ubangiji Allahnsu.
Tedaj so vstali na stopnicah izmed Lévijevcev: Ješúa, Baní, Kadmiél, Šebanjá, Buní, Šerebjá, Baní in Kenáni in z močnim glasom vpili h Gospodu, svojemu Bogu.
5 Lawiyawan nan, Yeshuwa, Kadmiyel, Bani, Hashabnehiya, Sherebiya, Hodiya, Shebaniya da Fetahahiya, suka ce, “Ku miƙe tsaye ku yabi Ubangiji Allahnku, wanda yake har abada abadin.” “Albarka ta tabbata ga sunanka mai ɗaukaka, bari kuma a ɗaukaka shi bisa dukan albarka da yabo.
Potem so Lévijevci Ješúa, Kadmiél, Baní, Hašabnejá, Šerebjá, Hodijá, Šebanjá in Petahjá rekli: »Vstanite in blagoslavljajte Gospoda, svojega Boga, na veke vekov in blagoslovljeno bodi tvoje veličastno ime, ki je vzvišeno nad vsem blagoslavljanjem in hvalo.«
6 Kai kaɗai ne Ubangiji. Kai ka yi sammai, har ma da sama sammai, da dukan rundunar taurari, da duniya da kuma dukan abin da yake cikinta, da tekuna da dukan abubuwan da suke cikinsu. Ka ba da rai ga kome, kuma rundunonin sama suna maka sujada.
Ti, celó ti sam si Gospod. Naredil si nebo in nebesa nebes, z vso njihovo vojsko, zemljo in vse stvari, ki so na njej, morja in vse, kar je v njih in ti jih vse ohranjaš in nebeška vojska te obožuje.
7 “Kai ne Ubangiji Allah, wanda ya zaɓi Abram, ya fitar da shi daga Ur na Kaldiyawa, ya kuma ba shi suna Ibrahim.
Ti si Gospod Bog, ki je izbral Abrama in ga privedel naprej iz Ura Kaldejcev in si mu dal ime Abraham.
8 Kai ka sami zuciyarsa da aminci a gare ka, ka kuma yi alkawari da shi cewa za ka ba zuriyarsa ƙasar Kan’aniyawa, da ta Hittiyawa, da ta Amoriyawa, da ta Ferizziyawa, da ta Yebusiyawa, da kuma ta Girgashiyawa. Ka kiyaye alkawarinka domin kai mai adalci ne.
Njegovo srce si pred seboj našel zvesto in z njim si sklenil zavezo, da daš deželo Kánaancev, Hetejcev, Amoréjcev, Perizéjcev, Jebusejcev in Girgašéjcev, da jo daš, pravim, njegovemu semenu in izvršil si svoje besede, kajti pravičen si.
9 “Ka ga wahalar kakanninmu a Masar; ka kuwa ji kukansu a Jan Teku.
Videl si stisko naših očetov v Egiptu in prisluhnil njihovemu vpitju pri Rdečem morju
10 Ka aika da alamu masu banmamaki da al’ajabai a kan Fir’auna, a kan dukan shugabanninsa da kuma a kan dukan mutanen ƙasarsa, gama ka ga irin danniyar da suka yi wa mutanenka. Ka samo wa kanka suna, wadda ta dawwama har yă zuwa yau.
in pokazal si znamenja in čudeže na faraonu in na vseh njegovih služabnikih in na vsemu ljudstvu njegove dežele, kajti ti veš, da so ponosno postopali zoper njih. Tako si si pridobil ime, kakor je to ta dan.
11 Ka raba teku a gaban kakanninmu, saboda su wuce cikinsa a busasshiyar ƙasa, amma ka hallaka masu binsu cikin zurfafa, nutse kamar dutse a cikin ruwa.
Pred njimi si razdelil morje, tako da so šli skozi sredo morja po suhi deželi. Njihove preganjalce si vrgel v globine kakor kamen v sredo mogočnih vodá.
12 Da rana ka bishe kakanninmu da girgije, da dare kuwa ka bishe su da ginshiƙin wuta don ka ba su haske a hanyar da za su bi.
Poleg tega si jih podnevi vodil z oblačnim stebrom in ponoči z ognjenim stebrom, da bi jim dal svetlobo na poti, po kateri naj bi šli.
13 “Ka sauko a kan Dutsen Sinai; ka yi musu magana daga sama. Ka ba su ƙa’idodi da dokokin da suke masu adalci da kuma daidai, ka ba su farillai da umarnai da suke da kyau.
Ti si tudi prihajal dol na goro Sinaj in govoril z njimi iz nebes in jim dajal prave sodbe in resnične postave, dobre zakone in zapovedi.
14 Ka sanar da su Asabbacinka mai tsarki, ka kuma ba su umarnai, da farillai, da kuma dokoki ta wurin bawanka Musa.
Dal si jim spoznati svoj sveti šabat in jim zapovedal predpise, zakone in postave, po roki svojega služabnika Mojzesa
15 Cikin yunwansu ka ba su burodi daga sama, cikin ƙishirwansu kuma ka fitar musu ruwa daga dutse. Ka faɗa musu su shiga su mallaki ƙasar da ka rantse ta wurin ɗaga hannu cewa za ka ba su.
in dajal si jim kruh iz nebes za njihovo lakoto in zanje si za njihovo žejo privedel vodo iz skale in jim obljubljal, da naj bi šli in vzeli v last deželo, ki si jim jo prisegel, da jim jo daš.
16 “Amma su kakanninmu, suka yi fariya da taurinkai, ba su kuwa yi biyayya ga umarnanka ba.
Toda oni in naši očetje so ponosno postopali in otrdili svoje vratove in niso prisluhnili tvojim zapovedim
17 Suka ƙi su saurare ka, suka kāsa tuna da mu’ujizan da ka aikata a cikinsu. Suka yi taurinkai, cikin tawayensu kuma suka naɗa shugaba don su koma bautarsu. Amma kai Allah ne mai gafartawa, mai alheri da jinƙai, mai jinkirin fushi, mai yalwar ƙauna. Saboda haka ba ka yashe su ba,
in odklonili so ubogati niti niso razmišljali o tvojih čudežih, ki si jih storil med njimi, temveč so otrdili svoje vratove in v svojem uporu so določili poveljnika, da se vrnejo k svojemu suženjstvu. Toda ti si Bog, pripravljen odpustiti, milostljiv in usmiljen, počasen za jezo in velike prijaznosti in jih nisi zapustil.
18 ko ma sa’ad da suka yi wa kansu siffar ɗan maraƙi, suka ce, ‘Wannan shi ne allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar,’ ko sa’ad da suka yi saɓo mai bantsoro.
Da, ko so si naredili ulito tele in rekli: »To je tvoj Bog, ki te je privedel iz Egipta, « in počeli so veliko izzivanj,
19 “Saboda jinƙanka mai girma, ba ka yashe su a hamada ba. Da rana, ginshiƙin girgije bai daina bishe su a hanyarsu ba, da dare kuma ginshiƙin wuta bai daina haskakawa a hanyar da za su bi ba.
jih vendar ti v svojih mnogoterih usmiljenih nisi zapustil v divjini. Podnevi oblačen steber ni odšel od njih, da jih vodi po poti niti ognjeni steber ponoči, da jim kaže svetlobo in pot, po kateri naj bi šli.
20 Ka ba da Ruhunka mai kyau don yă koyar da su. Ba ka janye Manna naka daga bakunansu ba, ka kuma ba su ruwa don ƙishirwansu.
Dajal si jim tudi svojega dobrega duha, da jih pouči in pred njihovimi usti nisi zadržal mane in za njihovo žejo si jim dajal vodo.
21 Shekaru arba’in ka riƙe su a cikin hamada; ba su rasa kome ba, rigunansu ba su yage ba, ƙafafunsu kuwa ba su kumbura ba.
Da, štirideset let si jih podpiral v divjini, tako da jim ničesar ni manjkalo. Njihova oblačila se niso postarala in njihova stopala niso otekla.
22 “Ka ba su mulkoki da al’ummai, kana ba su har ma da ƙasashen da suke jeji. Suka ci ƙasar Sihon na sarkin Heshbon da ƙasar Og inda sarkin Bashan yake mulki.
Poleg tega si jim dajal kraljestva in narode in razdelil si jih po pokrajinah. Tako so vzeli v last deželo Sihón, deželo hešbónskega kralja in deželo bašánskega kralja Oga.
23 Ka sa’ya’yansu maza suka yi yawa kamar taurarin sararin sama, ka kuma kawo su cikin ƙasar da ka faɗa wa kakanninsu su shiga su mallake.
Tudi njihove otroke si pomnožil kakor zvezd na nebu in jih privedel v deželo, glede katere si njihovim očetom obljubil, da naj bi šli vanjo, da jo vzamejo v last.
24 ’Ya’yansu maza suka shiga suka kuma mallaki ƙasar. A gabansu ka rinjayi Kan’aniyawan da suke zama a cikin ƙasar; ka ba da Kan’aniyawa a gare su, tare da sarakunansu da kuma mutanen ƙasar, su yi da su yadda suke so.
Tako so otroci šli v deželo, jo vzeli v last in ti si pred njimi podjarmil prebivalce dežele, Kánaance in jih dal v njihove roke, z njihovimi kralji in ljudstvom dežele, da so lahko z njimi storili, kakor so hoteli.
25 Suka kame birane masu katanga masu ƙarfi, da ƙasa masu ba da amfani; suka mallaki gidaje cike da kowane irin abu mai kyau, da rijiyoyin da aka riga aka haƙa, da gonakin inabi, da gonakin itatuwan zaitun da kuma itatuwan ba da’ya’ya a yalwace a ciki. Suka ci suka ƙoshi, suka kuma yi ƙiba; suka ji daɗi cikin alherinka mai girma.
Zavzeli so utrjena mesta in tolsto deželo in vzeli v last hiše, polne vseh dobrin, izkopane vodnjake, vinograde, oljčne nasade in sadnih dreves v obilju. Tako so jedli, bili nasičeni, se odebelili in se razveseljevali v tvoji veliki dobroti.
26 “Amma suka yi rashin biyayya suka kuma yi tawaye gare ka; suka sa dokarka a bayansu. Suka kashe annabawanka waɗanda suka gargaɗe su don su mai da su gare ka; suka aikata saɓo mai bantsoro.
Kljub temu so bili neposlušni in so se uprli zoper tebe in tvojo postavo vrgli za svoje hrbte in usmrtili tvoje preroke, ki so pričevali zoper njih, da jih obrnejo k tebi in naredili so velika izzivanja.
27 Saboda haka ka miƙa su ga abokan gābansu waɗanda suka yi musu danniya. Amma sa’ad da ake danniyarsu sai suka yi kuka gare ka. Daga sama ka ji su, cikin jinƙanka mai girma kuwa ka ba su mai ceto, wanda ya fisshe su daga hannun abokan gābansu.
Zato si jih izročil v roko njihovih sovražnikov, ki so jih stiskali. V času svoje stiske, ko so klicali k tebi, si jih uslišal iz nebes in glede na svoja mnogotera usmiljenja si jim dal rešitelje, ki so jih rešili iz roke njihovih sovražnikov.
28 “Amma nan da nan, da suka sami hutu, sai suka sāke aikata abin da yake mugu a idonka. Sai ka yashe su ga hannun abokan gābansu don su yi mulki a kansu. Sa’ad da suka yi kuka kuma gare ka, ka ji daga sama, cikin jinƙanka kuma ka fisshe su sau da sau.
Toda potem, ko so imeli počitek, so pred teboj ponovno storili zlo. Zato si jih pustil v roki njihovih sovražnikov, tako da so imeli gospostvo nad njimi. Vendar ko so se vrnili in klicali k tebi, si jih slišal iz nebes in mnogokrat si jih osvobodil glede na svoja usmiljenja.
29 “Ka gargaɗe su su dawo ga dokarka, amma suka yi fariya, suka bijire wa umarnanka. Suka yi zunubi game da farillanka waɗanda ta wurinsu ne mutum zai rayu in ya yi biyayya da su. Cikin taurinkai suka juye bayansu daga gare ka, suka zama masu taurinkai, suka kuma ƙi su saurara.
In ti pričuješ zoper njih, da bi jih lahko ponovno privedel k svoji postavi. Vendar so ponosno postopali in niso prisluhnili tvojim zapovedim, temveč so grešili zoper tvoje sodbe (katere, če jih človek izpolnjuje, bo živel v njih) in umaknili ramo in otrdili svoj vrat in niso hoteli prisluhniti.
30 Shekaru masu yawa ka yi haƙuri da su. Ta wurin Ruhunka ka gargaɗe su ta wurin annabawa. Duk da haka ba su kasa kunne ba, saboda haka ka miƙa su ga maƙwabtansu.
Vendar si jih mnogo let prenašal in zoper njih pričeval po svojem duhu v svojih prerokih, vendar niso hoteli pazljivo prisluhniti. Zato si jih dajal v roko ljudstvu dežel.
31 Amma cikin tausayinka mai girma ba ka kawo su ga ƙarshe ko ka yashe su ba, gama kai Allah ne mai alheri da kuma mai jinƙai.
Vendar jih zaradi svojih velikih usmiljenj nisi popolnoma použil niti zapustil, kajti ti si usmiljen in milostljiv Bog.
32 “To yanzu, ya Allahnmu, mai girma, mai iko, da kuma mai banrazana, wanda yake kiyaye alkawarinsa na ƙauna, kada ka bar dukan wannan wahala ta zama kamar marar muhimmanci a idanunka, wahalar da ta zo a kanmu, a kan sarakunanmu da shugabanni, a kan firistocinmu da annabawa, a kan kakanninmu da kuma dukan mutanenka, daga kwanakin sarakunan Assuriya har yă zuwa yau.
Zdaj torej, naš Bog, velik, mogočen in strašen Bog, ki ohranjaš zavezo in usmiljenje, naj se vsa stiska, ki je prišla nad nas, na naše kralje, na naše prince, na naše duhovnike, na naše očete in na vse tvoje ljudstvo, od časa asirskih kraljev do današnjega dne, ne zdi majhna pred teboj.
33 Cikin dukan abubuwan da suka faru da mu, ka kasance mai adalci; ka yi aminci, yayinda mu kuwa muka aikata mugu.
Vendar si ti pravičen v vsem, kar si privedel nad nas, kajti storil si pravilno, toda mi smo storili zlobno.
34 Sarakunanmu, da shugabanninmu, da firistocinmu da kuma kakanninmu ba su bi dokarka ba, ba su ma mai da hankali ga umarnanka ko gargaɗin da ka yi musu ba.
Niti se naši kralji, naši princi, naši duhovniki, niti naši očetje, niso držali tvoje postave, niti niso prisluhnili tvojim zapovedim in tvojim pričevanjem, s katerimi si pričeval zoper njih.
35 Ko ma yayinda suke a masarautarsu, suna jin daɗin girmar kyautatawarka gare su, cikin ƙasar mai girma, da kuma mai fāɗin da ka ba su, ba su bauta maka ko su juye daga mugayen hanyoyinsu ba.
Kajti niso služili tebi v svojem kraljestvu in v tvoji veliki dobroti, ki jim jo daješ v veliki in obilni deželi, ki jo postavljaš prednje niti se niso odvrnili od svojih zlobnih del.
36 “Amma duba, mu bayi ne a yau, bayi a ƙasar da ka ba kakanninmu don su ci amfaninta da kuma waɗansu abubuwa masu kyau da take bayarwa.
Glej, mi smo ta dan služabniki in glede dežele, ki si jo dal našim očetom, da jemo njen sad in njeno dobro, glej, mi smo služabniki v njej
37 Saboda zunubanmu, yalwar girbin da muke samu yana tafiya wurin sarakunan da ka sa a kanmu. Suna mulki bisa jikunanmu, da bisa garkenmu yadda suka ga dama. Muna cikin baƙin ciki.
in ta rojeva mnogo donosa kraljem, ki si jih zaradi naših grehov postavil nad nas. Prav tako imajo po njihovem užitku gospostvo nad našimi telesi in nad našo živino in mi smo v veliki stiski.
38 “Saboda wannan duka, muna yin zaunannen alkawari, muna sa shi a rubuce, shugabanninmu kuwa da Lawiyawanmu, da firistocinmu suna buga hatimansu a kai.”
Zaradi vsega tega delamo zanesljivo zavezo in jo zapisujemo in naši princi, Lévijevci in duhovniki, jo pečatijo.

< Nehemiya 9 >