< Nehemiya 9 >

1 A rana ta ashirin da huɗu ga watan nan, Isra’ilawa suka taru, suna yin azumi, suna sa rigunan makoki, suna kuma zuba toka a kansu.
Potom dvadcátého čtvrtého dne téhož měsíce shromáždili se synové Izraelští, a postíce se v žíních, posypali se prstí,
2 Waɗanda suke zuriyar Isra’ilawa suka ware kansu daga dukan baƙi. Suka tsaya, suka kuma furta zunubansu da muguntar kakanninsu.
(Oddělilo se pak bylo símě Izraelské ode všech cizozemců), a stojíce, vyznávali hříchy své i nepravosti otců svých.
3 Sa’ad da suke nan a tsaye, aka ɗauki awa uku ana karanta Littafin Dokar Ubangiji Allahnsu. Aka kuma ɗauki awa uku ana sujada ga Ubangiji Allahnsu.
I stáli na místech svých, a čtli v knize zákona Hospodina Boha svého čtyřikrát za den, a čtyřikrát vyznávali a klaněli se Hospodinu Bohu svému.
4 A kan dakalin kuwa akwai Lawiyawa, wato, Yeshuwa, Bani, Kadmiyel, Shebaniya, Bunni, Sherebiya, Bani da Kenani tsaye, waɗanda suka kira da babbar murya ga Ubangiji Allahnsu.
Za tím vystoupivše na výstupek Levítský Jesua a Báni, Kadmiel, Sebaniáš, Bunni, Serebiáš, Báni a Chenani, volali hlasem velikým k Hospodinu Bohu svému.
5 Lawiyawan nan, Yeshuwa, Kadmiyel, Bani, Hashabnehiya, Sherebiya, Hodiya, Shebaniya da Fetahahiya, suka ce, “Ku miƙe tsaye ku yabi Ubangiji Allahnku, wanda yake har abada abadin.” “Albarka ta tabbata ga sunanka mai ɗaukaka, bari kuma a ɗaukaka shi bisa dukan albarka da yabo.
A řekli Levítové ti, Jesua, Kadmiel, Báni, Chasabniáš, Serebiáš, Hodiáš, Sebaniáš a Petachiáš: Vstaňte, dobrořečte Hospodinu Bohu svému, od věků až na věky, a ať dobrořečí slavnému jménu jeho, a vyššímu nad každé dobrořečení i chválu.
6 Kai kaɗai ne Ubangiji. Kai ka yi sammai, har ma da sama sammai, da dukan rundunar taurari, da duniya da kuma dukan abin da yake cikinta, da tekuna da dukan abubuwan da suke cikinsu. Ka ba da rai ga kome, kuma rundunonin sama suna maka sujada.
Ty jsi, Hospodine, sám ten jediný, ty jsi učinil nebesa, nebesa nebes i všecko vojsko jejich, zemi i všecko, což jest na ní, moře i všecko, což jest v nich, obživuješ také všecko, ano i vojska nebeská před tebou se sklánějí.
7 “Kai ne Ubangiji Allah, wanda ya zaɓi Abram, ya fitar da shi daga Ur na Kaldiyawa, ya kuma ba shi suna Ibrahim.
Ty jsi, Hospodine, Bůh ten, kterýž jsi vyvolil Abrama, a vyvedl jej z Ur Kaldejských, a dal jsi jemu jméno Abraham.
8 Kai ka sami zuciyarsa da aminci a gare ka, ka kuma yi alkawari da shi cewa za ka ba zuriyarsa ƙasar Kan’aniyawa, da ta Hittiyawa, da ta Amoriyawa, da ta Ferizziyawa, da ta Yebusiyawa, da kuma ta Girgashiyawa. Ka kiyaye alkawarinka domin kai mai adalci ne.
A nalezl jsi srdce jeho věrné před sebou, a učinil jsi s ním smlouvu, že dáš zemi Kananejského, Hetejského, Amorejského, Ferezejského, Jebuzejského a Gergezejského, že dáš ji semeni jeho, a naplnils slova svá, nebo spravedlivý jsi ty.
9 “Ka ga wahalar kakanninmu a Masar; ka kuwa ji kukansu a Jan Teku.
Popatřil jsi zajisté na trápení otců našich v Egyptě, a křik jejich vyslyšel jsi při moři Rudém.
10 Ka aika da alamu masu banmamaki da al’ajabai a kan Fir’auna, a kan dukan shugabanninsa da kuma a kan dukan mutanen ƙasarsa, gama ka ga irin danniyar da suka yi wa mutanenka. Ka samo wa kanka suna, wadda ta dawwama har yă zuwa yau.
A ukazovals znamení a zázraky na Faraonovi i na všech služebnících jeho, i na všem lidu země jeho; nebo věděl jsi, že jsou pýchu provodili nad nimi. Èímž jsi dobyl sobě jména, jakž se to podnes vidí.
11 Ka raba teku a gaban kakanninmu, saboda su wuce cikinsa a busasshiyar ƙasa, amma ka hallaka masu binsu cikin zurfafa, nutse kamar dutse a cikin ruwa.
Nadto i moře jsi před nimi rozdělil, tak že přešli prostředkem moře po suše, a ty, jenž je stihali, uvrhl jsi do hlubin, jako kámen do vody veliké.
12 Da rana ka bishe kakanninmu da girgije, da dare kuwa ka bishe su da ginshiƙin wuta don ka ba su haske a hanyar da za su bi.
A sloupem oblakovým vodils je ve dne, a sloupem ohnivým v noci, osvěcuje jim cestu, kudy by jíti měli.
13 “Ka sauko a kan Dutsen Sinai; ka yi musu magana daga sama. Ka ba su ƙa’idodi da dokokin da suke masu adalci da kuma daidai, ka ba su farillai da umarnai da suke da kyau.
Potom jsi sstoupil na horu Sinai, a mluvil jsi s nimi s nebe, a vydal jsi jim soudy přímé a zákony pravé, ustanovení a přikázaní dobrá.
14 Ka sanar da su Asabbacinka mai tsarki, ka kuma ba su umarnai, da farillai, da kuma dokoki ta wurin bawanka Musa.
Též i sobotu svou svatou známu jsi jim učinil, a přikázaní, ustanovení i zákon vydals jim skrze Mojžíše, služebníka svého.
15 Cikin yunwansu ka ba su burodi daga sama, cikin ƙishirwansu kuma ka fitar musu ruwa daga dutse. Ka faɗa musu su shiga su mallaki ƙasar da ka rantse ta wurin ɗaga hannu cewa za ka ba su.
Také i chléb s nebe dal jsi jim v hladu jejich, a vodu z skály vyvedl jsi jim v žízni jejich, a rozkázal jsi jim, aby šli a dědičně vládli zemí, kterouž jsi zdvihna ruku svou, přisáhl dáti jim.
16 “Amma su kakanninmu, suka yi fariya da taurinkai, ba su kuwa yi biyayya ga umarnanka ba.
Oni pak a otcové naši pyšně sobě počínali, a zatvrdivše šíji svou, neposlouchali přikázaní tvých.
17 Suka ƙi su saurare ka, suka kāsa tuna da mu’ujizan da ka aikata a cikinsu. Suka yi taurinkai, cikin tawayensu kuma suka naɗa shugaba don su koma bautarsu. Amma kai Allah ne mai gafartawa, mai alheri da jinƙai, mai jinkirin fushi, mai yalwar ƙauna. Saboda haka ba ka yashe su ba,
Nýbrž hned nechtěli slyšeti, aniž se rozpomenuli na divné činy tvé, kteréž jsi působil při nich, a zatvrdivše šíji svou, ustavovali sobě vůdce, chtíce se navrátiti k porobení svému z zarputilosti své. Ty však, Bože, snadný k odpuštění, milostivý a lítostivý, dlouho shovívající a hojný v milosrdenství, neopustils jich.
18 ko ma sa’ad da suka yi wa kansu siffar ɗan maraƙi, suka ce, ‘Wannan shi ne allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar,’ ko sa’ad da suka yi saɓo mai bantsoro.
Ano i tehdáž, když sobě udělali tele slité a řekli: Tito jsou bohové tvoji, kteříž tě vyvedli z Egypta, a dopustili se velikého rouhání.
19 “Saboda jinƙanka mai girma, ba ka yashe su a hamada ba. Da rana, ginshiƙin girgije bai daina bishe su a hanyarsu ba, da dare kuma ginshiƙin wuta bai daina haskakawa a hanyar da za su bi ba.
Ty však pro svá mnohá slitování neopustil jsi jich na poušti. Sloup oblakový neodcházel od nich ve dne, veda je po cestě, ani sloup ohnivý v noci, osvěcuje je a cestu, po níž jíti měli.
20 Ka ba da Ruhunka mai kyau don yă koyar da su. Ba ka janye Manna naka daga bakunansu ba, ka kuma ba su ruwa don ƙishirwansu.
Nadto Ducha svého dobrého dal jsi k vyučování jich, manny své také neodjals od úst jejich, a vodu dal jsi jim v žízni jejich.
21 Shekaru arba’in ka riƙe su a cikin hamada; ba su rasa kome ba, rigunansu ba su yage ba, ƙafafunsu kuwa ba su kumbura ba.
A tak za čtyřidceti let krmil jsi je na poušti. V ničemž nedostatku neměli, oděv jejich nezvetšel, a nohy jejich se neodhnetly.
22 “Ka ba su mulkoki da al’ummai, kana ba su har ma da ƙasashen da suke jeji. Suka ci ƙasar Sihon na sarkin Heshbon da ƙasar Og inda sarkin Bashan yake mulki.
Potom dal jsi jim království a národy, kteréž jsi rozehnal do koutů, tak že dědičně obdrželi zemi Seonovu, a zemi krále Ezebon, i zemi Oga krále Bázan.
23 Ka sa’ya’yansu maza suka yi yawa kamar taurarin sararin sama, ka kuma kawo su cikin ƙasar da ka faɗa wa kakanninsu su shiga su mallake.
Syny pak jejich rozmnožil jsi jako hvězdy nebeské, a uvedl jsi je do země, o kteréž jsi byl řekl otcům jejich, že do ní vejdou, aby jí vládli.
24 ’Ya’yansu maza suka shiga suka kuma mallaki ƙasar. A gabansu ka rinjayi Kan’aniyawan da suke zama a cikin ƙasar; ka ba da Kan’aniyawa a gare su, tare da sarakunansu da kuma mutanen ƙasar, su yi da su yadda suke so.
Nebo všedše synové, dědičně obdrželi zemi tu, když jsi snížil před nimi obyvatele té země Kananejské, a dals je v ruku jejich, i krále jejich, i národy té země, aby s nimi nakládali podlé vůle své.
25 Suka kame birane masu katanga masu ƙarfi, da ƙasa masu ba da amfani; suka mallaki gidaje cike da kowane irin abu mai kyau, da rijiyoyin da aka riga aka haƙa, da gonakin inabi, da gonakin itatuwan zaitun da kuma itatuwan ba da’ya’ya a yalwace a ciki. Suka ci suka ƙoshi, suka kuma yi ƙiba; suka ji daɗi cikin alherinka mai girma.
A tak vzali města hrazená i pole úrodná, a dědičně ujali domy plné všeho dobrého, studnice vykopané, vinice a olivoví, i stromoví ovoce nesoucí velmi mnohé. I jedli, a nasyceni jsouce, vytyli, a v dobrodiní tvém hojném rozkoší oplývali.
26 “Amma suka yi rashin biyayya suka kuma yi tawaye gare ka; suka sa dokarka a bayansu. Suka kashe annabawanka waɗanda suka gargaɗe su don su mai da su gare ka; suka aikata saɓo mai bantsoro.
Když pak popouzejíce tě, zprotivili se tobě, zavrhše zákon tvůj za hřbet svůj, a proroky tvé zmordovali, kteříž jim osvědčovali, aby je obrátili k tobě, a dopouštěli se velikého rouhání,
27 Saboda haka ka miƙa su ga abokan gābansu waɗanda suka yi musu danniya. Amma sa’ad da ake danniyarsu sai suka yi kuka gare ka. Daga sama ka ji su, cikin jinƙanka mai girma kuwa ka ba su mai ceto, wanda ya fisshe su daga hannun abokan gābansu.
Dával jsi je v ruku nepřátel jejich, kteříž je ssužovali. A když v čas ssoužení svého volali k tobě, tys je s nebe vyslýchal, a podlé mnohých slitování svých dával jsi jim vysvoboditele, kteříž je vysvobozovali z ruky nepřátel jejich.
28 “Amma nan da nan, da suka sami hutu, sai suka sāke aikata abin da yake mugu a idonka. Sai ka yashe su ga hannun abokan gābansu don su yi mulki a kansu. Sa’ad da suka yi kuka kuma gare ka, ka ji daga sama, cikin jinƙanka kuma ka fisshe su sau da sau.
Mezitím, jakž jen oddechnutí měli, zase znovu činili zlé před tebou, a protož pouštěl jsi je v ruku nepřátel jejich, aby panovali nad nimi. Když se pak opět obrátili, a křičeli k tobě, tys je s nebe vyslýchal a vysvobozoval podlé slitování svých po mnohé časy.
29 “Ka gargaɗe su su dawo ga dokarka, amma suka yi fariya, suka bijire wa umarnanka. Suka yi zunubi game da farillanka waɗanda ta wurinsu ne mutum zai rayu in ya yi biyayya da su. Cikin taurinkai suka juye bayansu daga gare ka, suka zama masu taurinkai, suka kuma ƙi su saurara.
A napomínals jich, abys je obrátil k zákonu svému, ale oni pyšně sobě počínali, a neposlouchali přikázaní tvých, a proti soudům tvým hřešili, v nichžto, činil-li by je člověk, byl by živ. Nýbrž plece svého uchylujíce, šíji svou zatvrzovali, a neposlouchali.
30 Shekaru masu yawa ka yi haƙuri da su. Ta wurin Ruhunka ka gargaɗe su ta wurin annabawa. Duk da haka ba su kasa kunne ba, saboda haka ka miƙa su ga maƙwabtansu.
A však shovíval jsi jim po mnohá léta, osvědčuje jim duchem svým skrze proroky své, a když neposlouchali, dal jsi je v ruku národům zemí.
31 Amma cikin tausayinka mai girma ba ka kawo su ga ƙarshe ko ka yashe su ba, gama kai Allah ne mai alheri da kuma mai jinƙai.
Ale pro slitování svá mnohá nedals jim do konce zahynouti, aniž jsi jich opustil, proto že jsi Bůh milostivý a lítostivý.
32 “To yanzu, ya Allahnmu, mai girma, mai iko, da kuma mai banrazana, wanda yake kiyaye alkawarinsa na ƙauna, kada ka bar dukan wannan wahala ta zama kamar marar muhimmanci a idanunka, wahalar da ta zo a kanmu, a kan sarakunanmu da shugabanni, a kan firistocinmu da annabawa, a kan kakanninmu da kuma dukan mutanenka, daga kwanakin sarakunan Assuriya har yă zuwa yau.
Nyní tedy, ó Bože náš, silný, veliký, mocný a hrozný, kterýž ostříháš smlouvy a milosrdenství, nechť to není u tebe za málo, že ty všecky těžkosti na nás přišly, na krále naše, knížata naše, kněží naše, proroky naše i na otce naše, a na všecken lid tvůj, hned ode dnů králů Assyrských, až do tohoto dne,
33 Cikin dukan abubuwan da suka faru da mu, ka kasance mai adalci; ka yi aminci, yayinda mu kuwa muka aikata mugu.
Ačkoli ty jsi spravedlivý ve všech těch věcech, kteréž přišly na nás. Nebo jsi spravedlivě to učinil, ale my jsme bezbožně činili.
34 Sarakunanmu, da shugabanninmu, da firistocinmu da kuma kakanninmu ba su bi dokarka ba, ba su ma mai da hankali ga umarnanka ko gargaɗin da ka yi musu ba.
I králové naši, knížata naše, kněží naši i otcové naši neplnili zákona tvého, aniž šetřili přikázaní tvých a svědectví tvých, jimiž se jim osvědčoval.
35 Ko ma yayinda suke a masarautarsu, suna jin daɗin girmar kyautatawarka gare su, cikin ƙasar mai girma, da kuma mai fāɗin da ka ba su, ba su bauta maka ko su juye daga mugayen hanyoyinsu ba.
Nebo oni v království svém a v dobrodiní tvém hojném, kteréž jsi jim ukazoval, a v zemi široké a úrodné, kterouž jsi jim dal, nesloužili tobě, aniž se odvrátili od činů svých zlých.
36 “Amma duba, mu bayi ne a yau, bayi a ƙasar da ka ba kakanninmu don su ci amfaninta da kuma waɗansu abubuwa masu kyau da take bayarwa.
Aj, my jsme dnes manové, a to v zemi, kterouž jsi dal otcům našim, aby jedli ovoce její a dobré věci její, aj, jsme v ní manové.
37 Saboda zunubanmu, yalwar girbin da muke samu yana tafiya wurin sarakunan da ka sa a kanmu. Suna mulki bisa jikunanmu, da bisa garkenmu yadda suka ga dama. Muna cikin baƙin ciki.
Jižť úrody své vydává v hojnosti králům, kteréž jsi postavil nad námi pro hříchy naše, a oniť i nad těly našimi se potřásají, i nad hovady našimi podlé vůle své, tak že jsme u veliké úzkosti.
38 “Saboda wannan duka, muna yin zaunannen alkawari, muna sa shi a rubuce, shugabanninmu kuwa da Lawiyawanmu, da firistocinmu suna buga hatimansu a kai.”
Se vším však tím činíme smlouvu nepohnutelnou, i zapisujeme, kteréž potvrzují knížata naše, Levítové naši, i kněží naši.

< Nehemiya 9 >