< Nehemiya 8 >

1 sai dukan mutane suka taru kamar mutum guda a dandali a gaban Ƙofar Ruwa. Suka faɗa wa Ezra malamin Doka yă fitar da Littafin Dokar Musa, wanda Ubangiji ya umarta domin Isra’ila.
İsrailliler kentlerine yerleştikten sonra, yedinci ay tek vücut halinde Su Kapısı'nın karşısındaki alanda toplandılar. Bilgin Ezra'ya RAB'bin Musa aracılığıyla İsrail halkına verdiği buyrukları içeren Yasa Kitabı'nı getirmesini söylediler.
2 Saboda haka a rana ta farko ga watan bakwai, Ezra firist, ya kawo Doka a gaban taro, wanda ya ƙunshi maza da mata da dukan waɗanda za su iya fahimta.
Yedinci ayın birinci günü Kâhin Ezra Yasa Kitabı'nı halkın toplandığı yere getirdi. Dinleyip anlayabilecek kadın erkek herkes oradaydı.
3 Ya karanta Dokar da ƙarfi daga safe har tsakar rana yayinda yake a kan dandali da yake fuskantar dandali a gaban Ƙofar Ruwa, gaban maza, mata da kuma sauran mutanen da za su iya fahimta. Dukan mutane kuwa suka saurara a hankali ga karatun Littafin Dokar.
Ezra Su Kapısı'nın karşısındaki alanda kadınların, erkeklerin ve anlayabilecek yaştaki çocukların önünde, sabahtan öğlene kadar Yasa Kitabı'nı okudu. Herkes dikkatle dinledi.
4 Ezra malamin Doka ya tsaya a kan dakalin itacen da aka yi saboda wannan hidima. Kusa da shi a damansa, Mattitiya, Shema, Anahiya, Uriya, Hilkiya da Ma’asehiya suka tsaya; a hagunsa kuma Fedahiya, Mishayel, Malkiya, Hashum, Hashbaddana, Zakariya da Meshullam suka tsaya.
Bilgin Ezra toplantı için hazırlanmış ahşap bir zemin üzerinde duruyordu. Sağında Mattitya, Şema, Anaya, Uriya, Hilkiya ve Maaseya vardı. Solunda ise Pedaya, Mişael, Malkiya, Haşum, Haşbaddana, Zekeriya ve Meşullam duruyordu.
5 Sai Ezra ya buɗe littafin. Dukan mutane kuwa suka gan shi domin yana tsaye a bisa fiye da inda mutane suke tsaye; yayinda ya buɗe littafin kuwa, dukan mutane suka miƙe tsaye.
Ezra halkın gözü önünde kitabı açtı. Halktan daha yüksek bir yerde duruyordu. Kitabı açar açmaz herkes ayağa kalktı.
6 Ezra ya yabi Ubangiji, Allah mai girma; dukan mutane kuwa suka tā da hannuwansu suka amsa, “Amin! Amin!” Sa’an nan suka sunkuya suka yi wa Ubangiji sujada da fuskokinsu har ƙasa.
Ezra yüce Tanrı'ya, RAB'be övgüler sundu. Bütün halk ellerini kaldırarak, “Amin! Amin!” diye karşılık verdi. Hep birlikte eğilip yere kapanarak RAB'be tapındılar.
7 Lawiyawa, wato, su Yeshuwa, Bani, Sherebiya, Yamin, Akkub, Shabbetai, Hodiya, Ma’asehiya, Kelita, Azariya, Yozabad, Hanan da Felahiya, suka koyar da mutane a cikin Dokar yayinda mutane suke a tsaye a can.
Levililer'den Yeşu, Bani, Şerevya, Yamin, Akkuv, Şabbetay, Hodiya, Maaseya, Kelita, Azarya, Yozavat, Hanan ve Pelaya ayakta duran halka yasayı anlattılar.
8 Suka karanta daga Littafin Dokar Allah, suna sa kowa ya gane, suna kuma ba da fassarar domin mutane su fahimci abin da ake karatu.
Tanrı'nın Yasa Kitabı'nı okuyup açıkladılar, herkesin anlamasını sağlayacak biçimde yorumladılar.
9 Sa’an nan Nehemiya gwamna, Ezra firist da kuma wanda yake malamin Doka, da Lawiyawa waɗanda suke koyar da mutane, suka ce musu duka, “Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangiji Allahnku. Kada ku yi makoki ko kuka.” Gama dukan mutane suna ta kuka yayinda suke sauraran kalmomin Dokar.
Vali Nehemya, Kâhin ve Bilgin Ezra ve halka öğretmenlik yapan Levililer, “Bugün Tanrınız RAB için kutsal bir gündür. Yas tutup ağlamayın” dediler. Çünkü bütün halk Kutsal Yasa'yı dinlerken ağlıyordu.
10 Nehemiya ya ce, “Ku koma gidajenku ku ci abinci mai kyau, ku sha abin sha mai zaƙi, ku kuma aika wa wanda ba shi da shi. Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangijinmu. Kada ku yi baƙin ciki, gama farin cikin Ubangiji shi ne ƙarfinku.”
Nehemya da, “Gidin, yağlı yiyip tatlı için” dedi, “Hazırlığı olmayanlara da bir pay gönderin. Çünkü bugün Rabbimiz için kutsal bir gündür. Üzülmeyin. RAB'bin verdiği sevinç sizi güçlü kılar.”
11 Lawiyawa suka rarrashi mutane duka suna cewa, “Ku natsu, gama wannan rana ce mai tsarki. Kada ku yi baƙin ciki.”
Levililer, “Sakin olun, bugün kutsal bir gündür, üzülmeyin” diyerek halkı yatıştırdılar.
12 Sa’an nan dukan mutane suka koma gidajensu suka ci, suka sha, suka aika wa wanda ba shi da abinci, gama yanzu sun fahimci kalmomin da aka karanta musu.
Böylece herkes yiyip içmek, yiyeceklerini başkalarıyla paylaşmak ve büyük şenlik yapmak üzere evinin yolunu tuttu. Çünkü kendilerine okunanları anlamışlardı.
13 A rana ta biyu ga wata, shugabannin iyalai, tare da firistoci da Lawiyawa, suka taru kewaye da Ezra malamin Doka don su mai da hankali ga kalmomin Dokar.
Ertesi gün bütün aile başları, kâhinler ve Levililer Kutsal Yasa'nın buyruklarını öğrenmek için Bilgin Ezra'nın çevresine toplandılar.
14 Suka tarar a rubuce a cikin Doka wadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa, cewa Isra’ilawa su zauna a bukkoki a lokaci bikin watan bakwai
Yasada RAB'bin Musa aracılığıyla verdiği şu buyruğu buldular: Yedinci ayda kutlanan bayramda İsrailliler çardaklarda oturmalı.
15 kuma cewa ya kamata su yi shelar wannan magana, su kuma yaɗa ta a duk garuruwansu da kuma cikin Urushalima cewa, “Ku fita zuwa cikin ƙasar tudu ku kawo rassa daga itatuwan zaitun da na zaitun jeji, da kuma daga dargaza, da dabino da itatuwa masu ganye, don yin bukkoki”, kamar yadda yake a rubuce.
Bütün kentlerde ve Yeruşalim'de şu duyuru yapılsın: “Dağlara çıkın; yasada yazılana uygun olarak, çardak yapmak üzere zeytin, iğde, mersin ve hurma dalları, sık yapraklı ağaç dalları getirin.”
16 Sai mutanen suka fita suka dawo da rassa suka kuma yi wa kansu bukkoki a bisa rufin ɗakunansu, a cikin filaye, a shirayin gidan Allah, da ciki dandalin da yake kusa da Ƙofar Ruwa, da kuma a dandalin da yake a Ƙofar Efraim.
Böylece halk dalları getirip damlarında, evlerinin ve Tanrı Tapınağı'nın avlularında, Su Kapısı ve Efrayim Kapısı alanlarında çardaklar yaptı.
17 Dukan jama’ar da suka komo daga zaman bauta suka yi bukkoki suka kuma zauna a cikinsu. Daga kwanakin Yoshuwa ɗan Nun har yă zuwa yau, Isra’ilawa ba su taɓa yin bikinsa haka ba. Mutane suka cika da farin ciki sosai.
Sürgünden dönen herkes yaptığı çardakta oturdu. İsrailliler Nun oğlu Yeşu'nun döneminden beri böyle bir kutlama yapmamışlardı. Herkes büyük sevinç içindeydi.
18 Kowace rana, daga rana farko zuwa ƙarshe, Ezra ya karanta daga Littafin Dokar Allah. Suka yi bikin kwana bakwai, a rana ta takwas kuma suka yi muhimmin taro bisa ga ƙa’ida.
Ezra ilk günden son güne kadar, her gün Tanrı'nın Yasa Kitabı'nı okudu. Yedi gün bayram yaptılar. Sekizinci gün kural uyarınca kutsal toplantı yapıldı.

< Nehemiya 8 >