< Nehemiya 8 >

1 sai dukan mutane suka taru kamar mutum guda a dandali a gaban Ƙofar Ruwa. Suka faɗa wa Ezra malamin Doka yă fitar da Littafin Dokar Musa, wanda Ubangiji ya umarta domin Isra’ila.
Et le septième mois était venu, et les enfants d’Israël étaient dans leurs villes. Or tout le peuple s’assembla comme un seul homme dans la place qui est devant la porte des eaux; et ils dirent à Esdras, le scribe, d’apporter le livre de la loi de Moïse que le Seigneur avait prescrite à Israël.
2 Saboda haka a rana ta farko ga watan bakwai, Ezra firist, ya kawo Doka a gaban taro, wanda ya ƙunshi maza da mata da dukan waɗanda za su iya fahimta.
Esdras, le prêtre, apporta donc la loi au premier jour du septième mois devant la multitude des hommes et des femmes, et devant tous ceux qui pouvaient la comprendre.
3 Ya karanta Dokar da ƙarfi daga safe har tsakar rana yayinda yake a kan dandali da yake fuskantar dandali a gaban Ƙofar Ruwa, gaban maza, mata da kuma sauran mutanen da za su iya fahimta. Dukan mutane kuwa suka saurara a hankali ga karatun Littafin Dokar.
Et il lut dans le livre clairement, sur la place qui était devant la porte des eaux, depuis le matin jusqu’au milieu du jour, en la présence des hommes, des femmes et des sages; et les oreilles de tout le peuple étaient attentives à la lecture du livre.
4 Ezra malamin Doka ya tsaya a kan dakalin itacen da aka yi saboda wannan hidima. Kusa da shi a damansa, Mattitiya, Shema, Anahiya, Uriya, Hilkiya da Ma’asehiya suka tsaya; a hagunsa kuma Fedahiya, Mishayel, Malkiya, Hashum, Hashbaddana, Zakariya da Meshullam suka tsaya.
Et Esdras, le scribe, se tint debout sur une estrade en bois qu’il avait faite pour parler; et se tinrent aussi debout près de lui Mathathias, Séméïa, Ania, Uria, Helcia et Maasia, à sa droite; et, à sa gauche, Phadaïa, Misaël, Melchia, Hasum, Hasbadana, Zacharie et Mosollam.
5 Sai Ezra ya buɗe littafin. Dukan mutane kuwa suka gan shi domin yana tsaye a bisa fiye da inda mutane suke tsaye; yayinda ya buɗe littafin kuwa, dukan mutane suka miƙe tsaye.
Et Esdras ouvrit le livre devant tout le peuple; car il était élevé au-dessus de tout le peuple; et, lorsqu’il l’eut ouvert, tout le peuple se tint debout.
6 Ezra ya yabi Ubangiji, Allah mai girma; dukan mutane kuwa suka tā da hannuwansu suka amsa, “Amin! Amin!” Sa’an nan suka sunkuya suka yi wa Ubangiji sujada da fuskokinsu har ƙasa.
Et Esdras bénit le Seigneur le Dieu grand; et tout le peuple répondit, Amen, amen, élevant ses mains; et ils s’inclinèrent et adorèrent Dieu, inclinés vers la terre.
7 Lawiyawa, wato, su Yeshuwa, Bani, Sherebiya, Yamin, Akkub, Shabbetai, Hodiya, Ma’asehiya, Kelita, Azariya, Yozabad, Hanan da Felahiya, suka koyar da mutane a cikin Dokar yayinda mutane suke a tsaye a can.
Cependant Josué, Bani, Sérébia, Jamin, Accub, Septhaï, Odia, Maasia, Célita, Azarias, Jozabed, Hanan, Phalaïa, les Lévites, faisaient faire silence au peuple pour entendre la loi; et le peuple se tenait debout à sa place.
8 Suka karanta daga Littafin Dokar Allah, suna sa kowa ya gane, suna kuma ba da fassarar domin mutane su fahimci abin da ake karatu.
Et ils lurent dans le livre de la loi de Dieu distinctement et clairement pour que l’on comprit; et l’on comprit lorsqu’ils lisaient.
9 Sa’an nan Nehemiya gwamna, Ezra firist da kuma wanda yake malamin Doka, da Lawiyawa waɗanda suke koyar da mutane, suka ce musu duka, “Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangiji Allahnku. Kada ku yi makoki ko kuka.” Gama dukan mutane suna ta kuka yayinda suke sauraran kalmomin Dokar.
Or Néhémias (c’est Athersatha) dit, ainsi qu’Esdras, prêtre et scribe, et les Lévites qui interprétaient la loi à tout le peuple: Le jour est sanctifié au Seigneur notre Dieu; ne vous lamentez pas, et ne pleurez pas; car tout le peuple pleurait, pendant qu’il entendait les paroles de la loi.
10 Nehemiya ya ce, “Ku koma gidajenku ku ci abinci mai kyau, ku sha abin sha mai zaƙi, ku kuma aika wa wanda ba shi da shi. Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangijinmu. Kada ku yi baƙin ciki, gama farin cikin Ubangiji shi ne ƙarfinku.”
Et il leur dit: Allez, mangez des viandes grasses, et buvez du vin mêlé de miel, et envoyez des parts à ceux qui ne s’en sont point préparé, parce que c’est le saint jour du Seigneur; et ne vous attristez point; car la joie du Seigneur est notre force.
11 Lawiyawa suka rarrashi mutane duka suna cewa, “Ku natsu, gama wannan rana ce mai tsarki. Kada ku yi baƙin ciki.”
Or, les Lévites faisaient faire silence parmi tout le peuple, disant: Soyez en silence, parce que le jour est saint, et ne vous affligez point.
12 Sa’an nan dukan mutane suka koma gidajensu suka ci, suka sha, suka aika wa wanda ba shi da abinci, gama yanzu sun fahimci kalmomin da aka karanta musu.
C’est pourquoi tout le peuple s’en alla pour manger et pour boire, pour envoyer des parts et pour faire grande réjouissance, parce qu’ils avaient compris les paroles qu’il leur avait enseignées.
13 A rana ta biyu ga wata, shugabannin iyalai, tare da firistoci da Lawiyawa, suka taru kewaye da Ezra malamin Doka don su mai da hankali ga kalmomin Dokar.
Et, au second jour, les princes des familles de tout le peuple, les prêtres et les Lévites, s’assemblèrent auprès d’Esdras, le scribe, afin qu’il leur interprétât les paroles de la loi
14 Suka tarar a rubuce a cikin Doka wadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa, cewa Isra’ilawa su zauna a bukkoki a lokaci bikin watan bakwai
Ils trouvèrent écrit dans la loi, que le Seigneur avait ordonné, par l’entremise de Moïse, que les enfants d’Israël habitassent dans les tabernacles au jour solennel, au septième mois,
15 kuma cewa ya kamata su yi shelar wannan magana, su kuma yaɗa ta a duk garuruwansu da kuma cikin Urushalima cewa, “Ku fita zuwa cikin ƙasar tudu ku kawo rassa daga itatuwan zaitun da na zaitun jeji, da kuma daga dargaza, da dabino da itatuwa masu ganye, don yin bukkoki”, kamar yadda yake a rubuce.
Et qu’ils proclamassent et publiassent une annonce dans toutes leurs villes et dans Jérusalem, disant: Sortez sur la montagne, et apportez des feuilles d’olivier, des feuilles du bois le plus beau, des feuilles de myrte, des rameaux de palmiers, et des feuilles des bois touffus, afin de faire des tabernacles, comme il est écrit.
16 Sai mutanen suka fita suka dawo da rassa suka kuma yi wa kansu bukkoki a bisa rufin ɗakunansu, a cikin filaye, a shirayin gidan Allah, da ciki dandalin da yake kusa da Ƙofar Ruwa, da kuma a dandalin da yake a Ƙofar Efraim.
Ainsi, le peuple sortit, et ils en apportèrent. Et ils se firent des tabernacles, chacun sur la terrasse de sa maison, dans son vestibule, et dans les parvis de la maison de Dieu, sur la place de la porte des eaux et sur la place de la porte d’Ephraïm.
17 Dukan jama’ar da suka komo daga zaman bauta suka yi bukkoki suka kuma zauna a cikinsu. Daga kwanakin Yoshuwa ɗan Nun har yă zuwa yau, Isra’ilawa ba su taɓa yin bikinsa haka ba. Mutane suka cika da farin ciki sosai.
Toute l’assemblée de ceux qui étaient revenus de la captivité fit donc des tabernacles, et ils habitèrent dans ces tabernacles: or, les enfants d’Israël n’avaient pas fait cette fête pareillement depuis les jours de Josué, fils de Nun, jusqu’à ce jour. Ainsi, il y eut une allégresse très grande.
18 Kowace rana, daga rana farko zuwa ƙarshe, Ezra ya karanta daga Littafin Dokar Allah. Suka yi bikin kwana bakwai, a rana ta takwas kuma suka yi muhimmin taro bisa ga ƙa’ida.
Or Esdras lut dans le livre de la loi de Dieu chaque jour, depuis le premier jour jusqu’au dernier jour, et ils firent une solennité durant sept jours, et une réunion au huitième jour, suivant le rite.

< Nehemiya 8 >