< Nehemiya 8 >

1 sai dukan mutane suka taru kamar mutum guda a dandali a gaban Ƙofar Ruwa. Suka faɗa wa Ezra malamin Doka yă fitar da Littafin Dokar Musa, wanda Ubangiji ya umarta domin Isra’ila.
Or tout le peuple s'assembla, comme si ce n'eût été qu'un seul homme, en la place qui était devant la porte des eaux; et ils dirent à Esdras le Scribe qu'il apportât le Livre de la Loi de Moïse, laquelle l'Eternel avait ordonnée à Israël.
2 Saboda haka a rana ta farko ga watan bakwai, Ezra firist, ya kawo Doka a gaban taro, wanda ya ƙunshi maza da mata da dukan waɗanda za su iya fahimta.
Et ainsi le premier jour du septième mois Esdras le Sacrificateur apporta la Loi devant l'assemblée, composée d'hommes, et de femmes, et de tous ceux qui étaient capables d'entendre, afin qu'on l'écoutât.
3 Ya karanta Dokar da ƙarfi daga safe har tsakar rana yayinda yake a kan dandali da yake fuskantar dandali a gaban Ƙofar Ruwa, gaban maza, mata da kuma sauran mutanen da za su iya fahimta. Dukan mutane kuwa suka saurara a hankali ga karatun Littafin Dokar.
Et il lut au Livre, dans la place qui [était] devant la porte des eaux, depuis l'aube du jour jusqu'à midi, en la présence des hommes, et des femmes, et de ceux qui étaient capables d'entendre; et les oreilles de tout le peuple étaient attentives à la lecture du Livre de la Loi.
4 Ezra malamin Doka ya tsaya a kan dakalin itacen da aka yi saboda wannan hidima. Kusa da shi a damansa, Mattitiya, Shema, Anahiya, Uriya, Hilkiya da Ma’asehiya suka tsaya; a hagunsa kuma Fedahiya, Mishayel, Malkiya, Hashum, Hashbaddana, Zakariya da Meshullam suka tsaya.
Ainsi Esdras le Scribe se tint debout sur un lieu éminent bâti de bois, qu'on avait dressé pour cela; et il avait auprès de lui Mattitia, Sémah, Hanaja, Urija, Hilkija et Mahaséja, à sa main droite; et à sa gauche étaient Pédaja, Misaël, Malkija, Hasum, Hasbadduna, Zacharie, et Mésullam.
5 Sai Ezra ya buɗe littafin. Dukan mutane kuwa suka gan shi domin yana tsaye a bisa fiye da inda mutane suke tsaye; yayinda ya buɗe littafin kuwa, dukan mutane suka miƙe tsaye.
Et Esdras ouvrit le Livre devant tout le peuple; car il était au-dessus de tout le peuple; et sitôt qu'il l'eut ouvert, tout le peuple se tint debout.
6 Ezra ya yabi Ubangiji, Allah mai girma; dukan mutane kuwa suka tā da hannuwansu suka amsa, “Amin! Amin!” Sa’an nan suka sunkuya suka yi wa Ubangiji sujada da fuskokinsu har ƙasa.
Puis Esdras bénit l'Eternel, le grand Dieu; et tout le peuple répondit: Amen! Amen! En élevant leurs mains. Puis ils s'inclinèrent et se prosternèrent devant l'Eternel, le visage contre terre.
7 Lawiyawa, wato, su Yeshuwa, Bani, Sherebiya, Yamin, Akkub, Shabbetai, Hodiya, Ma’asehiya, Kelita, Azariya, Yozabad, Hanan da Felahiya, suka koyar da mutane a cikin Dokar yayinda mutane suke a tsaye a can.
Aussi Jésuah, Bani, Sérebja, Jamin, Hakkub, Sabéthaï, Hodija, Mahaséja, Kélita, Hazaria, Jozabad, Hanan, Pelaja, et les [autres] Lévites, faisaient comprendre la Loi au peuple, le peuple se tenant en sa place.
8 Suka karanta daga Littafin Dokar Allah, suna sa kowa ya gane, suna kuma ba da fassarar domin mutane su fahimci abin da ake karatu.
Et ils lisaient au Livre de la Loi de Dieu, ils l'expliquaient, et en donnaient l'intelligence, la faisant comprendre par l'Ecriture [même.]
9 Sa’an nan Nehemiya gwamna, Ezra firist da kuma wanda yake malamin Doka, da Lawiyawa waɗanda suke koyar da mutane, suka ce musu duka, “Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangiji Allahnku. Kada ku yi makoki ko kuka.” Gama dukan mutane suna ta kuka yayinda suke sauraran kalmomin Dokar.
Or Néhémie, qui est Attirsatha, et Esdras Sacrificateur et Scribe, et les Lévites qui instruisaient le peuple dirent à tout le peuple; ce jour est saint à l'Eternel notre Dieu, ne menez point de deuil, et ne pleurez point; car tout le peuple pleura dès qu'il eut entendu les paroles de la Loi.
10 Nehemiya ya ce, “Ku koma gidajenku ku ci abinci mai kyau, ku sha abin sha mai zaƙi, ku kuma aika wa wanda ba shi da shi. Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangijinmu. Kada ku yi baƙin ciki, gama farin cikin Ubangiji shi ne ƙarfinku.”
Puis on leur dit: Allez, mangez du plus gras, et buvez du plus doux; et envoyez-en des portions à ceux qui n'ont rien de prêt; car ce jour est saint à notre Seigneur: ne soyez donc point tristes, puisque la joie de l'Eternel est votre force.
11 Lawiyawa suka rarrashi mutane duka suna cewa, “Ku natsu, gama wannan rana ce mai tsarki. Kada ku yi baƙin ciki.”
Et les Lévites faisaient faire silence parmi tout le peuple, en disant: Faites silence, car ce jour est saint, et ne vous attristez point.
12 Sa’an nan dukan mutane suka koma gidajensu suka ci, suka sha, suka aika wa wanda ba shi da abinci, gama yanzu sun fahimci kalmomin da aka karanta musu.
Ainsi tout le peuple s'en alla pour manger et pour boire, et pour envoyer des présents, et pour faire une grande réjouissance, parce qu'ils avaient bien compris les paroles qu'on leur avait enseignées.
13 A rana ta biyu ga wata, shugabannin iyalai, tare da firistoci da Lawiyawa, suka taru kewaye da Ezra malamin Doka don su mai da hankali ga kalmomin Dokar.
Et le second jour [du mois], les Chefs des pères de tout le peuple, les Sacrificateurs, et les Lévites, s'assemblèrent vers Esdras le Scribe, pour avoir l'intelligence des paroles de la Loi.
14 Suka tarar a rubuce a cikin Doka wadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa, cewa Isra’ilawa su zauna a bukkoki a lokaci bikin watan bakwai
Ils trouvèrent donc écrit en la Loi que l'Eternel avait ordonnée par le moyen de Moïse, que les enfants d'Israël demeurassent dans des tabernacles pendant la fête solennelle au septième mois.
15 kuma cewa ya kamata su yi shelar wannan magana, su kuma yaɗa ta a duk garuruwansu da kuma cikin Urushalima cewa, “Ku fita zuwa cikin ƙasar tudu ku kawo rassa daga itatuwan zaitun da na zaitun jeji, da kuma daga dargaza, da dabino da itatuwa masu ganye, don yin bukkoki”, kamar yadda yake a rubuce.
Ce qu'ils firent savoir et qu'ils publièrent par toutes leurs villes, et à Jérusalem, en disant: Allez sur la montagne, et apportez des rameaux d'oliviers, et des rameaux d'autres arbres huileux, des rameaux de myrte, des rameaux de palmier, et des rameaux de bois branchus, afin de faire des tabernacles, selon ce qui est écrit.
16 Sai mutanen suka fita suka dawo da rassa suka kuma yi wa kansu bukkoki a bisa rufin ɗakunansu, a cikin filaye, a shirayin gidan Allah, da ciki dandalin da yake kusa da Ƙofar Ruwa, da kuma a dandalin da yake a Ƙofar Efraim.
Le peuple donc alla [sur la montagne], et ils apportèrent [des rameaux], et se firent des tabernacles, chacun sur son toit, et dans les cours [de leurs maisons], et dans les parvis de la maison de Dieu, et à la place de la porte des eaux, et à la place de la porte d'Ephraïm.
17 Dukan jama’ar da suka komo daga zaman bauta suka yi bukkoki suka kuma zauna a cikinsu. Daga kwanakin Yoshuwa ɗan Nun har yă zuwa yau, Isra’ilawa ba su taɓa yin bikinsa haka ba. Mutane suka cika da farin ciki sosai.
Et ainsi toute l'assemblée de ceux qui étaient retournés de la captivité fit des tabernacles, et ils se tinrent dans les tabernacles. Or les enfants d'Israël n'en avaient point fait de tels, depuis les jours de Josué fils de Nun, jusqu'à ce jour-là; et il y eut une fort grande joie.
18 Kowace rana, daga rana farko zuwa ƙarshe, Ezra ya karanta daga Littafin Dokar Allah. Suka yi bikin kwana bakwai, a rana ta takwas kuma suka yi muhimmin taro bisa ga ƙa’ida.
Et on lut au Livre de la Loi de Dieu chaque jour, depuis le premier jour jusqu'au dernier. Ainsi on célébra la fête solennelle pendant sept jours, et il y eut une assemblée solennelle au huitième jour, comme il était ordonné.

< Nehemiya 8 >