< Nehemiya 8 >

1 sai dukan mutane suka taru kamar mutum guda a dandali a gaban Ƙofar Ruwa. Suka faɗa wa Ezra malamin Doka yă fitar da Littafin Dokar Musa, wanda Ubangiji ya umarta domin Isra’ila.
All the people gathered as one man in the open area in front of the Water Gate. They asked Ezra the scribe to bring the Book of the Law of Moses, which Yahweh had commanded Israel.
2 Saboda haka a rana ta farko ga watan bakwai, Ezra firist, ya kawo Doka a gaban taro, wanda ya ƙunshi maza da mata da dukan waɗanda za su iya fahimta.
On the first day of the seventh month, Ezra the priest brought the law before the assembly, both men and women, and all who could hear and understand.
3 Ya karanta Dokar da ƙarfi daga safe har tsakar rana yayinda yake a kan dandali da yake fuskantar dandali a gaban Ƙofar Ruwa, gaban maza, mata da kuma sauran mutanen da za su iya fahimta. Dukan mutane kuwa suka saurara a hankali ga karatun Littafin Dokar.
He faced the open area in front of the Water Gate, and he read from it from early morning until midday, before men and women, and any who could understand, and all the people listened attentively to the book of the law.
4 Ezra malamin Doka ya tsaya a kan dakalin itacen da aka yi saboda wannan hidima. Kusa da shi a damansa, Mattitiya, Shema, Anahiya, Uriya, Hilkiya da Ma’asehiya suka tsaya; a hagunsa kuma Fedahiya, Mishayel, Malkiya, Hashum, Hashbaddana, Zakariya da Meshullam suka tsaya.
Then Ezra the scribe stood on a high wooden platform which the people had made for the purpose. Standing beside him were Mattithiah, Shema, Anaiah, Uriah, Hilkiah, and Maaseiah, on his right side; and Pedaiah, Mishael, Malchijah, Hashum, Hashbaddanah, Zechariah, and Meshullam were standing on his left side.
5 Sai Ezra ya buɗe littafin. Dukan mutane kuwa suka gan shi domin yana tsaye a bisa fiye da inda mutane suke tsaye; yayinda ya buɗe littafin kuwa, dukan mutane suka miƙe tsaye.
Ezra opened the book in the sight of all the people, for he was standing above the people, and when he opened it all the people stood up.
6 Ezra ya yabi Ubangiji, Allah mai girma; dukan mutane kuwa suka tā da hannuwansu suka amsa, “Amin! Amin!” Sa’an nan suka sunkuya suka yi wa Ubangiji sujada da fuskokinsu har ƙasa.
Ezra gave thanks to Yahweh, the great God, and all the people lifted up their hands and answered, “Amen! Amen!” Then they bowed their heads and worshiped Yahweh with their faces to the ground.
7 Lawiyawa, wato, su Yeshuwa, Bani, Sherebiya, Yamin, Akkub, Shabbetai, Hodiya, Ma’asehiya, Kelita, Azariya, Yozabad, Hanan da Felahiya, suka koyar da mutane a cikin Dokar yayinda mutane suke a tsaye a can.
Also Jeshua, Bani, Sherebiah, Jamin, Akkub, Shabbethai, Hodiah, Maaseiah, Kelita, Azariah, Jozabad, Hanan, Pelaiah—the Levites—helped the people understand the law, while the people remained in their place.
8 Suka karanta daga Littafin Dokar Allah, suna sa kowa ya gane, suna kuma ba da fassarar domin mutane su fahimci abin da ake karatu.
They read in the book, The Law of God, making it clear with interpretation and giving the meaning so the people understood the reading.
9 Sa’an nan Nehemiya gwamna, Ezra firist da kuma wanda yake malamin Doka, da Lawiyawa waɗanda suke koyar da mutane, suka ce musu duka, “Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangiji Allahnku. Kada ku yi makoki ko kuka.” Gama dukan mutane suna ta kuka yayinda suke sauraran kalmomin Dokar.
Nehemiah the governor, and Ezra the priest and scribe, and the Levites who were interpreting to the people said to all the people, “This day is holy to Yahweh your God. Do not mourn or weep.” For all the people wept when they heard the words of the law.
10 Nehemiya ya ce, “Ku koma gidajenku ku ci abinci mai kyau, ku sha abin sha mai zaƙi, ku kuma aika wa wanda ba shi da shi. Wannan rana mai tsarki ce ga Ubangijinmu. Kada ku yi baƙin ciki, gama farin cikin Ubangiji shi ne ƙarfinku.”
Then Nehemiah said to them, “Go your way, eat the fat and have something sweet to drink, and send some of it to one who has nothing prepared, for this day is holy to our Lord. Do not be grieved, for the joy of Yahweh is your strength.”
11 Lawiyawa suka rarrashi mutane duka suna cewa, “Ku natsu, gama wannan rana ce mai tsarki. Kada ku yi baƙin ciki.”
So the Levites made the people be quiet, saying, “Hush! for this day is holy. Do not be grieved.”
12 Sa’an nan dukan mutane suka koma gidajensu suka ci, suka sha, suka aika wa wanda ba shi da abinci, gama yanzu sun fahimci kalmomin da aka karanta musu.
Then all the people went their way to eat and to drink and to share food and to celebrate with great joy because they had understood the words that were made known to them.
13 A rana ta biyu ga wata, shugabannin iyalai, tare da firistoci da Lawiyawa, suka taru kewaye da Ezra malamin Doka don su mai da hankali ga kalmomin Dokar.
On the second day the leaders of the ancestors' families from all the people, the priests and the Levites, came together to Ezra the scribe to gain insight from the words of the law.
14 Suka tarar a rubuce a cikin Doka wadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa, cewa Isra’ilawa su zauna a bukkoki a lokaci bikin watan bakwai
They found written in the law how Yahweh had commanded through Moses that the people of Israel should live in shelters during the festival of the seventh month.
15 kuma cewa ya kamata su yi shelar wannan magana, su kuma yaɗa ta a duk garuruwansu da kuma cikin Urushalima cewa, “Ku fita zuwa cikin ƙasar tudu ku kawo rassa daga itatuwan zaitun da na zaitun jeji, da kuma daga dargaza, da dabino da itatuwa masu ganye, don yin bukkoki”, kamar yadda yake a rubuce.
They should make a proclamation in all their cities, and in Jerusalem, saying, “Go out into the hill country, and bring back branches from olive and wild olive trees, and from myrtle, palms and shade trees, to make shelters, as it is written.”
16 Sai mutanen suka fita suka dawo da rassa suka kuma yi wa kansu bukkoki a bisa rufin ɗakunansu, a cikin filaye, a shirayin gidan Allah, da ciki dandalin da yake kusa da Ƙofar Ruwa, da kuma a dandalin da yake a Ƙofar Efraim.
So the people went out and brought the branches back and made themselves shelters, each on their own roofs, in their courtyards, in the courts of the house of God, in the open area in front of the Water Gate, and in the square at the Gate of Ephraim.
17 Dukan jama’ar da suka komo daga zaman bauta suka yi bukkoki suka kuma zauna a cikinsu. Daga kwanakin Yoshuwa ɗan Nun har yă zuwa yau, Isra’ilawa ba su taɓa yin bikinsa haka ba. Mutane suka cika da farin ciki sosai.
All the assembly of those who had returned from captivity made shelters and lived in them. For since the days of Joshua son of Nun to that day, the people of Israel had not celebrated this festival, and so their joy was very great.
18 Kowace rana, daga rana farko zuwa ƙarshe, Ezra ya karanta daga Littafin Dokar Allah. Suka yi bikin kwana bakwai, a rana ta takwas kuma suka yi muhimmin taro bisa ga ƙa’ida.
Also day by day, from the first day to the last, Ezra read from the book of the law of God. They kept the festival for seven days and on the eighth day was a solemn assembly, in obedience to the decree.

< Nehemiya 8 >