< Nehemiya 7 >

1 Bayan an sāke gina katangar na kuma sa ƙofofi a wurarensu, sai aka naɗa masu tsaro, da mawaƙa, da Lawiyawa.
Una vez reconstruida la muralla y levantadas las puertas, nombré a los porteros, a los cantores y a los levitas.
2 Na sa ɗan’uwana Hanani tare da Hananiya shugaban fada aikin riƙon Urushalima, domin shi Hananiya mutum mai mutunci ne, mai tsoron Allah fiye da yawancin mutane.
Puse a mi hermano Hanani a cargo de Jerusalén, junto con Hananías, el comandante de la fortaleza, porque era un hombre honesto que respetaba a Dios más que muchos otros.
3 Na ce musu, “Kada a buɗe ƙofofin Urushalima da sassafe sai rana ta fito sosai. Yayinda matsaran ƙofofi suna aiki, a kulle ƙofofin a sa musu sakata kafin matsaran su tashi, wajen fāɗuwar rana. Ku kuma naɗa mazaunan Urushalima a matsayin masu tsaro, waɗansunsu a wuraren aiki, waɗansun kuma kusa da gidajensu.”
Les dije: “No permitan que se abran las puertas de Jerusalén hasta que el sol esté caliente, y asegúrate de que los guardias cierren y echen el cerrojo a las puertas mientras estén de servicio. Nombra a algunos de los habitantes de Jerusalén como guardias, para que estén en sus puestos, frente a sus propias casas”.
4 Birnin Urushalima kuwa tana da fāɗi da girma, amma mutanen da suke zama a cikinta kaɗan ne, ba a kuma gina gidaje da yawa ba tukuna.
En aquellos tiempos la ciudad era grande y con mucho espacio, pero no había mucha gente en ella, y las casas no habían sido reconstruidas.
5 Sai Allahna ya sa a zuciyata in tara manyan gari, shugabanni da talakawa don a rubuta su bisa ga iyalansu. Na sami littafin asali na waɗanda suka fara dawowa. Ga abin da na tarar an rubuta a ciki.
Mi Dios me animó a que todos -los nobles, los funcionarios y el pueblo- vinieran a registrarse según su genealogía familiar. Encontré el registro genealógico de los que habían regresado primero. Esto es lo que descubrí escrito allí.
6 Waɗannan su ne mutanen yankin da suka dawo daga zaman bautar da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kame (sun dawo Urushalima da Yahuda, kowanne zuwa garinsa.
Esta es una lista de la gente de la provincia que regresó del cautiverio. Estos eran los exiliados que habían sido llevados a Babilonia por el rey Nabucodonosor. Regresaron a Jerusalén y a Judá, a sus ciudades de origen.
7 Sun dawo tare da Zerubbabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Azariya, da Ra’amiya, da Nahamani, da Mordekai, da Bilshan, da Misfar, da Bigwai, da Nehum da kuma Ba’ana). Ga jerin mutanen Isra’ila.
Estaban dirigidos por Zorobabel, Jesúa, Nehemías, Azarías, Raamías, Nahamani, Mardoqueo, Bilsán, Misperet, Bigvai, Nehum y Baana. Este es el número de hombres del pueblo de Israel:
8 Zuriyar Farosh mutum 2,172
Los hijos de Paros, 2.172;
9 ta Shefatiya 372
los hijos de Sefatías, 372;
10 ta Ara 652
los hijos de Ara, 652;
11 ta Fahat-Mowab (ta wurin Yeshuwa da Yowab) 2,818
los hijos de Pahat-moab, (los hijos de Jesúa y Joab), 2.818;
12 ta Elam 1,254
los hijos de Elam, 1.254;
13 ta Zattu 845
los hijos de Zatu, 845;
14 ta Zakkai 760
los hijos de Zacai, 760;
15 ta Binnuyi 648
los hijos de Binui, 648;
16 ta Bebai 628
los hijos de Bebai, 628;
17 ta Azgad 2,322
los hijos de Azgad, 2.322;
18 ta Adonikam 667
los hijos de Adonicam, 667;
19 ta Bigwai 2,067
los hijos de Bigvai, 2.067.
20 ta Adin 655
Los hijos de Adin, 655.
21 ta Ater (ta wurin Hezekiya) 98
Los hijos de Ater, (hijos de Ezequías), 98;
22 ta Hashum 328
los hijos de Hasum, 328;
23 ta Bezai 324
los hijos de Bezai, 324;
24 ta Harif 112
los hijos de Harif, 112;
25 ta Gibeyon 95.
los hijos de Gabaón, 95;
26 Mutanen Betlehem da na Netofa 188
el pueblo de Belén y Netofa, 188;
27 na Anatot 128
el pueblo de Anatot, 128;
28 na Bet-Azmawet 42
el pueblo de Bet-azmavet 42;
29 na Kiriyat Yeyarim, Kefira da na Beyerot 743
el pueblo de Quiriat-jearim, Cafira y Beerot, 743;
30 na Rama da na Geba 621
el pueblo de Ramá y Geba, 621;
31 na Mikmash 122
el pueblo de Micmas, 122;
32 na Betel da na Ai 123
el pueblo de Bet-el y Ai, 123;
33 na ɗayan Nebo 52
el pueblo del otro Nebo, 52;
34 na ɗayan Elam 1,254
los hijos del otro Elam, 1.254;
35 na Harim 2 320
los hijos de Harim, 320;
36 na Yeriko 345
los hijos de Jericó, 345;
37 na Lod, da na Hadid, da na Ono 721
los hijos de Lod, Hadid y Ono, 721;
38 na Sena’a 3,930.
los hijos de Senaa, 3.930.
39 Ga zuriyar Firistoci. Zuriyar Yedahiya (ta wurin iyalin Yeshuwa) 973
Este es el número de los sacerdotes: los hijos de Jedaías (por la familia de Jesúa), 973;
40 ta Immer 1,052
los hijos de Imer, 1.052;
41 ta Fashhur 1,247
los hijos de Pasur, 1.247;
42 ta Harim 1,017.
los hijos de Harim, 1.017.
43 Ga zuriyar Lawiyawa. Zuriyar Yeshuwa da Kadmiyel (ta wurin Hodeba) 74.
Este es el número de los levitas: los hijos de Jesúa por Cadmiel (hijos de Hodavías), 74;
44 Mawaƙa. Zuriyar Asaf mutum 148.
los cantores de los hijos de Asaf, 148;
45 Ga zuriyar Matsaran Ƙofofi. Zuriyar Shallum, Ater, Talmon, Akkub, Hatita da Shobai 138.
los porteros de las familias de Salum, Ater, Talmón, Acub, Hatita y Sobai, 138.
46 Ma’aikatan haikali. Zuriyar Ziha, Hasufa, Tabbawot,
Los descendientes de estos servidores del Templo: Ziha, Hasufa, Tabaot,
47 da ta Keros, da ta Siya, da ta Fadon,
Queros, Sia, Padón,
48 da ta Lebana, da ta Hagaba, da ta Shalmai,
Lebana, Hagaba, Salmai,
49 da ta Hanan, da ta Giddel, da ta Gahar,
Hanán, Gidel, Gahar,
50 da ta Reyahiya, da ta Rezin, da ta Nekoda,
Reaía, Rezín, Necoda,
51 da ta Gazzam, da ta Uzza, da ta Faseya,
Gazam, Uza, Paseah,
52 da ta Besai, da ta Meyunawa, da ta Nefussiyawa,
Besai, Mehunim, Nefusim,
53 da ta Bakbuk, da ta Hakufa, da ta Harhur,
Bacbuc, Hacufa, Harhur,
54 da ta Bazlit, da ta Mehida, da ta Harsha,
Bazlut, Mehída, Harsa,
55 da ta Barkos, da ta Sisera, da ta Tema,
Barcos, Sísara, Tema,
56 da ta Neziya, da kuma ta Hatifa.
Nezía, y Hatifa.
57 Ga zuriyar bayin Solomon. Zuriyar Sotai, da ta Soferet, da ta Ferida,
Los descendientes de los siervos del rey Salomón: Sotai, Soferet, Perida,
58 da ta Ya’ala, da ta Darkon, da ta Giddel,
Jaala, Darcón, Gidel,
59 Shefatiya, Hattil, Fokeret-Hazzebayim, da Amon.
Sefatías, Hatil, Poqueret-hazebaim y Amón.
60 Zuriyar ma’aikatan haikali da ta bayin Solomon su 392.
El total de los siervos del Templo y de los descendientes de los siervos de Salomón era de 392.
61 Waɗansu sun hauro daga garuruwan Tel-Mela, Tel-Harsha, Kerub, Addon da Immer, amma ba su iya nuna cewa iyalansu su zuriyar Isra’ila ce ba,
Los que procedían de las ciudades de Tel-mela, Tel-Harsa, Querub, Addán e Imer no podían demostrar su genealogía familiar, ni siquiera que eran descendientes de Israel.
62 zuriyar Delahiya, Tobiya, da Nekoda 642.
Entre ellos estaban las familias de Delaía, Tobías y Necoda, 642 en total.
63 Na wajen firistoci kuwa su ne, Zuriyar Hobahiya, da ta Hakkoz, da ta Barzillai (wani mutumin da ya auri’yar Barzillai mutumin Gileyad, aka kuma kira shi da wannan suna).
Además había tres familias sacerdotales, hijos de Habaía, Cos y Barzilai. (Barzilai se había casado con una mujer descendiente de Barzilai de Galaad, y se llamaba por ese nombre).
64 Waɗannan ne aka nemi sunayensu a cikin tarihin asalin iyalai, amma ba a same su a ciki ba, saboda haka aka hana su shiga cikin firistoci, sun zama kamar marasa tsarki.
Se buscó un registro de ellos en las genealogías, pero no se encontraron sus nombres, por lo que se les prohibió servir como sacerdotes.
65 Sai gwamna ya umarce su kada su ci wani abinci mafi tsarki, sai akwai firist da zai nemi nufin Ubangiji ta wurin Urim da Tummim.
El gobernador les ordenó que no comieran nada de los sacrificios del santuario hasta que un sacerdote pudiera preguntar al Señor sobre el asunto utilizando el Urim y el Tumim.
66 Yawan jama’ar duka ya kai mutum 42,360,
El total de personas que regresaron fue de 42.360.
67 ban da bayinsu maza da mata 7,337. Suna kuma da mawaƙa maza da mata 245.
Además había 7.337 sirvientes y 245 cantores y cantoras.
68 Akwai dawakai 736, alfadarai 245
Tenían 736 caballos, 245 mulas,
69 raƙuma 435, da kuma jakuna 6,720.
435 camellos y 6.720 burros.
70 Waɗansu shugabannin iyalai suka ba da kyautai domin taimakon aiki. Gwamna ya ba da darik 1,000 na zinariya, kwanoni 50, da riguna 530 don firistoci.
Algunos de los jefes de familia hicieron contribuciones voluntarias para el trabajo. El gobernador entregó a la tesorería 1.000 dáricos de oro, 50 cuencos y 530 conjuntos de ropa para los sacerdotes.
71 Waɗansu shugabannin iyalai sun ba da darik 20,000 na zinariya da mina 2,200 na azurfa don aiki.
Algunos de los jefes de familia donaron al tesoro para la obra 20.000 dáricos de oro y 2.200 minas de plata.
72 Jimillar da sauran mutane suka bayar ta kai darik 20,000 na zinariya, minas 2,000 na azurfa, da riguna sittin da bakwai don firistoci.
El resto del pueblo donó 20.000 dáricos de oro, 2.000 minas de plata y 67 conjuntos de ropa para los sacerdotes.
73 Firistoci, da Lawiyawa, da matsaran ƙofofi, da mawaƙa, da ma’aikatan haikali tare da waɗansu mutane da kuma sauran mutanen Isra’ila, suka zauna a garuruwansu. Da wata na bakwai ya zo, Isra’ilawa kuwa sun riga sun zauna a garuruwansu,
Los sacerdotes, los levitas, los porteros, los cantores y los servidores del Templo, así como parte del pueblo y el resto de los israelitas, volvieron a vivir en sus pueblos específicos. En el séptimo mes los israelitas vivían en sus pueblos,

< Nehemiya 7 >