< Nehemiya 7 >

1 Bayan an sāke gina katangar na kuma sa ƙofofi a wurarensu, sai aka naɗa masu tsaro, da mawaƙa, da Lawiyawa.
And it came to pass, when the wall was built, and I had set up the doors, —and the doorkeepers and the singers and the Levites had been appointed,
2 Na sa ɗan’uwana Hanani tare da Hananiya shugaban fada aikin riƙon Urushalima, domin shi Hananiya mutum mai mutunci ne, mai tsoron Allah fiye da yawancin mutane.
that I gave Hanani my brother, and Hananiah captain of the castle, charge over Jerusalem, for, he, was a truly faithful man, and revered God above many.
3 Na ce musu, “Kada a buɗe ƙofofin Urushalima da sassafe sai rana ta fito sosai. Yayinda matsaran ƙofofi suna aiki, a kulle ƙofofin a sa musu sakata kafin matsaran su tashi, wajen fāɗuwar rana. Ku kuma naɗa mazaunan Urushalima a matsayin masu tsaro, waɗansunsu a wuraren aiki, waɗansun kuma kusa da gidajensu.”
And I said unto them, Let not the gates of Jerusalem be opened until, hot, be the sun, and, while they are standing by, let them close the doors, and make them fast, —setting watches, of the inhabitants of Jerusalem, every one in his watch, and every one over against his own house.
4 Birnin Urushalima kuwa tana da fāɗi da girma, amma mutanen da suke zama a cikinta kaɗan ne, ba a kuma gina gidaje da yawa ba tukuna.
Now, the city, was broad on both hands, and large, but, the people, were few in the midst thereof, —and the houses had not been built.
5 Sai Allahna ya sa a zuciyata in tara manyan gari, shugabanni da talakawa don a rubuta su bisa ga iyalansu. Na sami littafin asali na waɗanda suka fara dawowa. Ga abin da na tarar an rubuta a ciki.
So then my God put it into my heart, and I gathered together the nobles and the deputies and the people, to register their genealogy, —then found I a register roll, of them who came up at the first, and found written therein: —
6 Waɗannan su ne mutanen yankin da suka dawo daga zaman bautar da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kame (sun dawo Urushalima da Yahuda, kowanne zuwa garinsa.
These, are the sons of the province, who came up from among the Captives of the Exile, whom Nebuchadnezzar king of Babylon did exile, —but they came back to Jerusalem and to Judah, every one to his own city;
7 Sun dawo tare da Zerubbabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Azariya, da Ra’amiya, da Nahamani, da Mordekai, da Bilshan, da Misfar, da Bigwai, da Nehum da kuma Ba’ana). Ga jerin mutanen Isra’ila.
who came in with Zerubbabel, Jeshua, Nehemiah, Azariah, Raamiah, Nahamani, Mordecai, Bilshan, Mispereth, Bigvai, Nehum, Baanah, —the number of the men of the people of Israel.
8 Zuriyar Farosh mutum 2,172
The sons of Parosh, two thousand, one hundred, and seventy-two;
9 ta Shefatiya 372
The sons of Shephatiah, three hundred, and seventy-two;
10 ta Ara 652
The sons of Arah, six hundred, and fifty-two;
11 ta Fahat-Mowab (ta wurin Yeshuwa da Yowab) 2,818
The sons of Pahath-moab, belonging to the sons of Jeshua and Joab, two thousand, eight hundred, and eighteen;
12 ta Elam 1,254
The sons of Elam, a thousand, two hundred and fifty-four;
13 ta Zattu 845
The sons of Zattu, eight hundred, and forty-five;
14 ta Zakkai 760
The sons of Zaccai, seven hundred, and sixty;
15 ta Binnuyi 648
The sons of Binnui, six hundred, and forty-eight;
16 ta Bebai 628
The sons of Bebai, six hundred, and twenty-eight;
17 ta Azgad 2,322
The sons of Azgad, two thousand, three hundred, and twenty-two;
18 ta Adonikam 667
The sons of Adonikam, six hundred, and sixty-seven;
19 ta Bigwai 2,067
The sons of Bigvai, two thousand, and sixty-seven;
20 ta Adin 655
The sons of Adin, six hundred, and fifty-five;
21 ta Ater (ta wurin Hezekiya) 98
The sons of Ater, pertaining to Hezekiah, ninety-eight;
22 ta Hashum 328
The sons of Hashum, three hundred, and twenty-eight;
23 ta Bezai 324
The sons of Bezai, three hundred, and twenty-four;
24 ta Harif 112
The sons of Hariph, a hundred, and twelve;
25 ta Gibeyon 95.
The sons of Gibeon, ninety-five;
26 Mutanen Betlehem da na Netofa 188
The men of Bethlehem, and Netophah, a hundred, and eighty-eight;
27 na Anatot 128
The men of Anathoth, a hundred, and twenty-eight;
28 na Bet-Azmawet 42
The men of Beth-azmaveth, forty-two;
29 na Kiriyat Yeyarim, Kefira da na Beyerot 743
The men of Kiriath-jearim, Chephirah and Beeroth, seven hundred, and forty-three;
30 na Rama da na Geba 621
The men of Ramah and Geba, six hundred, and twenty-one;
31 na Mikmash 122
The men of Mickmas, a hundred, and twenty-two;
32 na Betel da na Ai 123
The men of Bethel and Ai, a hundred and twenty-three;
33 na ɗayan Nebo 52
The men of the other Nebo, fifty-two;
34 na ɗayan Elam 1,254
The sons of the other Elam, a thousand, two hundred, and fifty-four;
35 na Harim 2 320
The sons of Harim, three hundred, and twenty;
36 na Yeriko 345
The sons of Jericho, three hundred, and forty-five;
37 na Lod, da na Hadid, da na Ono 721
The sons of Lod, Hadid and One, seven hundred, and twenty-one;
38 na Sena’a 3,930.
The sons of Senaah, three thousand, nine hundred, and thirty;
39 Ga zuriyar Firistoci. Zuriyar Yedahiya (ta wurin iyalin Yeshuwa) 973
The priests, The sons of Jedaiah, of the house of Jeshua, nine hundred, and seventy-three;
40 ta Immer 1,052
The sons of Immer, a thousand, and fifty-two;
41 ta Fashhur 1,247
The sons of Pashhur, a thousand, two hundred, and forty-seven;
42 ta Harim 1,017.
The sons of Harim, a thousand, and seventeen;
43 Ga zuriyar Lawiyawa. Zuriyar Yeshuwa da Kadmiyel (ta wurin Hodeba) 74.
The Levites, The sons of Jeshua, of Kadmiel, of the sons of Hodevah, seventy-four;
44 Mawaƙa. Zuriyar Asaf mutum 148.
The singers, The sons of Asaph, a hundred, and forty-eight;
45 Ga zuriyar Matsaran Ƙofofi. Zuriyar Shallum, Ater, Talmon, Akkub, Hatita da Shobai 138.
The doorkeepers, The sons of Shallum, the sons of Ater, the sons of Talmon, the sons of Akkub, the sons of Hatita, the sons of Shobai, a hundred, and thirty-eight;
46 Ma’aikatan haikali. Zuriyar Ziha, Hasufa, Tabbawot,
The Nethinim, The sons of Ziha, the sons of Hasupha, the sons of Tabbaoth;
47 da ta Keros, da ta Siya, da ta Fadon,
the sons of Keros, the sons of Sia, the sons of Padon;
48 da ta Lebana, da ta Hagaba, da ta Shalmai,
the sons of Lebana, the sons of Hagaba, the sons of Salmai;
49 da ta Hanan, da ta Giddel, da ta Gahar,
the sons of Hanan, the sons of Giddel, the sons of Gahar;
50 da ta Reyahiya, da ta Rezin, da ta Nekoda,
the sons of Reaiah, the sons of Rezin, the sons of Nekoda;
51 da ta Gazzam, da ta Uzza, da ta Faseya,
the sons of Gazzam, the sons of Uzza, the sons of Paseah;
52 da ta Besai, da ta Meyunawa, da ta Nefussiyawa,
the sons of Besai, the sons of Meunim, the sons of Nephushesim;
53 da ta Bakbuk, da ta Hakufa, da ta Harhur,
the sons of Bakbuk, the sons of Hakupha, the sons of Harhur;
54 da ta Bazlit, da ta Mehida, da ta Harsha,
the sons of Bazlith, the sons of Mehida, the sons of Harsha;
55 da ta Barkos, da ta Sisera, da ta Tema,
the sons of Barkos, the sons of Sisera, the sons of Temah;
56 da ta Neziya, da kuma ta Hatifa.
the sons of Neziah, the sons of Hatipha.
57 Ga zuriyar bayin Solomon. Zuriyar Sotai, da ta Soferet, da ta Ferida,
The Sons of the Servants of Solomon, The sons of Sotai, the sons of Sophereth, the sons of Perida;
58 da ta Ya’ala, da ta Darkon, da ta Giddel,
the sons of Jaala, the sons of Darkon, the sons of Giddel;
59 Shefatiya, Hattil, Fokeret-Hazzebayim, da Amon.
the sons of Shephatiah, the sons of Hattil, the sons of Pochereth-hazzebaim, the sons of Amon.
60 Zuriyar ma’aikatan haikali da ta bayin Solomon su 392.
All the Nethinim, and the Sons of the Servants of Solomon, were three hundred, and ninety-two.
61 Waɗansu sun hauro daga garuruwan Tel-Mela, Tel-Harsha, Kerub, Addon da Immer, amma ba su iya nuna cewa iyalansu su zuriyar Isra’ila ce ba,
And, these, are they who came up from Tel-melah, Tel-harsha, Cherub, Addon, and Immer, —but they could not tell their ancestral house, nor their seed, whether, of Israel, they were:
62 zuriyar Delahiya, Tobiya, da Nekoda 642.
the sons of Delaiah, the sons of Tobiah, the sons of Nekoda, —six hundred and forty-two,
63 Na wajen firistoci kuwa su ne, Zuriyar Hobahiya, da ta Hakkoz, da ta Barzillai (wani mutumin da ya auri’yar Barzillai mutumin Gileyad, aka kuma kira shi da wannan suna).
And, of the priests, the sons of Hobaiah, the sons of Hakkoz, —the sons of Barzillai, who had taken of the daughters of Barzillai the Gileadite to wife, and was called after their name.
64 Waɗannan ne aka nemi sunayensu a cikin tarihin asalin iyalai, amma ba a same su a ciki ba, saboda haka aka hana su shiga cikin firistoci, sun zama kamar marasa tsarki.
These, sought their writing wherein they were registered, but it was not found, —so they were desecrated out of the priesthood;
65 Sai gwamna ya umarce su kada su ci wani abinci mafi tsarki, sai akwai firist da zai nemi nufin Ubangiji ta wurin Urim da Tummim.
and the governor told them, they must not eat of the most holy things, —until there should stand up a priest, with Lights and Perfections.
66 Yawan jama’ar duka ya kai mutum 42,360,
All the gathered host together, was forty-two thousand, three hundred, and sixty;
67 ban da bayinsu maza da mata 7,337. Suna kuma da mawaƙa maza da mata 245.
besides, their men-servants and maid-servants, were these, seven thousand, three hundred, and thirty-seven, —and, to them, pertained, singing-men and singing-women, two hundred, and forty-five:
68 Akwai dawakai 736, alfadarai 245
their horses, were seven hundred, and thirty-six, —their mules, two hundred, and forty-five;
69 raƙuma 435, da kuma jakuna 6,720.
camels, four hundred, and thirty-five, —asses, six thousand, seven hundred, and twenty.
70 Waɗansu shugabannin iyalai suka ba da kyautai domin taimakon aiki. Gwamna ya ba da darik 1,000 na zinariya, kwanoni 50, da riguna 530 don firistoci.
And, a portion of the ancestral chiefs, gave unto the work, —the governor, gave unto the treasury, of gold, a thousand darics, tossing bowls, fifty, tunics for priests, five hundred, and thirty;
71 Waɗansu shugabannin iyalai sun ba da darik 20,000 na zinariya da mina 2,200 na azurfa don aiki.
and, some of the ancestral chiefs, gave unto the treasury of the work, of gold, twenty thousand darics, —and, of silver, two thousand and two hundred manehs;
72 Jimillar da sauran mutane suka bayar ta kai darik 20,000 na zinariya, minas 2,000 na azurfa, da riguna sittin da bakwai don firistoci.
and, that which the rest of the people gave, was, of gold, twenty thousand darics, and, of silver, two thousand manehs, —and, tunics for priests, sixty-seven.
73 Firistoci, da Lawiyawa, da matsaran ƙofofi, da mawaƙa, da ma’aikatan haikali tare da waɗansu mutane da kuma sauran mutanen Isra’ila, suka zauna a garuruwansu. Da wata na bakwai ya zo, Isra’ilawa kuwa sun riga sun zauna a garuruwansu,
So the priests and the Levites and the door-keepers and the singers and some of the people, and the Nethinim and all Israel, took up their abode in their cities. And, when the seventh month arrived, the sons of Israel were in their cities.

< Nehemiya 7 >