< Nehemiya 6 >
1 Sa’ad da magana ta zo kunnen Sanballat, da Tobiya, da Geshem mutumin Arab da kuma sauran abokan gābanmu cewa na sāke gina katangar har babu sauran tsaguwa da ta ragu, ko da yake har zuwa lokacin ban sa ƙofofi a ƙyamare ba
І сталося, коли почув Санваллат, і Товійя, і араб Ґешем та решта наших ворогів, що я збудував мура, і що не позоста́лося в ньому ви́лому, — але до цього ча́су дверей у брамах я не повставля́в, —
2 Sanballat da Geshem suka aika mini wannan saƙo cewa, “Ka zo, mu sadu a wani ƙauye a filin Ono.” Amma makirci ne suke yi don su cuce ni;
то послав Санваллат та Ґешем до мене, говорячи: „Приходь, і вмовимося ра́зом у Кефірімі в долині Оно!“А вони замишляли зробити мені зло.
3 saboda haka sai na aika musu da wannan amsa, na ce, “Ina cikin babban aiki, ba zan kuwa iya gangarawa ba. Don me zan bar aikin yă tsaya don in gangara zuwa wurinku?”
І послав я до них послів, говорячи: „Я роблю́ велику працю, і не мо́жу прийти. На́що буде перервана ця праця, як кину її та піду́ до вас?“
4 Suka yi ta aiko mini da wannan saƙo har sau huɗu, ni kuwa na yi ta ba su amsa irin ta dā.
І посилали до мене так само чотири ра́зи, а я відповідав їм так само.
5 Sai sau na biya, Sanballat ya aiki mataimakinsa gare ni da irin saƙo guda, kuma a hannunsa akwai wasiƙar da ba a yimƙe ba
І так само Санваллат п'ятий раз прислав до ме́не слугу́ свого́, а в руці його був відкритий лист.
6 wadda aka rubuta cewa, “An ba da labari cikin al’ummai, kuma Geshem ya ce gaskiya ne, cewa kai da Yahudawa kun shirya tawaye, saboda haka kuke sāke ginin katangar. Ban da haka ma, bisa ga waɗannan rahotanni kana shirin zaman sarkinsu
А в ньому написане: „Чується серед наро́дів, і Ґашму говорить: Ти та юдеї замишляєте відділитися, тому́ то ти будуєш того мура, і хочеш бути їм за царя, за тими слова́ми.
7 har ma ka naɗa annabawa su yi wannan shela game da kai a Urushalima, su ce, ‘Akwai sarki a Yahuda!’ To, wannan rahoto zai koma wurin sarki; saboda haka ka zo, mu tattauna wannan batu.”
Та й пророків ти понаставля́в, щоб викри́кували про тебе в Єрусалимі, говорячи: Цар в Юді! А тепер цар почує оці речі. Отож, — приходь, і пора́дьмося ра́зом!“
8 Sai na aika masa wannan amsa, na ce, “Babu wani abu haka da yake faruwa; ka dai ƙaga wannan daga tunaninka ne.”
І послав я до ньо́го, говорячи: „Не було́ таких речей, про які ти говориш, бо з серця свого ти їх повимишля́в!“
9 Suka dai yi ƙoƙari su tsoratar da mu, suna cewa, “Hannuwansu za su rasa ƙarfin yin aiki, ba kuwa za su ƙare aikin ba.” Amma na yi addu’a na ce, “Yanzu, ya Allah, ka ƙarfafa hannuwana.”
Бо всі вони лякали нас, говорячи: „Нехай осла́бнуть їхні руки з цієї праці, — і не буде вона зро́блена!“Та тепер, о Боже, зміцни́ мої ру́ки!
10 Wata rana na tafi gidan Shemahiya ɗan Delahiya, ɗan Mehetabel, wanda aka hana fita a gidansa. Ya ce mini, “Mu sadu gobe a gidan Allah, a cikin haikali, mu kuma kulle ƙofofin haikali, gama mutane suna zuwa su kashe ka, tabbatacce za su zo da dare su kashe ka.”
І я ввійшов до дому Шемаї, сина Делаї, Мегетав'їлового сина, а він був заде́ржаний. І він сказав: „Умовмося піти до Божого дому, до сере́дини храму, і замкне́мо храмові двері, бо при́йдуть забити тебе, — власне вночі при́йдуть забити тебе“.
11 Amma na ce, “Ya kamata mutum kamar ni yă gudu? Ko kuwa ya kamata wani kamar ni yă shiga cikin haikali don yă ceci ransa? Ba zan tafi ba!”
Та я відказав: „Чи такий чоловік, як я, має втікати? І хто́ є такий, як я, що вві́йде до храму й буде жити? Не ввійду́!“
12 Na gane cewa Allah bai aike shi ba, ya yi annabci a kaina domin Tobiya da Sanballat sun yi hayarsa ne.
І пізнав я, що то не Бог послав його, коли він говорив на мене те пророцтво, а то Товійя та Санваллат підкупи́ли його́...
13 An yi hayarsa don yă sa in ji tsoro in yi zunubi ta yin haka, sa’an nan za su ba ni mugun suna, su wofinta ni.
Бо він був підку́плений, щоб я боявся, — і зробив так, і згрішив. Це було для них на злий погові́р, щоб обра́зити мене.
14 Ya Allahna, ka tuna da Tobiya da Sanballat, saboda abin da suka yi; ka kuma tuna da annabiya Nowadiya da sauran annabawa waɗanda suke ƙoƙari su tsorata ni.
Запам'ятай же, Боже мій, Товійї та Санваллатові за цими вчинками його́, а також пророчиці Ноадії та решті пророків, що страха́ли мене!
15 Cikin kwana hamsin da biyu aka gama gina katangar, a ranar ashirin da biyar ga watan Elul.
І був закі́нчений мур двадцятого й п'ятого дня місяця елула, за п'ятдеся́т і два дні.
16 Sa’ad da dukan abokan gābanmu suka ji haka, dukan al’umman da suke kewaye da mu suka ji tsoro, suka rasa ƙarfin halinsu, domin sun gane cewa wannan aiki an yi shi da taimakon Allahnmu ne.
І сталося, як почули про це всі наші вороги, та побачили всі народи, що були навко́ло нас, то вони впали в оча́х своїх та й пізнали, що ця праця була зро́блена від нашого Бога!
17 A waɗannan kwanaki, manyan garin Yahuda suka yi ta aika wasiƙu masu yawa zuwa ga Tobiya, shi kuma ya yi ta aika musu da amsoshi.
Тими днями також шляхе́тні юдеї писали багато своїх листів, що йшли до Товійї, а Товійїні прихо́дили до них.
18 Gama mutane da yawa a cikin Yahuda sun rantse wa Tobiya za su goyi bayansa, domin ya auri’yar Shekaniya, ɗan Ara. Ɗansa kuma, wato, Yehohanan, ya auri’yar Meshullam, ɗan Berekiya.
Бо багато-хто в Юдеї були заприся́женими при́ятелями йому, бо він був зять Шеханії, Арахового сина, а син його Єгоханан узяв дочку́ Мешуллама, Берехіїного сина.
19 Ban da haka ma, mutanen sun yi ta ba ni labarin ayyuka masu kyau da Tobiya ya yi, sa’an nan kuma suna faɗa masa duk abin da na faɗa. Tobiya kuwa ya aika wasiƙu don yă tsorata ni.
І говорили передо мною добре про нього, а слова́ мої передавали йому. Товійя посилав листи́, щоб настраха́ти мене́.