< Nehemiya 6 >
1 Sa’ad da magana ta zo kunnen Sanballat, da Tobiya, da Geshem mutumin Arab da kuma sauran abokan gābanmu cewa na sāke gina katangar har babu sauran tsaguwa da ta ragu, ko da yake har zuwa lokacin ban sa ƙofofi a ƙyamare ba
Kwasekusithi oSanibhalathi loTobiya loGeshema umArabhiya lezinye izitha zethu sezizwile ukuthi ngiwakhile umduli lokuthi kakusalanga sikhala kuwo, lanxa kuze kube yilesosikhathi ngangingamisanga izivalo emasangweni,
2 Sanballat da Geshem suka aika mini wannan saƙo cewa, “Ka zo, mu sadu a wani ƙauye a filin Ono.” Amma makirci ne suke yi don su cuce ni;
oSanibhalathi loGeshema bathuma kimi besithi: Woza sihlangane ndawonye emizini emagcekeni eOno. Kodwa babecabange ukwenza okubi kimi.
3 saboda haka sai na aika musu da wannan amsa, na ce, “Ina cikin babban aiki, ba zan kuwa iya gangarawa ba. Don me zan bar aikin yă tsaya don in gangara zuwa wurinku?”
Ngasengithuma izithunywa kubo ngisithi: Ngenza umsebenzi omkhulu, ngakho kangilakho ukwehla. Kungani umsebenzi uzakuma, ngiwutshiye, ngehlele kini?
4 Suka yi ta aiko mini da wannan saƙo har sau huɗu, ni kuwa na yi ta ba su amsa irin ta dā.
Basebethuma kimi kane ngaleyondlela, ngabaphendula ngaleyondlela.
5 Sai sau na biya, Sanballat ya aiki mataimakinsa gare ni da irin saƙo guda, kuma a hannunsa akwai wasiƙar da ba a yimƙe ba
Ngakho uSanibhalathi wathuma kimi inceku yakhe ngaleyondlela ngokwesihlanu ilencwadi evulekileyo esandleni sayo.
6 wadda aka rubuta cewa, “An ba da labari cikin al’ummai, kuma Geshem ya ce gaskiya ne, cewa kai da Yahudawa kun shirya tawaye, saboda haka kuke sāke ginin katangar. Ban da haka ma, bisa ga waɗannan rahotanni kana shirin zaman sarkinsu
Kwakubhalwe kuyo ukuthi: Kuzwakele ezizweni, loGashimu uthi: Wena lamaJuda linakana ukuhlamuka; ngenxa yalokho wakha umduli, ukuze wena ube yinkosi yabo, njengalamazwi.
7 har ma ka naɗa annabawa su yi wannan shela game da kai a Urushalima, su ce, ‘Akwai sarki a Yahuda!’ To, wannan rahoto zai koma wurin sarki; saboda haka ka zo, mu tattauna wannan batu.”
Futhi umisile labaprofethi ukuze bamemezele ngawe eJerusalema, besithi: Kukhona inkosi koJuda. Khathesi-ke kuzazwakala enkosini njengalamazwi. Ngakho-ke woza, sicebisane.
8 Sai na aika masa wannan amsa, na ce, “Babu wani abu haka da yake faruwa; ka dai ƙaga wannan daga tunaninka ne.”
Ngasengithuma kuye ngisithi: Kazikho izinto ezinjengalezo ozitshoyo, kodwa uyazibumba zivela enhliziyweni yakho.
9 Suka dai yi ƙoƙari su tsoratar da mu, suna cewa, “Hannuwansu za su rasa ƙarfin yin aiki, ba kuwa za su ƙare aikin ba.” Amma na yi addu’a na ce, “Yanzu, ya Allah, ka ƙarfafa hannuwana.”
Ngoba bonke basethusa besithi: Izandla zabo zizadangala emsebenzini, ukuthi ungenziwa. Ngakho-ke qinisa izandla zami.
10 Wata rana na tafi gidan Shemahiya ɗan Delahiya, ɗan Mehetabel, wanda aka hana fita a gidansa. Ya ce mini, “Mu sadu gobe a gidan Allah, a cikin haikali, mu kuma kulle ƙofofin haikali, gama mutane suna zuwa su kashe ka, tabbatacce za su zo da dare su kashe ka.”
Mina sengingenile endlini kaShemaya indodana kaDelaya indodana kaMehethabheli owayezivalele, wasesithi: Asihlangane endlini kaNkulunkulu phakathi kwethempeli, sivale iminyango yethempeli, ngoba bayeza ukukubulala, yebo, bayeza ebusuku ukukubulala.
11 Amma na ce, “Ya kamata mutum kamar ni yă gudu? Ko kuwa ya kamata wani kamar ni yă shiga cikin haikali don yă ceci ransa? Ba zan tafi ba!”
Kodwa ngathi: Kambe umuntu onjengami angabaleka? Pho, nguwuphi umuntu onjengami ongangena ethempelini aphile? Kangiyikungena.
12 Na gane cewa Allah bai aike shi ba, ya yi annabci a kaina domin Tobiya da Sanballat sun yi hayarsa ne.
Ngasenginanzelela, khangela-ke, uNkulunkulu wayengamthumanga, kodwa wakhuluma isiprofetho esimelene lami ngoba oTobiya loSanibhalathi babemqhatshile.
13 An yi hayarsa don yă sa in ji tsoro in yi zunubi ta yin haka, sa’an nan za su ba ni mugun suna, su wofinta ni.
Ngakho wayeqhatshiwe ukuze ngesabe, ngenze njalo, ngone, ukuze babe lebizo elibi ngami, ukuze bangigcone.
14 Ya Allahna, ka tuna da Tobiya da Sanballat, saboda abin da suka yi; ka kuma tuna da annabiya Nowadiya da sauran annabawa waɗanda suke ƙoƙari su tsorata ni.
Khumbula, Nkulunkulu wami, uTobiya loSanibhalathi njengokwale imisebenzi yakhe, njalo loNowadiya umprofethikazi labanye abaprofethi ababengethusa.
15 Cikin kwana hamsin da biyu aka gama gina katangar, a ranar ashirin da biyar ga watan Elul.
Waphela-ke umduli ngolwamatshumi amabili lanhlanu kaEluli ngensuku ezingamatshumi amahlanu lambili.
16 Sa’ad da dukan abokan gābanmu suka ji haka, dukan al’umman da suke kewaye da mu suka ji tsoro, suka rasa ƙarfin halinsu, domin sun gane cewa wannan aiki an yi shi da taimakon Allahnmu ne.
Kwasekusithi zonke izitha zethu zisizwa, lazo zonke izizwe ezisizingelezeleyo zibona, zawa kakhulu emehlweni azo; ngoba zananzelela ukuthi lumsebenzi wenziwe nguNkulunkulu wethu.
17 A waɗannan kwanaki, manyan garin Yahuda suka yi ta aika wasiƙu masu yawa zuwa ga Tobiya, shi kuma ya yi ta aika musu da amsoshi.
Njalo ngalezonsuku izikhulu zakoJuda zandisa incwadi zazo eziya kuTobiya, lezikaTobiya zeza kuzo.
18 Gama mutane da yawa a cikin Yahuda sun rantse wa Tobiya za su goyi bayansa, domin ya auri’yar Shekaniya, ɗan Ara. Ɗansa kuma, wato, Yehohanan, ya auri’yar Meshullam, ɗan Berekiya.
Ngoba abanengi koJuda babefungile kuye ngoba wayengumkhwenyana kaShekaniya indodana kaAra, loJehohanani indodana yakhe wayethethe indodakazi kaMeshulamu indodana kaBerekiya.
19 Ban da haka ma, mutanen sun yi ta ba ni labarin ayyuka masu kyau da Tobiya ya yi, sa’an nan kuma suna faɗa masa duk abin da na faɗa. Tobiya kuwa ya aika wasiƙu don yă tsorata ni.
Njalo babekhuluma izenzo zakhe ezinhle phambi kwami, lamazwi ami bewakhuphela kuye. UTobiya wathumela incwadi zokungethusa.