< Nehemiya 6 >

1 Sa’ad da magana ta zo kunnen Sanballat, da Tobiya, da Geshem mutumin Arab da kuma sauran abokan gābanmu cewa na sāke gina katangar har babu sauran tsaguwa da ta ragu, ko da yake har zuwa lokacin ban sa ƙofofi a ƙyamare ba
Or, lorsque Sanaballat, Tobias, l'Arabe Gésam et le reste de nos ennemis, ouïrent que j'avais relevé le mur, ils en perdirent le souffle; cependant, alors, je n'avais pas encore mis les battants des portes.
2 Sanballat da Geshem suka aika mini wannan saƙo cewa, “Ka zo, mu sadu a wani ƙauye a filin Ono.” Amma makirci ne suke yi don su cuce ni;
Et Sanaballat et Gésam m'envoyèrent des messagers, disant: Viens, et rencontrons-nous tous ensemble dans l'un des bourgs de la plaine d'Ono. Mais, ils pensaient à me faire du mal.
3 saboda haka sai na aika musu da wannan amsa, na ce, “Ina cikin babban aiki, ba zan kuwa iya gangarawa ba. Don me zan bar aikin yă tsaya don in gangara zuwa wurinku?”
Je leur envoyai des messagers, disant: Je suis à faire une grande œuvre, et je ne pourrai descendre vers vous, de peur qu'elle ne soit suspendue; je descendrai dès qu'elle sera finie.
4 Suka yi ta aiko mini da wannan saƙo har sau huɗu, ni kuwa na yi ta ba su amsa irin ta dā.
Ils me firent dire derechef ces paroles, et je leur répondis comme la première fois.
5 Sai sau na biya, Sanballat ya aiki mataimakinsa gare ni da irin saƙo guda, kuma a hannunsa akwai wasiƙar da ba a yimƙe ba
Et Sanaballat m'envoya son serviteur, avec une lettre ouverte qu'il tenait à la main.
6 wadda aka rubuta cewa, “An ba da labari cikin al’ummai, kuma Geshem ya ce gaskiya ne, cewa kai da Yahudawa kun shirya tawaye, saboda haka kuke sāke ginin katangar. Ban da haka ma, bisa ga waɗannan rahotanni kana shirin zaman sarkinsu
Et il y était écrit: On a oui dire, parmi les nations, que toi et les Juifs pensez à vous révolter; et que, pour cela, tu édifies le rempart, et que tu seras leur roi.
7 har ma ka naɗa annabawa su yi wannan shela game da kai a Urushalima, su ce, ‘Akwai sarki a Yahuda!’ To, wannan rahoto zai koma wurin sarki; saboda haka ka zo, mu tattauna wannan batu.”
Et, outre cela, tu as aposté pour toi des prophètes, afin que tu sièges à Jérusalem, comme roi de Juda. Or, maintenant, ces choses vont être rapportées au roi; viens donc, et tenons conseil ensemble.
8 Sai na aika masa wannan amsa, na ce, “Babu wani abu haka da yake faruwa; ka dai ƙaga wannan daga tunaninka ne.”
Et je lui envoyai encore des messagers, disant: Cela n'est pas arrivé selon les paroles que tu dis, car tu les as feintes en ton cœur.
9 Suka dai yi ƙoƙari su tsoratar da mu, suna cewa, “Hannuwansu za su rasa ƙarfin yin aiki, ba kuwa za su ƙare aikin ba.” Amma na yi addu’a na ce, “Yanzu, ya Allah, ka ƙarfafa hannuwana.”
Ils voulaient tous ainsi nous effrayer, et ils disaient: Leurs mains en seront énervées; quant à ce travail, il ne sera pas achevé; mais moi, je fortifiai mes mains.
10 Wata rana na tafi gidan Shemahiya ɗan Delahiya, ɗan Mehetabel, wanda aka hana fita a gidansa. Ya ce mini, “Mu sadu gobe a gidan Allah, a cikin haikali, mu kuma kulle ƙofofin haikali, gama mutane suna zuwa su kashe ka, tabbatacce za su zo da dare su kashe ka.”
Et j'entrai en la demeure de Sémei, fils de Daishi, fils de Métabéhel, et il y était enfermé, et il me dit: Réunissons-nous dans le temple de Dieu, et nous en clorons les portes; car cette nuit ils viendront pour te tuer.
11 Amma na ce, “Ya kamata mutum kamar ni yă gudu? Ko kuwa ya kamata wani kamar ni yă shiga cikin haikali don yă ceci ransa? Ba zan tafi ba!”
Et je répondis: Quel est l'homme qui entrera dans le temple, et pourra vivre?
12 Na gane cewa Allah bai aike shi ba, ya yi annabci a kaina domin Tobiya da Sanballat sun yi hayarsa ne.
Et j'observai, et voilà que Dieu ne me l'avait pas envoyé; car sa prophétie était une fable inventée contre moi. En effet, Sanaballat et Tobias avaient salarié
13 An yi hayarsa don yă sa in ji tsoro in yi zunubi ta yin haka, sa’an nan za su ba ni mugun suna, su wofinta ni.
Contre moi une multitude de gens, afin que j'eusse peur, que je fisse ce qu'il conseillait, que je tombasse dans le péché, que j'eusse parmi eux un mauvais renom, et qu'ils m'outrageassent.
14 Ya Allahna, ka tuna da Tobiya da Sanballat, saboda abin da suka yi; ka kuma tuna da annabiya Nowadiya da sauran annabawa waɗanda suke ƙoƙari su tsorata ni.
Souvenez-vous, ô mon Dieu, de Tobias et de Sanaballat, selon leurs actions, et de Noadias le prophète, et des autres prophètes qui tentèrent de m'alarmer.
15 Cikin kwana hamsin da biyu aka gama gina katangar, a ranar ashirin da biyar ga watan Elul.
Et le mur fut achevé en cinquante-deux jours, le vingt-cinq du mois d'étal.
16 Sa’ad da dukan abokan gābanmu suka ji haka, dukan al’umman da suke kewaye da mu suka ji tsoro, suka rasa ƙarfin halinsu, domin sun gane cewa wannan aiki an yi shi da taimakon Allahnmu ne.
Et il advint, quand nos ennemis l'ouïrent, que toutes les nations d'alentour furent épouvantées, et qu'une grande frayeur tomba sur eux, et qu'ils connurent que l'achèvement de cette œuvre était de notre Dieu.
17 A waɗannan kwanaki, manyan garin Yahuda suka yi ta aika wasiƙu masu yawa zuwa ga Tobiya, shi kuma ya yi ta aika musu da amsoshi.
Et, en ces jours-là, des lettres de plusieurs nobles de Juda arrivaient à Tobias, et celles de Tobias leur arrivaient.
18 Gama mutane da yawa a cikin Yahuda sun rantse wa Tobiya za su goyi bayansa, domin ya auri’yar Shekaniya, ɗan Ara. Ɗansa kuma, wato, Yehohanan, ya auri’yar Meshullam, ɗan Berekiya.
Car plusieurs en Juda s'étaient engagés avec lui par serment, parce qu'il était gendre de Sechénias, fils d'Héraé; et que Jonan, son fils, avait épousé la fille de Mesulam, fils de Barachias.
19 Ban da haka ma, mutanen sun yi ta ba ni labarin ayyuka masu kyau da Tobiya ya yi, sa’an nan kuma suna faɗa masa duk abin da na faɗa. Tobiya kuwa ya aika wasiƙu don yă tsorata ni.
Et ils me rapportaient ses paroles, et ils lui répétaient les miennes, et Tobias écrivait des lettres pour m'effrayer.

< Nehemiya 6 >