< Nehemiya 6 >
1 Sa’ad da magana ta zo kunnen Sanballat, da Tobiya, da Geshem mutumin Arab da kuma sauran abokan gābanmu cewa na sāke gina katangar har babu sauran tsaguwa da ta ragu, ko da yake har zuwa lokacin ban sa ƙofofi a ƙyamare ba
Lorsque la nouvelle parvint à Sanballat, à Tobia, à Ghéchem, l’Arabe, et à nos autres ennemis, que j’avais reconstruit la muraille et qu’il n’y restait aucune brèche, (toutefois jusqu’à ce moment je n’avais pas fixé les battants aux portes),
2 Sanballat da Geshem suka aika mini wannan saƙo cewa, “Ka zo, mu sadu a wani ƙauye a filin Ono.” Amma makirci ne suke yi don su cuce ni;
Sanballat et Ghéchem m’envoyèrent dire: "Viens, nous allons conférer ensemble à Kefirim, dans la vallée d’Ono." Ils avaient l’intention de me faire du mal.
3 saboda haka sai na aika musu da wannan amsa, na ce, “Ina cikin babban aiki, ba zan kuwa iya gangarawa ba. Don me zan bar aikin yă tsaya don in gangara zuwa wurinku?”
Mais je leur expédiai des messagers et leur fis dire: "Je suis occupé à un grand ouvrage et ne puis y descendre. Pourquoi laisserai-je s’arrêter le travail en l’abandonnant, pour me rendre auprès de vous?"
4 Suka yi ta aiko mini da wannan saƙo har sau huɗu, ni kuwa na yi ta ba su amsa irin ta dā.
A quatre reprises, ils me firent transmettre la même proposition, et je leur donnai la même réponse.
5 Sai sau na biya, Sanballat ya aiki mataimakinsa gare ni da irin saƙo guda, kuma a hannunsa akwai wasiƙar da ba a yimƙe ba
Sanballat m’adressa la même invitation une cinquième fois par son valet, qui portait en sa main une lettre ouverte,
6 wadda aka rubuta cewa, “An ba da labari cikin al’ummai, kuma Geshem ya ce gaskiya ne, cewa kai da Yahudawa kun shirya tawaye, saboda haka kuke sāke ginin katangar. Ban da haka ma, bisa ga waɗannan rahotanni kana shirin zaman sarkinsu
contenant ces mots: "Le bruit s’est répandu parmi les peuples, et Gachmou le confirme, que toi et les Judéens, vous pensez vous révolter; dans ce but, tu rebâtirais la muraille, et tu songerais à devenir leur roi, d’après ce qui se dit.
7 har ma ka naɗa annabawa su yi wannan shela game da kai a Urushalima, su ce, ‘Akwai sarki a Yahuda!’ To, wannan rahoto zai koma wurin sarki; saboda haka ka zo, mu tattauna wannan batu.”
Tu aurais aussi suscité des prophètes chargés de te proclamer à Jérusalem "roi de Juda". Or, de tels bruits peuvent arriver jusqu’au roi: viens donc et concertons-nous ensemble."
8 Sai na aika masa wannan amsa, na ce, “Babu wani abu haka da yake faruwa; ka dai ƙaga wannan daga tunaninka ne.”
Je renvoyai vers lui pour lui faire dire: "Il n’y a rien de vrai dans tous ces faits que tu allègues, c’est ton imagination qui les a inventés."
9 Suka dai yi ƙoƙari su tsoratar da mu, suna cewa, “Hannuwansu za su rasa ƙarfin yin aiki, ba kuwa za su ƙare aikin ba.” Amma na yi addu’a na ce, “Yanzu, ya Allah, ka ƙarfafa hannuwana.”
Car tous ces gens cherchaient à nous intimider, se disant: "Leurs mains se relâcheront dans le travail, et il ne s’exécutera pas." Or, toi ô Seigneur, soutiens mes bras!
10 Wata rana na tafi gidan Shemahiya ɗan Delahiya, ɗan Mehetabel, wanda aka hana fita a gidansa. Ya ce mini, “Mu sadu gobe a gidan Allah, a cikin haikali, mu kuma kulle ƙofofin haikali, gama mutane suna zuwa su kashe ka, tabbatacce za su zo da dare su kashe ka.”
Je me rendis dans la maison de Chemaïa, fils de Delaïa, fils de Mehétabel, qui était enfermé chez lui. Il me dit: "Allons de concert dans la maison de Dieu, au fond du sanctuaire, et fermons les portes du sanctuaire, car ils vont venir te tuer; c’est dans la nuit qu’on viendra te mettre à mort."
11 Amma na ce, “Ya kamata mutum kamar ni yă gudu? Ko kuwa ya kamata wani kamar ni yă shiga cikin haikali don yă ceci ransa? Ba zan tafi ba!”
Je répondis: "Est-ce qu’un homme comme moi doit s’enfuir? Et quel est mon pareil qui oserait entrer dans le sanctuaire et qui resterait en vie? Je n’irai point."
12 Na gane cewa Allah bai aike shi ba, ya yi annabci a kaina domin Tobiya da Sanballat sun yi hayarsa ne.
Je reconnus par là que ce n’était pas Dieu qui l’avait envoyé, mais qu’il avait prononcé une prophétie à mon sujet, Tobia et Sanballat l’ayant soudoyé.
13 An yi hayarsa don yă sa in ji tsoro in yi zunubi ta yin haka, sa’an nan za su ba ni mugun suna, su wofinta ni.
En effet, il avait été soudoyé pour que, prenant peur, j’agisse selon son conseil et me rendisse coupable; cela leur aurait servi à me faire une mauvaise réputation et à me couvrir d’opprobre.
14 Ya Allahna, ka tuna da Tobiya da Sanballat, saboda abin da suka yi; ka kuma tuna da annabiya Nowadiya da sauran annabawa waɗanda suke ƙoƙari su tsorata ni.
Tiens compte, ô mon Dieu, à Tobia et à Sanballat de tels agissements; tiens compte aussi à la prophétesse Noadia et aux autres prophètes de ce qu’ils cherchaient à m’intimider.
15 Cikin kwana hamsin da biyu aka gama gina katangar, a ranar ashirin da biyar ga watan Elul.
La muraille fut achevée le vingt-cinquième jour du mois d’Eloul, au bout de cinquante-deux jours.
16 Sa’ad da dukan abokan gābanmu suka ji haka, dukan al’umman da suke kewaye da mu suka ji tsoro, suka rasa ƙarfin halinsu, domin sun gane cewa wannan aiki an yi shi da taimakon Allahnmu ne.
Lorsque nos ennemis en furent tous instruits, toutes les nations qui nous entouraient prirent peur et se sentirent bien diminuées à leurs propres yeux; elles reconnurent que c’était grâce à notre Dieu que cette entreprise avait été menée à bonne fin.
17 A waɗannan kwanaki, manyan garin Yahuda suka yi ta aika wasiƙu masu yawa zuwa ga Tobiya, shi kuma ya yi ta aika musu da amsoshi.
En ce même temps, les nobles de Juda multipliaient leurs lettres à l’adresse de Tobia, et celui-ci leur en faisait parvenir de son côté.
18 Gama mutane da yawa a cikin Yahuda sun rantse wa Tobiya za su goyi bayansa, domin ya auri’yar Shekaniya, ɗan Ara. Ɗansa kuma, wato, Yehohanan, ya auri’yar Meshullam, ɗan Berekiya.
Beaucoup de gens de Juda, en effet, lui étaient affiliés par un pacte, car il était le gendre de Chekhania, fils d’Arah, et son fils Johanan avait épousé la fille de Mechoullam, fils de Bérékhia.
19 Ban da haka ma, mutanen sun yi ta ba ni labarin ayyuka masu kyau da Tobiya ya yi, sa’an nan kuma suna faɗa masa duk abin da na faɗa. Tobiya kuwa ya aika wasiƙu don yă tsorata ni.
Ils vantaient aussi ses mérites devant moi et lui rapportaient mes paroles; Tobia, lui, envoyait des lettres pour m’intimider.