< Nehemiya 6 >

1 Sa’ad da magana ta zo kunnen Sanballat, da Tobiya, da Geshem mutumin Arab da kuma sauran abokan gābanmu cewa na sāke gina katangar har babu sauran tsaguwa da ta ragu, ko da yake har zuwa lokacin ban sa ƙofofi a ƙyamare ba
Lorsqu’il fut connu de Sanaballat, de Tobie, de Gosem l’Arabe et du reste de nos ennemis que j’avais rebâti la muraille et qu’il n’y restait plus de brèche — jusqu’à cette date toutefois je n’avais pas mis les battants aux portes, —
2 Sanballat da Geshem suka aika mini wannan saƙo cewa, “Ka zo, mu sadu a wani ƙauye a filin Ono.” Amma makirci ne suke yi don su cuce ni;
Sanaballat et Gosem m’envoyèrent dire: « Viens, et ayons ensemble une entrevue dans les villages, dans la vallée d’Ono. » Ils avaient le dessein de me faire du mal.
3 saboda haka sai na aika musu da wannan amsa, na ce, “Ina cikin babban aiki, ba zan kuwa iya gangarawa ba. Don me zan bar aikin yă tsaya don in gangara zuwa wurinku?”
Je leur envoyai des messagers pour leur dire: « J’exécute un grand travail, et je ne puis descendre. Pourquoi le travail serait-il interrompu, parce que je le quitterais pour descendre vers vous? »
4 Suka yi ta aiko mini da wannan saƙo har sau huɗu, ni kuwa na yi ta ba su amsa irin ta dā.
Ils m’adressèrent quatre fois la même proposition, et je leur fis la même réponse.
5 Sai sau na biya, Sanballat ya aiki mataimakinsa gare ni da irin saƙo guda, kuma a hannunsa akwai wasiƙar da ba a yimƙe ba
Sanaballat m’envoya de la même manière une cinquième fois son serviteur, qui tenait à la main une lettre ouverte.
6 wadda aka rubuta cewa, “An ba da labari cikin al’ummai, kuma Geshem ya ce gaskiya ne, cewa kai da Yahudawa kun shirya tawaye, saboda haka kuke sāke ginin katangar. Ban da haka ma, bisa ga waɗannan rahotanni kana shirin zaman sarkinsu
Il y était écrit: « Le bruit se répand parmi les nations et Gosem affirme que toi et les Juifs, vous avez dessein de vous révolter, et que c’est pour cela que tu rebâtis la muraille; et, d’après ces rapports, tu veux devenir leur roi.
7 har ma ka naɗa annabawa su yi wannan shela game da kai a Urushalima, su ce, ‘Akwai sarki a Yahuda!’ To, wannan rahoto zai koma wurin sarki; saboda haka ka zo, mu tattauna wannan batu.”
Et même tu as établis des prophètes pour faire à ton propos cette proclamation dans Jérusalem: Il y a un roi en Juda. Maintenant, on va informer le roi de cette affaire. Viens donc, et consultons-nous ensemble. »
8 Sai na aika masa wannan amsa, na ce, “Babu wani abu haka da yake faruwa; ka dai ƙaga wannan daga tunaninka ne.”
Et je lui envoyai dire: « Rien n’est arrivé de pareil à ces choses que tu dis; c’est de ton cœur que tu les inventes. »
9 Suka dai yi ƙoƙari su tsoratar da mu, suna cewa, “Hannuwansu za su rasa ƙarfin yin aiki, ba kuwa za su ƙare aikin ba.” Amma na yi addu’a na ce, “Yanzu, ya Allah, ka ƙarfafa hannuwana.”
Car tous voulaient nous effrayer, se disant: « Leurs mains affaiblies se détacheront de l’œuvre, et elle ne s’accomplira pas. » Maintenant, ô mon Dieu, donne force à mes mains!
10 Wata rana na tafi gidan Shemahiya ɗan Delahiya, ɗan Mehetabel, wanda aka hana fita a gidansa. Ya ce mini, “Mu sadu gobe a gidan Allah, a cikin haikali, mu kuma kulle ƙofofin haikali, gama mutane suna zuwa su kashe ka, tabbatacce za su zo da dare su kashe ka.”
Je me rendis chez Sémaïas, fils de Dalaïas, fils de Métabéel. Il s’était enfermé, et il dit: « Allons ensemble dans la maison de Dieu, dans l’intérieur du temple et fermons les portes du temple; car on vient pour te tuer; c’est pendant la nuit qu’on viendra pour te tuer. »
11 Amma na ce, “Ya kamata mutum kamar ni yă gudu? Ko kuwa ya kamata wani kamar ni yă shiga cikin haikali don yă ceci ransa? Ba zan tafi ba!”
Je répondis: « Un homme comme moi prendre la fuite...! Et comment un homme comme moi pénétrerait-il dans le temple et demeurerait-il en vie? Je n’entrerai point. »
12 Na gane cewa Allah bai aike shi ba, ya yi annabci a kaina domin Tobiya da Sanballat sun yi hayarsa ne.
Et je fis attention, et voici que ce n’était pas Dieu qui l’envoyait; il avait prononcé sur moi une prophétie parce que Tobie et Sanaballat l’avaient acheté.
13 An yi hayarsa don yă sa in ji tsoro in yi zunubi ta yin haka, sa’an nan za su ba ni mugun suna, su wofinta ni.
On l’avait acheté pour que j’aie peur, que j’agisse selon ses avis et que je pèche; et cela leur eut été un prétexte pour me faire un mauvais renom et me couvrir d’opprobre.
14 Ya Allahna, ka tuna da Tobiya da Sanballat, saboda abin da suka yi; ka kuma tuna da annabiya Nowadiya da sauran annabawa waɗanda suke ƙoƙari su tsorata ni.
Souvenez-vous, ô mon Dieu, de Tobie et de Sanaballat selon ces méfaits! Et aussi de Noadias le prophète, et des autres prophètes qui cherchaient à m’effrayer.
15 Cikin kwana hamsin da biyu aka gama gina katangar, a ranar ashirin da biyar ga watan Elul.
La muraille fut achevée le vingt-cinquième jour du mois d’Elul, en cinquante-deux jours.
16 Sa’ad da dukan abokan gābanmu suka ji haka, dukan al’umman da suke kewaye da mu suka ji tsoro, suka rasa ƙarfin halinsu, domin sun gane cewa wannan aiki an yi shi da taimakon Allahnmu ne.
Lorsque tous nos ennemis l’apprirent, toutes les nations qui étaient autour de nous furent dans la crainte; elles éprouvèrent un grand découragement et reconnurent que c’était par le secours de notre Dieu que cette œuvre s’était accomplie.
17 A waɗannan kwanaki, manyan garin Yahuda suka yi ta aika wasiƙu masu yawa zuwa ga Tobiya, shi kuma ya yi ta aika musu da amsoshi.
Dans ce temps-là aussi, des grands de Juda multipliaient leurs lettres à l’adresse de Tobie, et celles de Tobie leur parvenaient.
18 Gama mutane da yawa a cikin Yahuda sun rantse wa Tobiya za su goyi bayansa, domin ya auri’yar Shekaniya, ɗan Ara. Ɗansa kuma, wato, Yehohanan, ya auri’yar Meshullam, ɗan Berekiya.
Car beaucoup de grands en Juda lui étaient liés par serment, parce qu’il était gendre de Séchénias, fils d’Aréa, et que son fils Johanan avait pris pour femme la fille de Mosollam, fils de Barachie.
19 Ban da haka ma, mutanen sun yi ta ba ni labarin ayyuka masu kyau da Tobiya ya yi, sa’an nan kuma suna faɗa masa duk abin da na faɗa. Tobiya kuwa ya aika wasiƙu don yă tsorata ni.
Ils disaient même ses bonnes qualités devant moi, et ils lui rapportaient mes paroles. Tobie envoyait des lettres pour m’effrayer.

< Nehemiya 6 >