< Nehemiya 6 >
1 Sa’ad da magana ta zo kunnen Sanballat, da Tobiya, da Geshem mutumin Arab da kuma sauran abokan gābanmu cewa na sāke gina katangar har babu sauran tsaguwa da ta ragu, ko da yake har zuwa lokacin ban sa ƙofofi a ƙyamare ba
Now when Sanballat, Tobiah, and Geshem the Arabian and the rest of our enemies heard that I had rebuilt the wall and that there were no longer any sections left broken open, although I had not yet set up the doors in the gates,
2 Sanballat da Geshem suka aika mini wannan saƙo cewa, “Ka zo, mu sadu a wani ƙauye a filin Ono.” Amma makirci ne suke yi don su cuce ni;
Sanballat and Geshem sent to me saying, “Come, let us meet together somewhere in the plain of Ono.” But they intended to do harm to me.
3 saboda haka sai na aika musu da wannan amsa, na ce, “Ina cikin babban aiki, ba zan kuwa iya gangarawa ba. Don me zan bar aikin yă tsaya don in gangara zuwa wurinku?”
I sent messengers to them, saying, “I am doing a great work, and I cannot come down. Why should the work stop while I leave it and come down to you?”
4 Suka yi ta aiko mini da wannan saƙo har sau huɗu, ni kuwa na yi ta ba su amsa irin ta dā.
They sent me the same message four times, and I answered them the same way each time.
5 Sai sau na biya, Sanballat ya aiki mataimakinsa gare ni da irin saƙo guda, kuma a hannunsa akwai wasiƙar da ba a yimƙe ba
Sanballat sent his servant to me in the same way the fifth time, with an open letter in his hand.
6 wadda aka rubuta cewa, “An ba da labari cikin al’ummai, kuma Geshem ya ce gaskiya ne, cewa kai da Yahudawa kun shirya tawaye, saboda haka kuke sāke ginin katangar. Ban da haka ma, bisa ga waɗannan rahotanni kana shirin zaman sarkinsu
In it was written, “It is reported among the nations, and Geshem also says it, that you and the Jews are planning to rebel, for that is why you are rebuilding the wall. From what these reports say, you are about to become their king.
7 har ma ka naɗa annabawa su yi wannan shela game da kai a Urushalima, su ce, ‘Akwai sarki a Yahuda!’ To, wannan rahoto zai koma wurin sarki; saboda haka ka zo, mu tattauna wannan batu.”
You have also appointed prophets to make this proclamation about you in Jerusalem, saying, 'There is a king in Judah!' You can be sure the king will hear these reports. Therefore come, let us speak with one another.”
8 Sai na aika masa wannan amsa, na ce, “Babu wani abu haka da yake faruwa; ka dai ƙaga wannan daga tunaninka ne.”
Then I sent word to him saying, “No such things have occurred as you say, for within your heart you invented them.”
9 Suka dai yi ƙoƙari su tsoratar da mu, suna cewa, “Hannuwansu za su rasa ƙarfin yin aiki, ba kuwa za su ƙare aikin ba.” Amma na yi addu’a na ce, “Yanzu, ya Allah, ka ƙarfafa hannuwana.”
For they all wanted to make us afraid, thinking, “They will drop their hands from doing the work, and it will not be done.” But now, God, please strengthen my hands.
10 Wata rana na tafi gidan Shemahiya ɗan Delahiya, ɗan Mehetabel, wanda aka hana fita a gidansa. Ya ce mini, “Mu sadu gobe a gidan Allah, a cikin haikali, mu kuma kulle ƙofofin haikali, gama mutane suna zuwa su kashe ka, tabbatacce za su zo da dare su kashe ka.”
I went to the house of Shemaiah son of Delaiah son of Mehetabel, who was confined in his home. He said, “Let us meet together in the house of God, inside the temple, and let us close the doors of the temple, for they are coming to kill you. At night they are coming to kill you.”
11 Amma na ce, “Ya kamata mutum kamar ni yă gudu? Ko kuwa ya kamata wani kamar ni yă shiga cikin haikali don yă ceci ransa? Ba zan tafi ba!”
I replied, “Would a man like me run away? Would a man like me go into the temple just so he could save his own life? I will not go in!”
12 Na gane cewa Allah bai aike shi ba, ya yi annabci a kaina domin Tobiya da Sanballat sun yi hayarsa ne.
I realized that it was not God who sent him, but that he had prophesied against me. Tobiah and Sanballat had hired him.
13 An yi hayarsa don yă sa in ji tsoro in yi zunubi ta yin haka, sa’an nan za su ba ni mugun suna, su wofinta ni.
They hired him to make me afraid, so that I might do what he said and sin, so they could give me a bad name in order to humiliate me.
14 Ya Allahna, ka tuna da Tobiya da Sanballat, saboda abin da suka yi; ka kuma tuna da annabiya Nowadiya da sauran annabawa waɗanda suke ƙoƙari su tsorata ni.
Call to mind Tobiah and Sanballat, my God, and all that they did. Also call to mind the prophetess Noadiah and the rest of the prophets who tried to make me be afraid.
15 Cikin kwana hamsin da biyu aka gama gina katangar, a ranar ashirin da biyar ga watan Elul.
So the wall was finished on the twenty-fifth day of the month of Elul, after fifty-two days.
16 Sa’ad da dukan abokan gābanmu suka ji haka, dukan al’umman da suke kewaye da mu suka ji tsoro, suka rasa ƙarfin halinsu, domin sun gane cewa wannan aiki an yi shi da taimakon Allahnmu ne.
When all our enemies heard of it, all the nations around us, they became afraid and they fell greatly in their own eyes. For they knew the work was done with the help of our God.
17 A waɗannan kwanaki, manyan garin Yahuda suka yi ta aika wasiƙu masu yawa zuwa ga Tobiya, shi kuma ya yi ta aika musu da amsoshi.
At this time the nobles of Judah sent many letters to Tobiah, and Tobiah's letters came to them.
18 Gama mutane da yawa a cikin Yahuda sun rantse wa Tobiya za su goyi bayansa, domin ya auri’yar Shekaniya, ɗan Ara. Ɗansa kuma, wato, Yehohanan, ya auri’yar Meshullam, ɗan Berekiya.
For there were many in Judah who were bound by an oath to him, because he was the son-in-law of Shecaniah son of Arah. His son Jehohanan had taken as his wife the daughter of Meshullam son of Berechiah.
19 Ban da haka ma, mutanen sun yi ta ba ni labarin ayyuka masu kyau da Tobiya ya yi, sa’an nan kuma suna faɗa masa duk abin da na faɗa. Tobiya kuwa ya aika wasiƙu don yă tsorata ni.
They also spoke to me about his good deeds and reported my words back to him. Letters were sent to me from Tobiah to frighten me.