< Nehemiya 5 >

1 To, sai maza da matansu suka tā da fara gunaguni mai tsanani a kan’yan’uwansu Yahudawa.
Entonces hubo un gran clamor del pueblo y sus esposas contra sus compatriotas, los judíos.
2 Waɗansu suka ce, “Mu da’ya’yanmu maza da mata muna da yawa, muna bukatar hatsi domin mu ci mu rayu.”
Porque hubo algunos que dijeron: Nosotros, nuestros hijos y nuestras hijas, somos un gran número; obtengamos grano, para que podamos tener alimento para nuestras necesidades.
3 Waɗansu kuwa suka ce, “Saboda yunwa mun jinginar da gonakinmu, da gonakin inabinmu, da gidajenmu don mu sami hatsi.”
Y hubo algunos que dijeron: Estamos dando nuestros campos y nuestros viñedos y nuestras casas a cambio; obtengamos grano porque estamos en necesidad.
4 Har illa yau waɗansu suka ce, “Mun ci bashin kuɗi don mu biya haraji a kan gonakinmu, da gonakin inabinmu.
Y hubo otros que dijeron: Hemos dado en garantía nuestros campos y nuestros viñedos para obtener dinero para los impuestos del rey.
5 Ga shi kuwa, mu da su dangin juna ne,’ya’yanmu da nasu kuma ɗaya ne, duk da haka an tilasta mu mu sa’ya’yanmu mata da maza su zama bayi. Har ma an riga an bautar waɗansu daga cikin’ya’yanmu mata, amma ba mu da iko mu ce kome, domin gonakinmu da gonakin inabinmu suna a hannun waɗansu mutane.”
Pero nuestra carne es igual a la carne de nuestros compatriotas, y nuestros hijos como sus hijos, y ahora estamos entregando a nuestros hijos e hijas en manos de otros, para que sean sus sirvientes, y algunas de nuestras hijas son sirvientas incluso ahora, y no tenemos poder para detenerlo; Porque otros hombres tienen nuestros campos y nuestros viñedos.
6 Sa’ad da na ji kukansu da waɗannan koke-koke, na husata ƙwarai.
Y al escuchar su clamor y lo que dijeron, estaba muy enojado.
7 Na yi tunaninsu a zuciyata sa’an nan na zargi manyan gari da shugabanni. Na ce musu, “Kuna musguna wa’yan’uwanku ta wurin ba su rance da ruwa!” Saboda haka na kira babban taro gaba ɗaya don a magance wannan.
Y después de pensarlo, hice una protesta a los jefes y los gobernantes, por imponer una carga tal a sus compatriotas. Y convoque una gran reunión para tratar el caso.
8 Na ce, “Da dukan iyakar ƙoƙarinmu, mun fanshi’yan’uwanmu Yahudawan da aka sayar wa Al’ummai. Amma ga shi kuna sayar da’yan’uwanku ga Al’ummai, don kawai a sāke sayar mana da su!”
Y les dije: Hemos dado todo lo que pudimos dar, para hacer libres a nuestros hermanos judíos, que eran siervos y prisioneros de las naciones; y ahora, ¿renunciarían a sus hermanos para venderlos otra vez, y ¿Se convertirán en nuestra propiedad? Entonces no dijeron nada, respondiendo ni una palabra.
9 Saboda haka na ci gaba na ce, “Abin da kuke yi a yanzu ba daidai ba ne. Bai kamata ku yi tafiya cikin tsoron Allahnmu don mu guji ba’ar Al’ummai abokan gābanmu ba?
Y dije: Lo que están haciendo no está bien; ¿no es más necesario que vayas con el temor de nuestro Dios, por la vergüenza de las naciones enemigas nuestras?
10 Ni ma da’yan’uwana da kuma mutanena muna ba wa mutane bashin kuɗi da kuma hatsi. Sai mu daina sha’anin ba da rance da ruwa!
Incluso yo y mis sirvientes hemos estado tomando interés por el dinero y el grano que les hemos dejado tener. Así que ahora, dejemos está usura.
11 Yau sai ku mayar musu da gonakinsu, da gonakin inabinsu, da na zaitunsu, da gidajensu, da kashi ɗaya bisa ɗari na kuɗi, da na hatsi, da na ruwan inabi, da na mai, waɗanda kuka karɓa a wurinsu.”
Devuélvanles hoy mismo sus campos, sus viñedos, sus olivares y sus casas, y la centésima parte, del grano y el vino y el aceite que demandan de ellos.
12 Suka ce, “Za mu mayar musu, kuma ba za mu bukaci wani abu daga gare su ba. Za mu yi yadda ka faɗa.” Sai na tattara firistoci na kuma sa manyan gari da shugabanni su yi rantsuwa don su yi abin da suka yi alkawari.
Entonces ellos dijeron: Les devolveremos, y no tomaremos nada de ellos; Haremos lo que tu digas. Luego envié a los sacerdotes y les hice jurar que mantendrían este acuerdo.
13 Na kuma kakkaɓe hannuna, na ce, “Duk wanda ya karya wannan alkawari, haka Allah zai kakkaɓe shi daga gidansa da aikinsa. Allah zai kakkaɓe shi, yă wofintar da shi!” Da jin wannan, sai dukan taron suka ce, “Amin,” suka kuma yabi Ubangiji. Mutane kuwa suka yi kamar yadda suka yi alkawari.
Y sacudiendo los pliegues de mi túnica, dije: Que Dios envíe de su casa y de su trabajo a todo hombre que no cumpla con este acuerdo; así sea sacudido y despojado. Y toda la reunión de la gente dijo: “Así sea, y alabó al Señor”. Y la gente hizo lo que había dicho.
14 Ban da haka ma, daga shekara ta ashirin ta Sarki Artazerzes, sa’ad da aka naɗa ni in zama gwamnansu a ƙasar Yahuda, har zuwa shekara ta talatin da biyu na mulkinsa, shekara sha biyu ke nan, ko ni, ko’yan’uwana, ba wanda ya ci abincin da akan ba wa gwamna.
Desde el momento en que fui hecho gobernante del pueblo en la tierra de Judá, desde el año veinte hasta el año treinta y dos del rey Artajerjes, durante doce años, yo y mis siervos nunca hemos tomado la comida. Que era el derecho del gobernante.
15 Amma gwamnonin farko, waɗanda suka riga ni, sun ɗaura wa mutane kaya mai nauyi suka karɓi shekel arba’in na azurfa daga gare su haɗe da abinci da kuma ruwan inabi. Har bayin masu mulki ma sun nawaya wa mutane. Amma ni ban yi haka ba, saboda ina tsoron Allah.
Pero los gobernantes anteriores que estaban antes de mí hicieron a las personas responsables de su mantenimiento, y tomaron de ellos pan y vino al ritmo de cuarenta siclos de plata; e incluso sus siervos eran señores de la gente: pero no lo hice por el temor de Dios.
16 A maimakon haka, na miƙa kaina ga aiki a kan wannan katanga. Na tattara dukan mutanena a can don aikin; ba mu samar wa kanmu wata gona ba.
Y continué con el trabajo de este muro, y no adquirimos tierra para nosotros mismos, y todos mis sirvientes ayudaron con el trabajo.
17 Bugu da ƙari, Yahudawa da shugabanni ɗari da hamsin suna ci daga teburina, haka ma waɗanda suka zo wurinmu daga ƙasashen da suke kewaye.
Y más que esto, ciento cincuenta judíos y gobernantes fueron invitados a mi mesa, además de los que vinieron a nosotros desde las naciones que nos rodeaban.
18 Kowace rana akan shirya mini saniya ɗaya, zaɓaɓɓun tumaki shida da waɗansu kaji, kuma kowace kwana goma akan tanadar da ruwan inabi na kowane iri a yalwace. Duk da haka, ban taɓa nemi a ba ni abincin da akan ba wa gwamna ba, domin wahala ta yi wa jama’a yawa.
La comida preparada para un día era un buey y seis ovejas gordas, así como aves de corral; y una vez en diez días una bodega de todo tipo de vino; pero, de todos modos, no reclame la pensión a la que tenía derecho el gobernante, porque la carga ya era excesiva sobre la gente.
19 Ka tuna da ni, ka yi mini alheri, ya Allah, saboda dukan abubuwan da na yi saboda waɗannan mutane.
Ten en mente, oh Dios mío, por mi bien, todo lo que he hecho por este pueblo.

< Nehemiya 5 >