< Nehemiya 5 >

1 To, sai maza da matansu suka tā da fara gunaguni mai tsanani a kan’yan’uwansu Yahudawa.
I stade velika vika ljudi i žena na braæu njihovu Judejce.
2 Waɗansu suka ce, “Mu da’ya’yanmu maza da mata muna da yawa, muna bukatar hatsi domin mu ci mu rayu.”
Jer neki govorahu: nas i sinova naših i kæeri naših ima mnogo; da dobavimo žita da jedemo i ostanemo živi.
3 Waɗansu kuwa suka ce, “Saboda yunwa mun jinginar da gonakinmu, da gonakin inabinmu, da gidajenmu don mu sami hatsi.”
Drugi opet govorahu: da založimo polja svoja i vinograde i kuæe da dobijemo žita u ovoj gladi.
4 Har illa yau waɗansu suka ce, “Mun ci bashin kuɗi don mu biya haraji a kan gonakinmu, da gonakin inabinmu.
Još drugi govorahu: da uzajmimo novaca na polja svoja i vinograde za danak carski.
5 Ga shi kuwa, mu da su dangin juna ne,’ya’yanmu da nasu kuma ɗaya ne, duk da haka an tilasta mu mu sa’ya’yanmu mata da maza su zama bayi. Har ma an riga an bautar waɗansu daga cikin’ya’yanmu mata, amma ba mu da iko mu ce kome, domin gonakinmu da gonakin inabinmu suna a hannun waɗansu mutane.”
A tijelo je naše kao tijelo braæe naše, sinovi naši kao njihovi sinovi, i eto treba da damo sinove svoje i kæeri svoje u roblje, i neke kæeri naše veæ su robinje, a mi ne možemo ništa, jer polja naša i vinograde naše drže drugi.
6 Sa’ad da na ji kukansu da waɗannan koke-koke, na husata ƙwarai.
Zato se rasrdih vrlo kad èuh viku njihovu i te rijeèi.
7 Na yi tunaninsu a zuciyata sa’an nan na zargi manyan gari da shugabanni. Na ce musu, “Kuna musguna wa’yan’uwanku ta wurin ba su rance da ruwa!” Saboda haka na kira babban taro gaba ɗaya don a magance wannan.
I smislih u srcu svom i ukorih knezove i poglavare, i rekoh im: vi meæete bremena svaki na brata svojega. I sazvah veliki zbor njih radi.
8 Na ce, “Da dukan iyakar ƙoƙarinmu, mun fanshi’yan’uwanmu Yahudawan da aka sayar wa Al’ummai. Amma ga shi kuna sayar da’yan’uwanku ga Al’ummai, don kawai a sāke sayar mana da su!”
I rekoh im: mi otkupismo koliko mogosmo braæu svoju Judejce što bjehu prodani narodima; a vi li æete prodavati braæu svoju ili æe se prodavati nama? A oni umukoše i ne naðoše što bi odgovorili.
9 Saboda haka na ci gaba na ce, “Abin da kuke yi a yanzu ba daidai ba ne. Bai kamata ku yi tafiya cikin tsoron Allahnmu don mu guji ba’ar Al’ummai abokan gābanmu ba?
I rekoh: nije dobro što radite. Ne treba li vam hoditi u strahu Boga našega da nam se ne rugaju narodi, neprijatelji naši?
10 Ni ma da’yan’uwana da kuma mutanena muna ba wa mutane bashin kuɗi da kuma hatsi. Sai mu daina sha’anin ba da rance da ruwa!
I ja i braæa moja i momci moji davali smo im novaca i žita; ali oprostimo im taj dug.
11 Yau sai ku mayar musu da gonakinsu, da gonakin inabinsu, da na zaitunsu, da gidajensu, da kashi ɗaya bisa ɗari na kuɗi, da na hatsi, da na ruwan inabi, da na mai, waɗanda kuka karɓa a wurinsu.”
Hajde vratite im danas polja njihova i vinograde i maslinike i kuæe i što im na stotinu uzimate od novca i žita i vina i ulja.
12 Suka ce, “Za mu mayar musu, kuma ba za mu bukaci wani abu daga gare su ba. Za mu yi yadda ka faɗa.” Sai na tattara firistoci na kuma sa manyan gari da shugabanni su yi rantsuwa don su yi abin da suka yi alkawari.
A oni odgovoriše: vratiæemo i neæemo iskati od njih; uèiniæemo kako veliš. Tada sazvah sveštenike, i zakleh ih da æe tako uèiniti.
13 Na kuma kakkaɓe hannuna, na ce, “Duk wanda ya karya wannan alkawari, haka Allah zai kakkaɓe shi daga gidansa da aikinsa. Allah zai kakkaɓe shi, yă wofintar da shi!” Da jin wannan, sai dukan taron suka ce, “Amin,” suka kuma yabi Ubangiji. Mutane kuwa suka yi kamar yadda suka yi alkawari.
I istresoh njedra svoja i rekoh: ovako da istrese Bog svakoga iz kuæe njegove i iz truda njegova ko god ne ispuni ove rijeèi, i ovako da se istrese i bude prazan. I sav zbor reèe: amin. I hvališe Gospoda, i uèini narod po toj rijeèi.
14 Ban da haka ma, daga shekara ta ashirin ta Sarki Artazerzes, sa’ad da aka naɗa ni in zama gwamnansu a ƙasar Yahuda, har zuwa shekara ta talatin da biyu na mulkinsa, shekara sha biyu ke nan, ko ni, ko’yan’uwana, ba wanda ya ci abincin da akan ba wa gwamna.
I otkad mi car zapovjedi da im budem upravitelj u zemlji Judinoj, od godine dvadesete do trideset druge godine cara Artakserksa, dvanaest godina, ja i braæa moja ne jedosmo hrane upraviteljske.
15 Amma gwamnonin farko, waɗanda suka riga ni, sun ɗaura wa mutane kaya mai nauyi suka karɓi shekel arba’in na azurfa daga gare su haɗe da abinci da kuma ruwan inabi. Har bayin masu mulki ma sun nawaya wa mutane. Amma ni ban yi haka ba, saboda ina tsoron Allah.
A preðašnji upravitelji koji bijahu prije mene bijahu teški narodu uzimajuæi od njega hljeba i vina osim èetrdeset sikala srebra, i sluge njihove zapovijedahu po narodu; ali ja tako ne èinih bojeæi se Boga.
16 A maimakon haka, na miƙa kaina ga aiki a kan wannan katanga. Na tattara dukan mutanena a can don aikin; ba mu samar wa kanmu wata gona ba.
Nego i oko graðenja zida radih, i ne kupismo njive; i svi momci moji bijahu skupa ondje na poslu.
17 Bugu da ƙari, Yahudawa da shugabanni ɗari da hamsin suna ci daga teburina, haka ma waɗanda suka zo wurinmu daga ƙasashen da suke kewaye.
I Judejaca i poglavara sto i pedeset ljudi i koji dolažahu k nama iz okolnijeh naroda bijahu za mojim stolom.
18 Kowace rana akan shirya mini saniya ɗaya, zaɓaɓɓun tumaki shida da waɗansu kaji, kuma kowace kwana goma akan tanadar da ruwan inabi na kowane iri a yalwace. Duk da haka, ban taɓa nemi a ba ni abincin da akan ba wa gwamna ba, domin wahala ta yi wa jama’a yawa.
I gotovljaše se svaki dan po jedno goveèe, šest ovaca izabranijeh, i ptice gotovljahu mi se, i svakih deset dana davaše se svakojakoga vina izobila. I opet ne iskah hrane upraviteljske; jer služba bješe teška narodu.
19 Ka tuna da ni, ka yi mini alheri, ya Allah, saboda dukan abubuwan da na yi saboda waɗannan mutane.
Pomeni me, Bože moj, na dobro za sve što sam èinio ovomu narodu.

< Nehemiya 5 >