< Nehemiya 5 >
1 To, sai maza da matansu suka tā da fara gunaguni mai tsanani a kan’yan’uwansu Yahudawa.
De violentes plaintes éclatèrent parmi les gens du peuple et leurs femmes contre leurs frères, les Judéens.
2 Waɗansu suka ce, “Mu da’ya’yanmu maza da mata muna da yawa, muna bukatar hatsi domin mu ci mu rayu.”
Il y en avait qui disaient: "Nous avons nos fils et nos filles, des familles nombreuses, et nous voudrions obtenir du blé pour manger et sustenter notre vie."
3 Waɗansu kuwa suka ce, “Saboda yunwa mun jinginar da gonakinmu, da gonakin inabinmu, da gidajenmu don mu sami hatsi.”
D’Autres disaient: "Nous sommes réduits à donner en gage nos champs, nos vignes et nos maisons pour nous procurer du blé dans la disette."
4 Har illa yau waɗansu suka ce, “Mun ci bashin kuɗi don mu biya haraji a kan gonakinmu, da gonakin inabinmu.
D’Autres encore disaient: "Nous avons dû, pour acquitter l’impôt du roi, emprunter de l’argent sur nos champs et nos vignes.
5 Ga shi kuwa, mu da su dangin juna ne,’ya’yanmu da nasu kuma ɗaya ne, duk da haka an tilasta mu mu sa’ya’yanmu mata da maza su zama bayi. Har ma an riga an bautar waɗansu daga cikin’ya’yanmu mata, amma ba mu da iko mu ce kome, domin gonakinmu da gonakin inabinmu suna a hannun waɗansu mutane.”
Eh bien! Notre chair est comme la chair de nos frères, nos enfants sont comme leurs enfants, et pourtant nous astreignons nos fils et nos filles à être esclaves. Déjà il en est parmi nos filles qui sont asservies, et nous n’y pouvons rien, nos champs et nos vignes appartenant à d’autres."
6 Sa’ad da na ji kukansu da waɗannan koke-koke, na husata ƙwarai.
Je fus profondément affligé, quand j’entendis leurs plaintes et ces réclamations.
7 Na yi tunaninsu a zuciyata sa’an nan na zargi manyan gari da shugabanni. Na ce musu, “Kuna musguna wa’yan’uwanku ta wurin ba su rance da ruwa!” Saboda haka na kira babban taro gaba ɗaya don a magance wannan.
Je pris résolument mon parti et j’adressai des reproches aux nobles et aux chefs en leur disant: "Vous prêtez à usure l’un à l’autre!" Et je convoquai une grande assemblée contre eux.
8 Na ce, “Da dukan iyakar ƙoƙarinmu, mun fanshi’yan’uwanmu Yahudawan da aka sayar wa Al’ummai. Amma ga shi kuna sayar da’yan’uwanku ga Al’ummai, don kawai a sāke sayar mana da su!”
Là, je leur dis: "Nous, nous avons racheté nos frères, les Judéens, qui étaient vendus aux Gentils, autant que cela était en notre pouvoir; et vous, vous voudriez vendre vos frères, et c’est à nous qu’ils seraient vendus!" Ils se turent, ne trouvant rien à répliquer.
9 Saboda haka na ci gaba na ce, “Abin da kuke yi a yanzu ba daidai ba ne. Bai kamata ku yi tafiya cikin tsoron Allahnmu don mu guji ba’ar Al’ummai abokan gābanmu ba?
J’Ajoutai: "Ce que vous faites n’est pas bien. Ne devriez-vous pas marcher dans la crainte de notre Dieu, ne serait-ce qu’à cause des outrages des Gentils, qui sont nos ennemis?
10 Ni ma da’yan’uwana da kuma mutanena muna ba wa mutane bashin kuɗi da kuma hatsi. Sai mu daina sha’anin ba da rance da ruwa!
Moi aussi, de même que mes frères et mes gens, nous leur avons prêté de l’argent et du blé; de grâce, renonçons tous au paiement de ces dettes.
11 Yau sai ku mayar musu da gonakinsu, da gonakin inabinsu, da na zaitunsu, da gidajensu, da kashi ɗaya bisa ɗari na kuɗi, da na hatsi, da na ruwan inabi, da na mai, waɗanda kuka karɓa a wurinsu.”
Restituez-leur aujourd’hui même, je vous en prie, leurs champs, leurs vignes, leurs oliviers et leurs maisons, et abandonnez-leur les centaines de pièces d’argent, le blé, le moût et l’huile que vous leur avez prêtés."
12 Suka ce, “Za mu mayar musu, kuma ba za mu bukaci wani abu daga gare su ba. Za mu yi yadda ka faɗa.” Sai na tattara firistoci na kuma sa manyan gari da shugabanni su yi rantsuwa don su yi abin da suka yi alkawari.
Ils répondirent: "Nous rendrons tout, sans rien exiger d’eux; nous ferons tout comme tu le dis!" Alors je mandai les prêtres et devant ceux-ci je leur fis jurer d’agir ainsi.
13 Na kuma kakkaɓe hannuna, na ce, “Duk wanda ya karya wannan alkawari, haka Allah zai kakkaɓe shi daga gidansa da aikinsa. Allah zai kakkaɓe shi, yă wofintar da shi!” Da jin wannan, sai dukan taron suka ce, “Amin,” suka kuma yabi Ubangiji. Mutane kuwa suka yi kamar yadda suka yi alkawari.
Je secouai aussi le pan de mon vêtement en disant: "Que Dieu secoue ainsi et arrache à sa maison et à ses biens tout homme qui n’accomplira pas cette parole! Puisse-t-il être ainsi secoué et dépouillé!" Toute l’assemblée dit: "Amen!" Ils louèrent l’Éternel, et le peuple se conforma à la décision prise.
14 Ban da haka ma, daga shekara ta ashirin ta Sarki Artazerzes, sa’ad da aka naɗa ni in zama gwamnansu a ƙasar Yahuda, har zuwa shekara ta talatin da biyu na mulkinsa, shekara sha biyu ke nan, ko ni, ko’yan’uwana, ba wanda ya ci abincin da akan ba wa gwamna.
J’Ajoute qu’à partir du jour où le roi m’avait investi des fonctions de gouverneur du pays de Juda depuis la vingtième année jusqu’à la trente-deuxième année du roi Artahchasta, pendant douze années, je n’ai, non plus que mes frères, vécu des aliments dus au gouverneur.
15 Amma gwamnonin farko, waɗanda suka riga ni, sun ɗaura wa mutane kaya mai nauyi suka karɓi shekel arba’in na azurfa daga gare su haɗe da abinci da kuma ruwan inabi. Har bayin masu mulki ma sun nawaya wa mutane. Amma ni ban yi haka ba, saboda ina tsoron Allah.
Les précédents gouverneurs, mes prédécesseurs, chargeaient lourdement les gens du peuple; ils recevaient d’eux, en pain et en vin, une valeur dépassant quarante sicles par jour. Leurs valets aussi pressuraient le peuple. Moi, je n’agissais pas de la sorte, par respect de la divinité.
16 A maimakon haka, na miƙa kaina ga aiki a kan wannan katanga. Na tattara dukan mutanena a can don aikin; ba mu samar wa kanmu wata gona ba.
J’Ai aussi mis la main au travail du mur, nous n’avons acheté aucune terre, et tous mes gens étaient groupés là, occupés de la besogne.
17 Bugu da ƙari, Yahudawa da shugabanni ɗari da hamsin suna ci daga teburina, haka ma waɗanda suka zo wurinmu daga ƙasashen da suke kewaye.
Les Judéens et les chefs, au nombre de cent cinquante personnes, et ceux qui venaient à nous d’entre les Gentils, demeurant dans notre voisinage, étaient admis à ma table.
18 Kowace rana akan shirya mini saniya ɗaya, zaɓaɓɓun tumaki shida da waɗansu kaji, kuma kowace kwana goma akan tanadar da ruwan inabi na kowane iri a yalwace. Duk da haka, ban taɓa nemi a ba ni abincin da akan ba wa gwamna ba, domin wahala ta yi wa jama’a yawa.
Et ce qu’on apprêtait pour chaque jour un bœuf, six moutons de choix et des volailles tout cela était apprêté à mes frais; de même pour chaque période de dix jours, toutes sortes de vins en quantité. Malgré cela, je ne réclamais point les subsistances dues au gouverneur, car la corvée était lourde pour le peuple.
19 Ka tuna da ni, ka yi mini alheri, ya Allah, saboda dukan abubuwan da na yi saboda waɗannan mutane.
Tiens-moi compte, ô mon Dieu, pour mon bien, de tout ce que j’ai fait en faveur de ce peuple!