< Nehemiya 5 >

1 To, sai maza da matansu suka tā da fara gunaguni mai tsanani a kan’yan’uwansu Yahudawa.
[Later, ] many of the men and their wives protested loudly about what [some of] the [other] Jews were doing.
2 Waɗansu suka ce, “Mu da’ya’yanmu maza da mata muna da yawa, muna bukatar hatsi domin mu ci mu rayu.”
Some/One of them said, “We have many children. So we need a lot of grain to be able to eat and continue to live.”
3 Waɗansu kuwa suka ce, “Saboda yunwa mun jinginar da gonakinmu, da gonakin inabinmu, da gidajenmu don mu sami hatsi.”
Others said, “The fields and vineyards and houses that we own, it has been necessary for us to (mortgage them/promise to give them to someone if we do not pay back to him the money he has loaned us) in order to get money to buy grain, during this (famine/time where there is not much food).”
4 Har illa yau waɗansu suka ce, “Mun ci bashin kuɗi don mu biya haraji a kan gonakinmu, da gonakin inabinmu.
Others said, “We have [needed to] borrow money to pay the taxes that the king [commanded us to pay] on our fields and our vineyards.
5 Ga shi kuwa, mu da su dangin juna ne,’ya’yanmu da nasu kuma ɗaya ne, duk da haka an tilasta mu mu sa’ya’yanmu mata da maza su zama bayi. Har ma an riga an bautar waɗansu daga cikin’ya’yanmu mata, amma ba mu da iko mu ce kome, domin gonakinmu da gonakin inabinmu suna a hannun waɗansu mutane.”
We are Jews just like [IDM] they are. Our children are ([just as good as/equal with)] their children. But we have needed to sell some of our children to become slaves [in order to pay what we owe]. We have already sold some of our daughters to become slaves. Our fields and vineyards have been taken away from us, so now we do not have [the money to pay what we owe, and we are forced to sell our children to get money to pay those debts].”
6 Sa’ad da na ji kukansu da waɗannan koke-koke, na husata ƙwarai.
I was very angry when I heard these things that they were complaining about.
7 Na yi tunaninsu a zuciyata sa’an nan na zargi manyan gari da shugabanni. Na ce musu, “Kuna musguna wa’yan’uwanku ta wurin ba su rance da ruwa!” Saboda haka na kira babban taro gaba ɗaya don a magance wannan.
So I thought about what I could do about it. I told the leaders and officials [who were responsible for this work], “You are charging interest to your own relatives [when they borrow money from you]!” Then I called together a large group of people,
8 Na ce, “Da dukan iyakar ƙoƙarinmu, mun fanshi’yan’uwanmu Yahudawan da aka sayar wa Al’ummai. Amma ga shi kuna sayar da’yan’uwanku ga Al’ummai, don kawai a sāke sayar mana da su!”
and I said to their [leaders], “Some of our Jewish relatives have been forced to sell themselves to become slaves of people who have come from other countries. As much as we have been able to, we have been buying them back [out of slavery]. But now you are forcing your own relatives to sell themselves to you, their fellow Jews, as slaves!” [When I said that to them, ] they were silent. There was nothing that they could say [because they knew that what I said was true].
9 Saboda haka na ci gaba na ce, “Abin da kuke yi a yanzu ba daidai ba ne. Bai kamata ku yi tafiya cikin tsoron Allahnmu don mu guji ba’ar Al’ummai abokan gābanmu ba?
Then I said to them, “What you are doing is terrible [EUP]! You certainly ought to [RHQ] obey God and do what is right! If you did that, our enemies who do not revere Yahweh [would see that we are doing what is right and] would not ridicule us.
10 Ni ma da’yan’uwana da kuma mutanena muna ba wa mutane bashin kuɗi da kuma hatsi. Sai mu daina sha’anin ba da rance da ruwa!
My fellow Jews and I and my servants have lent money and grain to people [without charging interest]. So you all should stop charging interest on these loans.
11 Yau sai ku mayar musu da gonakinsu, da gonakin inabinsu, da na zaitunsu, da gidajensu, da kashi ɗaya bisa ɗari na kuɗi, da na hatsi, da na ruwan inabi, da na mai, waɗanda kuka karɓa a wurinsu.”
Also, you must give back to them their fields, their vineyards, their olive tree orchards, and their houses that you have taken from them. You must also give back to them the interest that you charged them when they borrowed money, grain, wine, and [olive] oil from you, and you must do it today!”
12 Suka ce, “Za mu mayar musu, kuma ba za mu bukaci wani abu daga gare su ba. Za mu yi yadda ka faɗa.” Sai na tattara firistoci na kuma sa manyan gari da shugabanni su yi rantsuwa don su yi abin da suka yi alkawari.
The leaders replied, “We will do what you have said. We will return to them everything that we forced them to give to us, and we will not require that they give us anything more.” Then I summoned the priests, and I forced the leaders to vow in front of them that they would do what they had promised to do.
13 Na kuma kakkaɓe hannuna, na ce, “Duk wanda ya karya wannan alkawari, haka Allah zai kakkaɓe shi daga gidansa da aikinsa. Allah zai kakkaɓe shi, yă wofintar da shi!” Da jin wannan, sai dukan taron suka ce, “Amin,” suka kuma yabi Ubangiji. Mutane kuwa suka yi kamar yadda suka yi alkawari.
I shook out the folds of my robe and said to them, “If you do not do what you have just now promised to do, I hope/desire that God will shake you like I am shaking my robe. He will take away your homes and everything else that you own.” They all replied, “Amen/May it be so!” And they praised Yahweh. Then they did what they had promised to do.
14 Ban da haka ma, daga shekara ta ashirin ta Sarki Artazerzes, sa’ad da aka naɗa ni in zama gwamnansu a ƙasar Yahuda, har zuwa shekara ta talatin da biyu na mulkinsa, shekara sha biyu ke nan, ko ni, ko’yan’uwana, ba wanda ya ci abincin da akan ba wa gwamna.
I was appointed to be the governor of Judea in the twentieth year that Artaxerxes was the king [of Persia]. For the next twelve years, until he had been ruling for almost 32 years, neither I nor my officials accepted [the money that we were allowed/entitled to receive to buy] food because of my being the governor.
15 Amma gwamnonin farko, waɗanda suka riga ni, sun ɗaura wa mutane kaya mai nauyi suka karɓi shekel arba’in na azurfa daga gare su haɗe da abinci da kuma ruwan inabi. Har bayin masu mulki ma sun nawaya wa mutane. Amma ni ban yi haka ba, saboda ina tsoron Allah.
The men who were governors before I became the governor had burdened the people by requiring them to pay a lot of taxes. They had forced each person to pay to them 40 silver coins every day, in addition to giving food and wine to them. Even their servants/officials oppressed the people. But I did not do that, because I revered God.
16 A maimakon haka, na miƙa kaina ga aiki a kan wannan katanga. Na tattara dukan mutanena a can don aikin; ba mu samar wa kanmu wata gona ba.
I also continued to work on the wall, and I did not take land from people [who were unable to pay back the money that they had borrowed from me]. All those who worked for me joined me to work on the wall.
17 Bugu da ƙari, Yahudawa da shugabanni ɗari da hamsin suna ci daga teburina, haka ma waɗanda suka zo wurinmu daga ƙasashen da suke kewaye.
Also, every day I was responsible to feed 150 Jewish officials, and also [official] visitors who came from nearby countries.
18 Kowace rana akan shirya mini saniya ɗaya, zaɓaɓɓun tumaki shida da waɗansu kaji, kuma kowace kwana goma akan tanadar da ruwan inabi na kowane iri a yalwace. Duk da haka, ban taɓa nemi a ba ni abincin da akan ba wa gwamna ba, domin wahala ta yi wa jama’a yawa.
Each day I [told my servants to] serve [us the meat from] one ox, six very good sheep, and chickens. And every ten days I gave them a large new supply of wine. But I knew that the people were burdened [by paying lots of taxes], so I did not accept [the money that I was entitled/allowed to receive to buy all this] food because of my being the governor.
19 Ka tuna da ni, ka yi mini alheri, ya Allah, saboda dukan abubuwan da na yi saboda waɗannan mutane.
My God, do not forget me, and reward me because of all that I have done for these people.

< Nehemiya 5 >