< Nehemiya 4 >

1 Da Sanballat ya ji cewa muna sāke ginin katangar, sai ya husata, ya haukace ƙwarai. Ya yi wa Yahudawa dariya,
Toda pripetilo se je, da ko je Sanbalát slišal, da smo gradili zid, da je bil besen in polastilo se ga je veliko ogorčenje in zasmehoval je Jude.
2 a gaban abokansa da kuma sojojin Samariya ya ce, “Me waɗancan Yahudawan nan marasa ƙarfi suke yi? Za su maido da katangarsu ne? Za su miƙa hadayu ne? Za su gama a rana ɗaya? Za su iya samun duwatsun gini daga tsibin matattun duwatsu?”
Pred svojimi brati in vojsko Samarije je spregovoril ter rekel: »Kaj počno ti slabotni Judje? Mar se bodo utrdili? Mar bodo žrtvovali? Mar bodo končali v [enem] dnevu? Mar bodo oživili kamne iz kupov smeti, ki so požgane?«
3 Tobiya wakilin mutanen Ammon wanda yake a gefensa ya ce, “Abin nan da suke gini, ko dila ma ya hau, zai rushe shi!”
Torej Amónec Tobija je bil ob njem in rekel: »Celo to, kar so zgradili, če gre gor lisjak, bo torej porušil njihov kamniti zid.«
4 Ka ji mu, ya Allahnmu, gama an rena mu. Bari zagin da suke yi mana yă koma kansu. Ka sa a kwashe su a kai su bauta a wata ƙasa.
Prisluhni, oh naš Bog, kajti mi smo prezirani. Obrni njihovo grajo na njihovo lastno glavo in jih daj za plen v deželi ujetništva
5 Kada ka rufe laifinsu, kada kuwa ka gafarta musu, gama sun ci mutuncinmu, mu da muke gini.
in ne pokrij njihove krivičnosti in naj njihov greh ne bo izbrisan izpred tebe, kajti do jeze so te izzivali pred graditelji.
6 Sai muka sāke ginin katangar sai da duka ta kai rabin tsayinta, gama mutane sun yi aiki da dukan ƙarfinsu.
Tako smo gradili obzidje in vse obzidje je bilo združeno skupaj do njegove polovice, kajti ljudstvo je imelo um, da dela.
7 Amma da Sanballat, da Tobiya, da Larabawa, da Ammonawa, da kuma mutanen Ashdod suka ji cewa gyare-gyaren katangar Urushalima yana cin gaba, ana kuma tattoshe wuraren da suka tsattsaga, sai suka husata ƙwarai.
Toda pripetilo se je, da ko so Sanbalát, Tobija, Arabci, Amónci in Ašdódčani slišali, da so bili zidovi Jeruzalema postavljeni in da so se vrzeli začele zapolnjevati, potem so bili zelo besni
8 Dukansu suka ƙulla su zo, su yi yaƙi da Urushalima, su tā da hankali a cikinta.
in vsi skupaj so skovali zaroto, da pridejo in se borijo zoper Jeruzalem in da to ovirajo.
9 Amma muka yi addu’a ga Allahnmu muka kuma sa masu tsaro da rana da kuma dare don mu magance wannan barazana.
Kljub temu smo naredili svojo molitev k svojemu Bogu in podnevi ter ponoči zaradi njih postavili stražo.
10 Ana cikin haka, mutane a Yahuda suka ce, “Ƙarfin ma’aikata yana kāsawa, akwai kuma sauran tarkace da yawa da ba za mu iya sāke gina katangar ba.”
Juda je rekel: »Moč nosilcev bremen je oslabela in tam je veliko smeti, tako, da nismo zmožni graditi obzidja.«
11 Abokan gābanmu sun ce, “Ba za su sani ba, ba kuwa za su gan mu ba, sai dai kawai su gan mu a cikinsu, za mu karkashe su, mu tsai da aikin.”
Naši nasprotniki pa so rekli: »Ne bodo vedeli niti videli, dokler ne pridemo v sredo mednje in jih pobijemo in povzročimo, da delo preneha.«
12 Sau da yawa Yahudawan da suke da zama kusa da abokan gābanmu sun yi ta zuwa suna yin mana magana, suna cewa “Ko’ina muka juya, za su fāɗa mana.”
Pripetilo pa se je, ko so prišli Judje, ki so prebivali poleg njih, da so nam desetkrat rekli: »Iz vseh krajev, od koder se boste vrnili k nam, bodo oni nad vami.«
13 Saboda haka na sa jama’a su ja ɗamara bisa ga iyalinsu a bayan katanga, a wuraren da ba a gina ba. Suna riƙe da takuba, da māsu, da bakkuna.
Zato sem postavil na nižjih mestih za obzidjem in na višjih mestih, sem celo postavil ljudstvo po njihovih družinah, z njihovimi meči, njihovimi sulicami in njihovimi loki.
14 Bayan na dudduba abubuwa, sai na miƙe tsaye na ce wa manyan gari da shugabanni da kuma sauran jama’a, “Kada ku ji tsoronsu. Ku tuna da Ubangiji, wanda yake mai girma da banrazana, ku yi yaƙi don’yan’uwanku, da’ya’yanku maza da mata, da matanku da kuma gidajenku.”
Pogledal sem, vstal in rekel plemičem, vladarjem in ostalemu ljudstvu: »Ne bojte se jih. Spominjajte se Gospoda, ki je velik in strašen in borite se za svoje brate, svoje sinove in svoje hčere, svoje žene in svoje hiše.«
15 Da abokan gābanmu suka ji muna sane da shirinsu, Allah kuma ya wargaje shirin nan, sai duk muka dawo ga katangar, kowa ya kama aikinsa.
Pripetilo se je, ko so naši sovražniki slišali, da nam je bilo to znano in je Bog njihovo namero privedel v nič, da smo se vsi izmed nas vrnili k obzidju, vsak k svojemu delu.
16 Daga wannan rana zuwa gaba, rabin mutane suka yi aiki, yayinda sauran rabin suka kintsa da māsu, da garkuwa, da bakkuna da makamai. Shugabanni suka goyi bayan dukan mutanen Yahuda
Pripetilo se je od tega časa naprej, da je polovica mojih služabnikov delala na delu, druga polovica pa je držala sulice, ščite, loke in brezrokavne verižne srajce in vladarji so bili zadaj za vso Judovo hišo.
17 waɗanda suke ginin katanga. Waɗanda suke ɗaukan kaya suka yi aikinsu da hannu ɗaya, suna kuma riƙe da makami a ɗaya hannun,
Tisti, ki so gradili na obzidju in tisti, ki so nosili bremena, s tistimi, ki so prenašali, vsak je z eno roko opravljal delo, z drugo roko pa je držal orožje.
18 kuma kowane mai gini ya ɗaura takobinsa a gefe yayinda yake aiki. Amma mutum mai busa ƙaho ya kasance tare da ni.
Kajti graditelji so gradili tako, da je imel vsakdo svoj meč opasan ob svoji strani. Tisti, ki je trobil na šofar, pa je bil poleg mene.
19 Sai na ce wa manyan gari, da shugabanni, da sauran jama’a, “Aikin nan babba ne kuma mai yawa, ga shi muna a rarrabe nesa da juna a katangar.
Rekel sem plemičem, vladarjem in ostalemu ljudstvu: »Delo je veliko in obsežno, mi pa smo na obzidju ločeni, eden daleč od drugega.
20 Duk inda kuka ji an busa ƙaho, sai ku taru a wurin. Allahnmu zai yi yaƙi dominmu!”
Na katerem mestu torej zaslišite glas šofarja, krenite tja k nam. Naš Bog se bo boril za nas.«
21 Saboda haka muka ci gaba da aiki, rabin mutane suna riƙe da māsu, daga wayewar gari har zuwa fitowar taurari.
Tako smo se trudili na delu. Polovica izmed njih je sulice držala od jutranjega vzhoda do pojavitve zvezd.
22 A wannan lokaci na kuma ce wa mutane, “A sa kowane mutum da mataimakinsa su zauna a Urushalima da dare, domin a yi tsaro da dare, da safe kuma a kama aiki.”
Prav tako sem ljudstvu istočasno rekel: »Naj vsak s svojim služabnikom prenočuje znotraj Jeruzalema, da nam bodo ponoči lahko straža in se trudili podnevi.«
23 Saboda haka ni, da’yan’uwana, da bayina, da matsaran da suke tare da ni, ba wanda ya tuɓe tufafinsa; kowa ya rataye makaminsa, ko ya je shan ruwa ma.
Tako niti jaz, niti moji bratje, niti moji služabniki, niti ljudje na straži, ki so mi sledili, nihče izmed nas ni odložil svojih oblačil, razen, da jih je vsak slekel za pranje.

< Nehemiya 4 >