< Nehemiya 4 >

1 Da Sanballat ya ji cewa muna sāke ginin katangar, sai ya husata, ya haukace ƙwarai. Ya yi wa Yahudawa dariya,
Or il arriva que lorsque Sanaballat eut appris que nous bâtissions le mur, il fut très irrité, et, extrêmement ému, il railla les Juifs,
2 a gaban abokansa da kuma sojojin Samariya ya ce, “Me waɗancan Yahudawan nan marasa ƙarfi suke yi? Za su maido da katangarsu ne? Za su miƙa hadayu ne? Za su gama a rana ɗaya? Za su iya samun duwatsun gini daga tsibin matattun duwatsu?”
Et dit devant ses frères et une grande foule de Samaritains: Que font ces Juifs imbéciles? Est-ce que les nations les laisseront faire? Est-ce qu’ils sacrifieront et achèveront en un seul jour? Est-ce qu’ils pourront bâtir en tirant d’entre des monceaux de poussière les pierres qui ont été brûlées?
3 Tobiya wakilin mutanen Ammon wanda yake a gefensa ya ce, “Abin nan da suke gini, ko dila ma ya hau, zai rushe shi!”
Mais même Tobie, l’Ammanite, qui était près de lui, dit: Qu’ils bâtissent; et si un renard monte, il franchira leur mur de pierre.
4 Ka ji mu, ya Allahnmu, gama an rena mu. Bari zagin da suke yi mana yă koma kansu. Ka sa a kwashe su a kai su bauta a wata ƙasa.
Ecoutez, ô notre Dieu, parce que nous sommes devenus un objet de mépris, détournez l’opprobre sur leur tête, et livrez-les au mépris dans une terre de captivité.
5 Kada ka rufe laifinsu, kada kuwa ka gafarta musu, gama sun ci mutuncinmu, mu da muke gini.
Ne couvrez point leur iniquité, et que leur crime ne soit point effacé de devant votre face; car ils ont raillé ceux qui bâtissaient.
6 Sai muka sāke ginin katangar sai da duka ta kai rabin tsayinta, gama mutane sun yi aiki da dukan ƙarfinsu.
C’est pourquoi nous bâtîmes le mur; et nous unîmes le tout jusqu’à la moitié, et le cœur du peuple fut excité à travailler.
7 Amma da Sanballat, da Tobiya, da Larabawa, da Ammonawa, da kuma mutanen Ashdod suka ji cewa gyare-gyaren katangar Urushalima yana cin gaba, ana kuma tattoshe wuraren da suka tsattsaga, sai suka husata ƙwarai.
Or il arriva que lorsque Sanaballat, Tobie, les Arabes, les Ammanites, et ceux d’Azot, eurent appris que les crevasses du mur de Jérusalem étaient bouchées, et que les brèches commençaient à être fermées, ils furent extrêmement irrités;
8 Dukansu suka ƙulla su zo, su yi yaƙi da Urushalima, su tā da hankali a cikinta.
Et ils s’assemblèrent tous à la fois pour venir et combattre contre Jérusalem, et nous dresser des embûches.
9 Amma muka yi addu’a ga Allahnmu muka kuma sa masu tsaro da rana da kuma dare don mu magance wannan barazana.
Et nous priâmes notre Dieu, et nous mîmes des gardes sur le mur, jour et nuit, contre eux.
10 Ana cikin haka, mutane a Yahuda suka ce, “Ƙarfin ma’aikata yana kāsawa, akwai kuma sauran tarkace da yawa da ba za mu iya sāke gina katangar ba.”
Or Juda dit: Elle est affaiblie, la force de celui qui porte; il y a trop de terre et nous ne pourrons pas bâtir le mur.
11 Abokan gābanmu sun ce, “Ba za su sani ba, ba kuwa za su gan mu ba, sai dai kawai su gan mu a cikinsu, za mu karkashe su, mu tsai da aikin.”
Et nos ennemis ont dit: Qu’ils ne sachent pas, mais qu’ils ignorent le moment où nous viendrons au milieu d’eux, où nous les tuerons, et où nous ferons cesser l’ouvrage.
12 Sau da yawa Yahudawan da suke da zama kusa da abokan gābanmu sun yi ta zuwa suna yin mana magana, suna cewa “Ko’ina muka juya, za su fāɗa mana.”
Mais il arriva que les Juifs qui habitaient près d’eux étant venus vers nous et nous l’ayant dit par dix fois, de tous les lieux d’où ils étaient venus vers nous,
13 Saboda haka na sa jama’a su ja ɗamara bisa ga iyalinsu a bayan katanga, a wuraren da ba a gina ba. Suna riƙe da takuba, da māsu, da bakkuna.
Je plaçai dans l’endroit, derrière le mur, tout autour, le peuple en ordre, avec leurs glaives, leurs lances et leurs arcs.
14 Bayan na dudduba abubuwa, sai na miƙe tsaye na ce wa manyan gari da shugabanni da kuma sauran jama’a, “Kada ku ji tsoronsu. Ku tuna da Ubangiji, wanda yake mai girma da banrazana, ku yi yaƙi don’yan’uwanku, da’ya’yanku maza da mata, da matanku da kuma gidajenku.”
Alors je regardai attentivement, puis je me levai, et je dis aux grands, aux magistrats et au reste du peuple: Ne craignez point devant eux. Souvenez-vous du Seigneur, le grand et le terrible, et combattez pour vos frères, vos fils, vos filles, vos femmes et vos maisons.
15 Da abokan gābanmu suka ji muna sane da shirinsu, Allah kuma ya wargaje shirin nan, sai duk muka dawo ga katangar, kowa ya kama aikinsa.
Or il arriva que, lorsque nos ennemis apprirent que nous avions été avertis, Dieu dissipa leur conseil; et nous retournâmes tous aux murs, chacun à son ouvrage.
16 Daga wannan rana zuwa gaba, rabin mutane suka yi aiki, yayinda sauran rabin suka kintsa da māsu, da garkuwa, da bakkuna da makamai. Shugabanni suka goyi bayan dukan mutanen Yahuda
Et il arriva que, depuis ce jour-là, la moitié des jeunes hommes faisait l’ouvrage, et l’autre moitié était prête au combat; et les lances et les boucliers, et les arcs et les cuirasses, et les princes, étaient derrière eux, dans toute la maison de Juda;
17 waɗanda suke ginin katanga. Waɗanda suke ɗaukan kaya suka yi aikinsu da hannu ɗaya, suna kuma riƙe da makami a ɗaya hannun,
La moitié de ceux qui bâtissaient au mur, qui portaient les fardeaux, et qui les chargeaient, faisait d’une main l’ouvrage, et de l’autre tenait le glaive;
18 kuma kowane mai gini ya ɗaura takobinsa a gefe yayinda yake aiki. Amma mutum mai busa ƙaho ya kasance tare da ni.
Car chacun de ceux qui bâtissaient était ceint de son épée aux reins. Ils bâtissaient donc, et ils sonnaient de la trompette auprès de moi,
19 Sai na ce wa manyan gari, da shugabanni, da sauran jama’a, “Aikin nan babba ne kuma mai yawa, ga shi muna a rarrabe nesa da juna a katangar.
Et je dis aux grands, aux magistrats et au reste du peuple: L’ouvrage est grand et de longue étendue, et nous sommes séparés sur le mur, loin l’un de l’autre;
20 Duk inda kuka ji an busa ƙaho, sai ku taru a wurin. Allahnmu zai yi yaƙi dominmu!”
Eu quelque lieu que vous entendiez le son de la trompette, accourez-y vers nous, notre Dieu combattra pour nous.
21 Saboda haka muka ci gaba da aiki, rabin mutane suna riƙe da māsu, daga wayewar gari har zuwa fitowar taurari.
Et nous-mêmes faisons l’ouvrage; et que la moitié de nous tienne la lance, depuis l’ascension de l’aurore jusqu’à ce que sortent les astres.
22 A wannan lokaci na kuma ce wa mutane, “A sa kowane mutum da mataimakinsa su zauna a Urushalima da dare, domin a yi tsaro da dare, da safe kuma a kama aiki.”
En ce temps-là aussi je dis au peuple: Que chacun, avec son serviteur, reste au milieu de Jérusalem; et remplaçons - nous pendant la nuit et le jour pour travailler.
23 Saboda haka ni, da’yan’uwana, da bayina, da matsaran da suke tare da ni, ba wanda ya tuɓe tufafinsa; kowa ya rataye makaminsa, ko ya je shan ruwa ma.
Or, moi, mes frères et mes serviteurs, et les gardes qui étaient derrière moi, nous ne quittions point nos vêtements, et chacun se dépouillait seulement pour se laver.

< Nehemiya 4 >