< Nehemiya 4 >

1 Da Sanballat ya ji cewa muna sāke ginin katangar, sai ya husata, ya haukace ƙwarai. Ya yi wa Yahudawa dariya,
Mais lorsque Sanballat apprit que nous construisions la muraille, il se mit en colère, fut très indigné, et se moqua des Juifs.
2 a gaban abokansa da kuma sojojin Samariya ya ce, “Me waɗancan Yahudawan nan marasa ƙarfi suke yi? Za su maido da katangarsu ne? Za su miƙa hadayu ne? Za su gama a rana ɗaya? Za su iya samun duwatsun gini daga tsibin matattun duwatsu?”
Il prit la parole devant ses frères et l'armée de Samarie, et dit: « Que font ces faibles Juifs? Vont-ils se fortifier? Vont-ils faire des sacrifices? Vont-ils finir en un jour? Vont-ils faire revivre les pierres des tas d'ordures, puisqu'elles sont brûlées? »
3 Tobiya wakilin mutanen Ammon wanda yake a gefensa ya ce, “Abin nan da suke gini, ko dila ma ya hau, zai rushe shi!”
Or Tobija, l'Ammonite, était près de lui, et il disait: « Ce qu'ils construisent, si un renard y grimpait, il briserait leur mur de pierre. »
4 Ka ji mu, ya Allahnmu, gama an rena mu. Bari zagin da suke yi mana yă koma kansu. Ka sa a kwashe su a kai su bauta a wata ƙasa.
« Écoute, notre Dieu, car nous sommes méprisés. Renvoie leur opprobre sur leur propre tête. Livrez-les au pillage dans un pays de captivité.
5 Kada ka rufe laifinsu, kada kuwa ka gafarta musu, gama sun ci mutuncinmu, mu da muke gini.
Ne couvre pas leur iniquité. Ne laisse pas leur péché s'effacer devant toi, car ils ont insulté les bâtisseurs. »
6 Sai muka sāke ginin katangar sai da duka ta kai rabin tsayinta, gama mutane sun yi aiki da dukan ƙarfinsu.
Nous construisîmes donc la muraille, et toute la muraille fut jointe jusqu'à la moitié de sa hauteur, car le peuple avait envie de travailler.
7 Amma da Sanballat, da Tobiya, da Larabawa, da Ammonawa, da kuma mutanen Ashdod suka ji cewa gyare-gyaren katangar Urushalima yana cin gaba, ana kuma tattoshe wuraren da suka tsattsaga, sai suka husata ƙwarai.
Mais lorsque Sanballat, Tobija, les Arabes, les Ammonites et les Asdodiens apprirent que la réparation des murs de Jérusalem avançait et que les brèches commençaient à être comblées, ils furent très en colère;
8 Dukansu suka ƙulla su zo, su yi yaƙi da Urushalima, su tā da hankali a cikinta.
et ils se concertèrent tous pour venir attaquer Jérusalem et semer la confusion parmi nous.
9 Amma muka yi addu’a ga Allahnmu muka kuma sa masu tsaro da rana da kuma dare don mu magance wannan barazana.
Mais nous avons prié notre Dieu, et nous avons veillé jour et nuit sur eux, à cause d'eux.
10 Ana cikin haka, mutane a Yahuda suka ce, “Ƙarfin ma’aikata yana kāsawa, akwai kuma sauran tarkace da yawa da ba za mu iya sāke gina katangar ba.”
Juda dit: « La force des porteurs de fardeaux s'affaiblit et il y a beaucoup de décombres, de sorte que nous ne pouvons pas construire la muraille. »
11 Abokan gābanmu sun ce, “Ba za su sani ba, ba kuwa za su gan mu ba, sai dai kawai su gan mu a cikinsu, za mu karkashe su, mu tsai da aikin.”
Nos adversaires ont dit: « Ils ne sauront ni ne verront, jusqu'à ce que nous entrions au milieu d'eux, que nous les tuions et que nous fassions cesser l'ouvrage. »
12 Sau da yawa Yahudawan da suke da zama kusa da abokan gābanmu sun yi ta zuwa suna yin mana magana, suna cewa “Ko’ina muka juya, za su fāɗa mana.”
Lorsque les Juifs qui habitaient près d'eux arrivèrent, ils nous dirent dix fois de toutes parts: « Où que vous vous tourniez, ils nous attaqueront. »
13 Saboda haka na sa jama’a su ja ɗamara bisa ga iyalinsu a bayan katanga, a wuraren da ba a gina ba. Suna riƙe da takuba, da māsu, da bakkuna.
C'est pourquoi j'ai placé des gardes dans les parties les plus basses de l'espace derrière la muraille, dans les endroits ouverts. Je plaçai le peuple par groupes de familles, avec leurs épées, leurs lances et leurs arcs.
14 Bayan na dudduba abubuwa, sai na miƙe tsaye na ce wa manyan gari da shugabanni da kuma sauran jama’a, “Kada ku ji tsoronsu. Ku tuna da Ubangiji, wanda yake mai girma da banrazana, ku yi yaƙi don’yan’uwanku, da’ya’yanku maza da mata, da matanku da kuma gidajenku.”
Je regardai, je me levai et je dis aux nobles, aux chefs et au reste du peuple: « N'ayez pas peur d'eux! Souvenez-vous du Seigneur, qui est grand et redoutable, et combattez pour vos frères, vos fils, vos filles, vos femmes et vos maisons. »
15 Da abokan gābanmu suka ji muna sane da shirinsu, Allah kuma ya wargaje shirin nan, sai duk muka dawo ga katangar, kowa ya kama aikinsa.
Lorsque nos ennemis apprirent que cela nous était connu, et que Dieu avait fait échouer leurs projets, nous retournâmes tous à la muraille, chacun à son ouvrage.
16 Daga wannan rana zuwa gaba, rabin mutane suka yi aiki, yayinda sauran rabin suka kintsa da māsu, da garkuwa, da bakkuna da makamai. Shugabanni suka goyi bayan dukan mutanen Yahuda
A partir de ce moment-là, la moitié de mes serviteurs travailla à l'ouvrage, et la moitié tint les lances, les boucliers, les arcs et les cottes de mailles; les chefs étaient derrière toute la maison de Juda.
17 waɗanda suke ginin katanga. Waɗanda suke ɗaukan kaya suka yi aikinsu da hannu ɗaya, suna kuma riƙe da makami a ɗaya hannun,
Ceux qui construisaient la muraille et ceux qui portaient les fardeaux se chargeaient eux-mêmes; chacun faisait l'ouvrage avec une de ses mains, et de l'autre tenait son arme.
18 kuma kowane mai gini ya ɗaura takobinsa a gefe yayinda yake aiki. Amma mutum mai busa ƙaho ya kasance tare da ni.
Parmi les bâtisseurs, chacun portait son épée au côté, et c'est ainsi qu'ils bâtissaient. Celui qui sonnait de la trompette était près de moi.
19 Sai na ce wa manyan gari, da shugabanni, da sauran jama’a, “Aikin nan babba ne kuma mai yawa, ga shi muna a rarrabe nesa da juna a katangar.
Je dis aux nobles, aux chefs et au reste du peuple: « L'ouvrage est grand et très étendu, et nous sommes séparés sur la muraille, loin les uns des autres.
20 Duk inda kuka ji an busa ƙaho, sai ku taru a wurin. Allahnmu zai yi yaƙi dominmu!”
Partout où vous entendez le son de la trompette, rassemblez-vous auprès de nous. Notre Dieu combattra pour nous. »
21 Saboda haka muka ci gaba da aiki, rabin mutane suna riƙe da māsu, daga wayewar gari har zuwa fitowar taurari.
Nous avons donc fait le travail. La moitié du peuple tenait les lances depuis le lever du jour jusqu'à l'apparition des étoiles.
22 A wannan lokaci na kuma ce wa mutane, “A sa kowane mutum da mataimakinsa su zauna a Urushalima da dare, domin a yi tsaro da dare, da safe kuma a kama aiki.”
Au même moment, je dis au peuple: « Que chacun, avec son serviteur, loge dans Jérusalem, afin que, la nuit, ils nous servent de garde et que, le jour, ils travaillent. »
23 Saboda haka ni, da’yan’uwana, da bayina, da matsaran da suke tare da ni, ba wanda ya tuɓe tufafinsa; kowa ya rataye makaminsa, ko ya je shan ruwa ma.
Ainsi, ni moi, ni mes frères, ni mes serviteurs, ni les hommes de la garde qui me suivaient n'enlevèrent nos vêtements. Chacun a apporté son arme à l'eau.

< Nehemiya 4 >