< Nehemiya 4 >

1 Da Sanballat ya ji cewa muna sāke ginin katangar, sai ya husata, ya haukace ƙwarai. Ya yi wa Yahudawa dariya,
And it came to pass, when Sanballat heard that we were building the wall, that it displeased him, and he became very angry, and he mocked at the Jews.
2 a gaban abokansa da kuma sojojin Samariya ya ce, “Me waɗancan Yahudawan nan marasa ƙarfi suke yi? Za su maido da katangarsu ne? Za su miƙa hadayu ne? Za su gama a rana ɗaya? Za su iya samun duwatsun gini daga tsibin matattun duwatsu?”
And he spoke before his brethren and the army of Samaria, and said, What are these feeble Jews doing? will people suffer them [to build]? will they sacrifice? will they complete it in one day? will they revive the stones out of the heaps of the rubbish, seeing that they have been burnt?
3 Tobiya wakilin mutanen Ammon wanda yake a gefensa ya ce, “Abin nan da suke gini, ko dila ma ya hau, zai rushe shi!”
And Tobiyah the 'Ammonite was near him, and he said, Even what they are building, if a fox were to run up, he would readily break through their stone wall.
4 Ka ji mu, ya Allahnmu, gama an rena mu. Bari zagin da suke yi mana yă koma kansu. Ka sa a kwashe su a kai su bauta a wata ƙasa.
Hear, O our God! how we are become a scorn; and bring their reproach back upon their own head, and give them up for prey in the land of captivity.
5 Kada ka rufe laifinsu, kada kuwa ka gafarta musu, gama sun ci mutuncinmu, mu da muke gini.
And cover not up their iniquity, and let not their sin be blotted out from before thee; for they have taunted [us] in the presence of the builders.
6 Sai muka sāke ginin katangar sai da duka ta kai rabin tsayinta, gama mutane sun yi aiki da dukan ƙarfinsu.
But we built the wall; and all the wall was joined together up to the half thereof; for the people had a heart to work.
7 Amma da Sanballat, da Tobiya, da Larabawa, da Ammonawa, da kuma mutanen Ashdod suka ji cewa gyare-gyaren katangar Urushalima yana cin gaba, ana kuma tattoshe wuraren da suka tsattsaga, sai suka husata ƙwarai.
And it came to pass, when Sanballat and Tobiyah, and the Arabians, and the 'Ammonites, and the Ashdodites, heard that the walls of Jerusalem were restored, and that the breaches began to be closed up, that it displeased them greatly.
8 Dukansu suka ƙulla su zo, su yi yaƙi da Urushalima, su tā da hankali a cikinta.
And they conspired all of them together to come to fight against Jerusalem, and to do it an injury.
9 Amma muka yi addu’a ga Allahnmu muka kuma sa masu tsaro da rana da kuma dare don mu magance wannan barazana.
But we prayed unto our God, and set a watch over them day and night, because of the others.
10 Ana cikin haka, mutane a Yahuda suka ce, “Ƙarfin ma’aikata yana kāsawa, akwai kuma sauran tarkace da yawa da ba za mu iya sāke gina katangar ba.”
And Judah said, The strength of the bearers of the burden is failing, and there is much rubbish; and we are not able to build on the wall.
11 Abokan gābanmu sun ce, “Ba za su sani ba, ba kuwa za su gan mu ba, sai dai kawai su gan mu a cikinsu, za mu karkashe su, mu tsai da aikin.”
And our adversaries said, “They shall not know, nor see until we come in the midst of them, and slay them, and so stop the work.”
12 Sau da yawa Yahudawan da suke da zama kusa da abokan gābanmu sun yi ta zuwa suna yin mana magana, suna cewa “Ko’ina muka juya, za su fāɗa mana.”
And it came to pass, when the Jews who dwelt near them came, that they said unto us ten times, “From all places whence ye may return home [they intend to come] over us.”
13 Saboda haka na sa jama’a su ja ɗamara bisa ga iyalinsu a bayan katanga, a wuraren da ba a gina ba. Suna riƙe da takuba, da māsu, da bakkuna.
I placed therefore on the lower parts of the place on the naked rocks behind the wall—there I placed the people after their families with their swords, their spears, and their bows.
14 Bayan na dudduba abubuwa, sai na miƙe tsaye na ce wa manyan gari da shugabanni da kuma sauran jama’a, “Kada ku ji tsoronsu. Ku tuna da Ubangiji, wanda yake mai girma da banrazana, ku yi yaƙi don’yan’uwanku, da’ya’yanku maza da mata, da matanku da kuma gidajenku.”
And I looked [about], and rose up, and said unto the nobles, and to the rulers, and to the rest of the people, Be not afraid of them: think on the Lord, the great and terrible, and fight for your brethren, your sons, and your daughters, your wives, and your houses.
15 Da abokan gābanmu suka ji muna sane da shirinsu, Allah kuma ya wargaje shirin nan, sai duk muka dawo ga katangar, kowa ya kama aikinsa.
And it came to pass, that, when our enemies heard that it was known unto us, God frustrated their counsel: and we returned, all of us, to the wall, every one unto his work.
16 Daga wannan rana zuwa gaba, rabin mutane suka yi aiki, yayinda sauran rabin suka kintsa da māsu, da garkuwa, da bakkuna da makamai. Shugabanni suka goyi bayan dukan mutanen Yahuda
And it came to pass from that day forth, that the half of my young men wrought at the work, while the other half of them were holding the spears, the shields, and the bows, and the coats of mail; and the princes stood behind all the house of Judah.
17 waɗanda suke ginin katanga. Waɗanda suke ɗaukan kaya suka yi aikinsu da hannu ɗaya, suna kuma riƙe da makami a ɗaya hannun,
Those that built on the wall, and those that bore burdens, with those that loaded, —every one with one of his hands wrought on the work, and with the other hand held a weapon.
18 kuma kowane mai gini ya ɗaura takobinsa a gefe yayinda yake aiki. Amma mutum mai busa ƙaho ya kasance tare da ni.
And the builders had every one his sword fastened around his loins while they were building; and he that blew the cornet stood alongside of me.
19 Sai na ce wa manyan gari, da shugabanni, da sauran jama’a, “Aikin nan babba ne kuma mai yawa, ga shi muna a rarrabe nesa da juna a katangar.
And I said unto the nobles, and to the rulers, and to the rest of the people, The work is great and extensive, and we are separated upon the wall, distant one from another.
20 Duk inda kuka ji an busa ƙaho, sai ku taru a wurin. Allahnmu zai yi yaƙi dominmu!”
In what place [then] ye hear the sound of the cornet, thither must ye assemble unto us: our God will fight for us.
21 Saboda haka muka ci gaba da aiki, rabin mutane suna riƙe da māsu, daga wayewar gari har zuwa fitowar taurari.
So we labored at the work, while the half of them were holding the spears from the rising of the morning-dawn till the stars appeared.
22 A wannan lokaci na kuma ce wa mutane, “A sa kowane mutum da mataimakinsa su zauna a Urushalima da dare, domin a yi tsaro da dare, da safe kuma a kama aiki.”
Likewise at the same time said I unto the people, Let every one with his young man lodge within Jerusalem, so that they may be in the night a guard to us, and during the day for the labor.
23 Saboda haka ni, da’yan’uwana, da bayina, da matsaran da suke tare da ni, ba wanda ya tuɓe tufafinsa; kowa ya rataye makaminsa, ko ya je shan ruwa ma.
And neither I, nor my brothers, nor my young men, nor the men of the guard who followed me—none of us took off our clothes, no one leaving them off even for washing himself.

< Nehemiya 4 >