< Nehemiya 4 >

1 Da Sanballat ya ji cewa muna sāke ginin katangar, sai ya husata, ya haukace ƙwarai. Ya yi wa Yahudawa dariya,
I stalo se, když uslyšel Sanballat, že stavíme zed, rozpálil se hněvem, a rozzlobiv se velmi, posmíval se Židům.
2 a gaban abokansa da kuma sojojin Samariya ya ce, “Me waɗancan Yahudawan nan marasa ƙarfi suke yi? Za su maido da katangarsu ne? Za su miƙa hadayu ne? Za su gama a rana ɗaya? Za su iya samun duwatsun gini daga tsibin matattun duwatsu?”
Nebo mluvil před bratřími svými a před vojskem Samařským, řka: Co ti bídní Židé berou před sebe? Tak-liž mají býti zanecháni? Což budou obětovati? Za jeden-liž den to dodělati mají? Také-liž i kamení z hromad rumu křísiti budou, kteréž spáleno jest?
3 Tobiya wakilin mutanen Ammon wanda yake a gefensa ya ce, “Abin nan da suke gini, ko dila ma ya hau, zai rushe shi!”
Tobiáš pak Ammonitský podlé něho řekl: Nechať stavějí, však liška přiběhna, prorazí zed jejich kamennou.
4 Ka ji mu, ya Allahnmu, gama an rena mu. Bari zagin da suke yi mana yă koma kansu. Ka sa a kwashe su a kai su bauta a wata ƙasa.
Slyš, ó Bože náš, že jsme v pohrdání, a obrať pohanění jejich na hlavu jejich, a dej je v loupež v zemi, do níž by zajati byli.
5 Kada ka rufe laifinsu, kada kuwa ka gafarta musu, gama sun ci mutuncinmu, mu da muke gini.
A nepřikrývej nepravosti jejich, a hřích jejich od tváři tvé ať není shlazen, proto že jsou tě popouzeli v stavitelích.
6 Sai muka sāke ginin katangar sai da duka ta kai rabin tsayinta, gama mutane sun yi aiki da dukan ƙarfinsu.
A tak stavěli jsme tu zed, a spojili všecku až do polu, a měl lid srdce k tomu dílu.
7 Amma da Sanballat, da Tobiya, da Larabawa, da Ammonawa, da kuma mutanen Ashdod suka ji cewa gyare-gyaren katangar Urushalima yana cin gaba, ana kuma tattoshe wuraren da suka tsattsaga, sai suka husata ƙwarai.
Což když uslyšel Sanballat, a Tobiáš a Arabští, Ammonitští i Azotští, že by na dýl přibývalo zdi Jeruzalémské, a že se již byly počaly mezery zavírati, rozpálili se hněvem velice.
8 Dukansu suka ƙulla su zo, su yi yaƙi da Urushalima, su tā da hankali a cikinta.
Protož spuntovali se všickni společně, aby táhli k boji proti Jeruzalému a aby jemu překážku učinili.
9 Amma muka yi addu’a ga Allahnmu muka kuma sa masu tsaro da rana da kuma dare don mu magance wannan barazana.
(My pak modlili jsem se Bohu svému, a postavili jsme stráž proti nim ve dne i v noci, bojíce se jich.
10 Ana cikin haka, mutane a Yahuda suka ce, “Ƙarfin ma’aikata yana kāsawa, akwai kuma sauran tarkace da yawa da ba za mu iya sāke gina katangar ba.”
Nebo řekli Judští: Zemdlelať jest síla nosičů, a rumu ještě mnoho jest, neodolaliť bychom jim, stavějíce zed.)
11 Abokan gābanmu sun ce, “Ba za su sani ba, ba kuwa za su gan mu ba, sai dai kawai su gan mu a cikinsu, za mu karkashe su, mu tsai da aikin.”
Anobrž i řekli nepřátelé naši: Nezvědíť, ani spatří, až vpadneme mezi ně, a pomordujeme je, aneb zastavíme to dílo.
12 Sau da yawa Yahudawan da suke da zama kusa da abokan gābanmu sun yi ta zuwa suna yin mana magana, suna cewa “Ko’ina muka juya, za su fāɗa mana.”
Když pak přišli Židé, kteříž s nimi bydlili, a pravili nám na desetkrát: Mějte pozor na všecka místa, kudyž se chodí k nám:
13 Saboda haka na sa jama’a su ja ɗamara bisa ga iyalinsu a bayan katanga, a wuraren da ba a gina ba. Suna riƙe da takuba, da māsu, da bakkuna.
Tedy postavil jsem na dolních místech za zdí, i na místech příkrých, a osadil jsem lidem po čeledech s meči, s kopími a lučišti jejich.
14 Bayan na dudduba abubuwa, sai na miƙe tsaye na ce wa manyan gari da shugabanni da kuma sauran jama’a, “Kada ku ji tsoronsu. Ku tuna da Ubangiji, wanda yake mai girma da banrazana, ku yi yaƙi don’yan’uwanku, da’ya’yanku maza da mata, da matanku da kuma gidajenku.”
A když jsem to spatřil, vstana, řekl jsem k přednějším a knížatům i k jinému lidu: Nebojte se jich, ale na Pána velikého a hrozného pamatujte, a bojujte za bratří své, za syny své a dcery své, za manželky své a domy své.
15 Da abokan gābanmu suka ji muna sane da shirinsu, Allah kuma ya wargaje shirin nan, sai duk muka dawo ga katangar, kowa ya kama aikinsa.
I stalo se, když uslyšeli nepřátelé naši, že jest nám to oznámeno, tožť Bůh rozptýlil radu jejich, a my navrátili jsme se všickni ke zdem, každý k dílu svému.
16 Daga wannan rana zuwa gaba, rabin mutane suka yi aiki, yayinda sauran rabin suka kintsa da māsu, da garkuwa, da bakkuna da makamai. Shugabanni suka goyi bayan dukan mutanen Yahuda
Ale však od toho dne polovice služebníků mých dělali, a polovice jich držela kopí, pavézy a lučiště, a pancíře, a knížata stála za vší čeledí Judskou.
17 waɗanda suke ginin katanga. Waɗanda suke ɗaukan kaya suka yi aikinsu da hannu ɗaya, suna kuma riƙe da makami a ɗaya hannun,
Ti také, kteříž dělali na zdi, i nosiči břemen, i nakladači, každý jednou rukou dělal, a v druhé držel braň.
18 kuma kowane mai gini ya ɗaura takobinsa a gefe yayinda yake aiki. Amma mutum mai busa ƙaho ya kasance tare da ni.
Z těch pak, kteříž stavěli, měl jeden každý meč svůj připásaný na bedrách svých, a tak stavěli, a trubač stál podlé mne.
19 Sai na ce wa manyan gari, da shugabanni, da sauran jama’a, “Aikin nan babba ne kuma mai yawa, ga shi muna a rarrabe nesa da juna a katangar.
Nebo jsem řekl k přednějším a knížatům i k jinému lidu: Dílo veliké a široké jest, a my porůznu jsme na zdi, podál jeden od druhého.
20 Duk inda kuka ji an busa ƙaho, sai ku taru a wurin. Allahnmu zai yi yaƙi dominmu!”
Na kterém byste koli místě uslyšeli hlas trouby, tu se shromažďte k nám. Bůh náš bude bojovati za nás.
21 Saboda haka muka ci gaba da aiki, rabin mutane suna riƙe da māsu, daga wayewar gari har zuwa fitowar taurari.
A tak my dělali jsme dílo, a polovice jich držela kopí od svitání až do soumraku.
22 A wannan lokaci na kuma ce wa mutane, “A sa kowane mutum da mataimakinsa su zauna a Urushalima da dare, domin a yi tsaro da dare, da safe kuma a kama aiki.”
Tehdáž také řekl jsem lidu: Každý s služebníkem svým nocuj u prostřed Jeruzaléma, ať je máme k stráži v noci, a ve dne k dílu.
23 Saboda haka ni, da’yan’uwana, da bayina, da matsaran da suke tare da ni, ba wanda ya tuɓe tufafinsa; kowa ya rataye makaminsa, ko ya je shan ruwa ma.
Pročež i já, i bratří moji, i služebníci moji, i strážní, kteříž chodí za mnou, nebudeme svláčeti oděvu svého. Žádný ho nesloží, leč u vody.

< Nehemiya 4 >