< Nehemiya 3 >

1 Eliyashib babban firist da’yan’uwansa firistoci suka tashi suka sāke gina Ƙofar Tumaki. Suka tsarkake ta, suka sa ƙofofinta a wurarensu, suka yi ginin har Hasumiyar Ɗari, wadda suka tsarkake, da kuma Hasumiyar Hananel.
Eliasib, el sumo sacerdote, y otros sacerdotes con él, comenzaron a reconstruir la Puerta de las Ovejas. La dedicaron y colocaron sus puertas. Luego siguieron construyendo hasta la Torre de los Cien y la Torre de Hananel y la dedicaron.
2 Mutanen Yeriko kuwa suka kama ginin daga mahaɗin, Zakkur ɗan Imri kuma ya fara ginin biye da su.
Los hombres de Jericó construyeron la parte contigua a Eliasib, y Zacur, hijo de Imri, construyó la siguiente.
3 ’Ya’yan Hassenaya ne suka gina Ƙofar Kifi. Suka kafa ginshiƙan, suka kuma sa ƙofofinta, da sakatunta, da kuma sandunan ƙarfenta a wurarensu.
La Puerta del Pescado fue reconstruida por los hijos de Senaa. Colocaron sus vigas y levantaron sus puertas, junto con sus cerrojos y barras.
4 Kusa da su kuma, Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz ne ya yi gyare-gyaren. Biye da shi kuma sai Meshullam ɗan Berekiya, ɗan Meshezabel ya yi gyare-gyare. Kusa da shi Zadok ɗan Ba’ana shi ma ya yi gyare-gyare.
La siguiente sección fue reparada por Meremot, hijo de Urías, hijo de Cos; junto a él, estaba Mesulam, hijo de Berequías, hijo de Mesezabeel; y junto a él, Sadoc, hijo de Baana.
5 Mutanen Tekowa ne suka yi gyare-gyare biye da shi, amma manyan garinsu suka ƙi su sa hannu cikin aikin da shugabanninsu suka bayar.
A continuación estaban los tecoítas, pero sus nobles se negaron a realizar trabajos manuales bajo un supervisor.
6 Yohiyada ɗan Faseya, da Meshullam ɗan Besodehiya ne suka gyara Ƙofar Yeshana. Suka kafa katakanta, suka sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta.
La Puerta Vieja fue reparada por Joiada, hijo de Paseah, y Mesulam, hijo de Besodías. Colocaron sus vigas y levantaron sus puertas, junto con sus cerrojos y barras.
7 Biye da su, mutanen Gibeyon da Mizfa Melatiya na Gibeyon da Yadon Meronot waɗanda suke ƙarƙashin ikon gwamnan Kewayen Kogin Yuferites ne suka yi gyare-gyaren.
Luego fueron Melatiá el gabaonita, Jadón el meronita y los hombres de Gabaón y Mizpa, que estaban bajo la jurisdicción del gobernador de la provincia al oeste del Éufrates.
8 Uzziyel ɗan Harhahiya, ɗaya daga cikin masu ƙeran zinariya ne ya yi gyare-gyaren sashe na biye; sai Hananiya, ɗaya daga cikin masu yin turare, ya yi gyare-gyaren biye da wannan. Suka gyara Urushalima har zuwa Katanga Mai Faɗi.
A continuación estaba Uziel, hijo de Harhaiah, uno de los orfebres; y junto a él, Hananías, hijo del perfumista. Ellos reforzaron Jerusalén hasta el Muro Ancho.
9 Refahiya ɗan Hur, mai mulkin rabin yankin Urushalima, ya yi gyare-gyaren sashe na biye.
El siguiente fue Refaías, hijo de Hur, gobernante de la mitad de Jerusalén.
10 Kusa da Refahiya, Yedahiya ɗan Harumaf ya yi gyare-gyaren daga gaban gidansa, sai Hattush ɗan Hashabnehiya ya yi gyare-gyaren biye da shi.
El siguiente fue Jedaías, hijo de Harumap, que hizo reparaciones frente a su casa. El siguiente fue Hattush, hijo de Hasabneías.
11 Malkiya ɗan Harim, da Hasshub ɗan Fahat-Mowab ya yi gyare-gyaren wani sashe da kuma Hasumiyar Wurin Gashi.
Malquías, hijo de Harim, y Hasub, hijo de Pahat-moab, trabajaron en otra sección, así como en la Torre de los Hornos.
12 Shallum ɗan Hallohesh, mai mulkin ɗayan rabin yankin Urushalima ya yi gyare-gyaren sashe na biye tare da taimakon’ya’yansa mata.
A continuación fue Salum, hijo de Halohes, gobernante de un medio distrito de Jerusalén, ayudado por sus hijas.
13 Hanun da mazaunan Zanowa ne suka gyara Ƙofar Kwari. Suka sāke gina ta suka sa ƙofofinta, da sakatunta, da sandunan ƙarfenta a wurarensu. Suka kuma gyara yadi ɗari biyar na katangar har zuwa Ƙofar Juji.
La Puerta del Valle fue reparada por Hanún y la gente que vivía en Zanoa. La reconstruyeron, colocaron sus puertas, junto con sus cerrojos y barras, y repararon mil codos de la muralla hasta la Puerta del Desecho.
14 Malkiya ɗan Rekab mai mulkin yankin Bet-Hakkerem ne ya yi gyare-gyaren Ƙofar Juji. Ya sāke gina ta ya kuma sa sakatunta, da sanduna ƙarfenta a wurarensu.
Malquías, hijo de Recab, jefe del distrito de Bet-haquerem, reparó la Puerta de la Basura, la reconstruyó y colocó sus puertas, junto con sus cerrojos y barras.
15 Shallum ɗan Kol-Hoze mai mulkin Mizfa ne ya yi gyare-gyaren Ƙofar Maɓuɓɓuga. Ya sāke gina ta, ya yi mata jinƙa yana sa ƙofofinta, da sakatunta, da kuma sandunan ƙarfenta a wurarensu. Ya kuma gyara katangar tafkin Silowam, ta Lambun Sarki, har zuwa matakalan da suka gangara daga Birnin Dawuda.
La Puerta de la Fuente fue reparada por Salún, hijo de Col-hoze, jefe del distrito de Mizpa. La reconstruyó, le puso un techo y levantó sus puertas, junto con sus cerrojos y barras. Reconstruyó el muro del estanque de Selá, junto al jardín del rey, hasta las escaleras que bajan de la ciudad de David.
16 Gaba da shi, Nehemiya ɗan Azbuk, mai mulkin rabin yankin Bet-Zur ne ya yi gyare-gyaren har zuwa kusa da kaburburan Dawuda, har zuwa haƙaƙƙen tafki da kuma Gidan Jarumawa.
Después de él, Nehemías, hijo de Azbuk, gobernante de un semidistrito de Bet-Zur, reparó hasta un punto frente al cementerio de David, hasta el estanque artificial y la Casa de los Guerreros Poderosos.
17 Biye da shi, Lawiyawa a ƙarƙashin Rehum ɗan Bani ne suka yi gyare-gyaren. Kusa da su, Hashabiya mai mulkin rabin yankin Keyila ne ya yi gyare-gyaren don yankinsa.
A continuación estaban los levitas bajo el mando de Rehum hijo de Bani, y a continuación estaba Hasabías, gobernante de la mitad de la región de Keila, que hizo las reparaciones en nombre de su distrito.
18 Biye da shi,’yan’uwansu Lawiyawa ne a ƙarƙashin Binnuyi ɗan Henadad, mai mulkin ɗayan rabin yankin Keyila suka yi gyare-gyaren.
Junto a ellos estaban sus vecinos bajo Binui, hijo de Henadad, gobernante de la otra mitad de la región de Keila.
19 Biye da su, Ezer ɗan Yeshuwa, mai mulkin Mizfa, ya yi gyara wani sashe, daga inda yake fuskantar hawan gidan makamai har zuwa kusurwa.
El siguiente fue Ezer, hijo de Jesúa, gobernante de Mizpa, quien reparó otra sección frente a la Colina de la Armería, donde la muralla gira.
20 Biye da shi, Baruk ɗan Zakkai da ƙwazo ya gyara wani sashe, daga kusurwa zuwa mashigin gidan Eliyashib babban firist.
El siguiente fue Baruc, hijo de Zabai, que trabajó duro reparando otra sección, desde donde la muralla gira hasta la entrada de la casa del sumo sacerdote Eliasib.
21 Biye da shi, Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz, ya yi gyaran wani sashe, daga mashigin gidan Eliyashib zuwa ƙarshensa.
A continuación, Meremot, hijo de Urías, ton de Cos, que reparó otro tramo, desde la entrada de la casa del sumo sacerdote Eliasib hasta el final.
22 Firistoci daga kewayen yankin ne suka yi gyare-gyaren biye da shi.
A continuación, los sacerdotes de los alrededores hicieron las reparaciones.
23 Can gaba da su, Benyamin da Hasshub ne suka yi gyare-gyaren a gaban gidansu, biye da su kuwa, Azariya ɗan Ma’asehiya, ɗan Ananiya ne ya yi gyare-gyaren kusa da gidansa.
Después de ellos estaban Benjamín y Jasub, que hicieron reparaciones frente a su casa, y junto a ellos, Azarías, hijo de Maasías, hijo de Ananías, hizo reparaciones junto a su casa.
24 Biye da shi, Binnuyi ɗan Henadad ya yi gyaran wani sashe, daga gidan Azariya zuwa kusurwa,
El siguiente fue Binui, hijo de Henadad, que reparó otra parte, desde la casa de Azarías hasta donde gira el muro y la esquina.
25 sai Falal ɗan Uzai ya yi aiki ɗaura da kusurwa da kuma doguwar hasumiya daga fadar da take bisa kusa da shirayin masu tsaro. Biye da shi, Fedahiya ɗan Farosh
Palal, hijo de Uzai, trabajó frente a donde gira el muro y la torre que se extiende desde el palacio superior, cerca del patio de la guardia. Luego estaban Pedaías, hijo de Paros
26 da masu hidimar haikali da suke zama a tudun Ofel ne suka yi gyare-gyaren har zuwa wani wuri ɗaura da Ƙofar Ruwa wajen gabas da kuma doguwar hasumiya.
y los servidores del Templo que vivían en la colina de Ofel, quienes hacían reparaciones frente a la Puerta del Agua hacia el este y la torre que se extiende.
27 Biye da su, mutanen Tekowa suka yi gyaran wani sashe, daga babbar doguwar hasumiya zuwa katangar Ofel.
A continuación estaban los tecoítas que repararon en otra sección frente a la gran torre que se extiende hasta la muralla de Ofel.
28 Daga Ƙofar Doki, firistoci ne suka yi gyare-gyaren, kowanne a gaban gidansa.
Encima de la Puerta de los Caballos, cada uno de los sacerdotes hizo reparaciones frente a su propia casa.
29 Biye da su, Zadok ɗan Immer ya yi gyare-gyaren ɗaura da gidansa. Biye da shi, Shemahiya ɗan Shekaniya, mai tsaron Ƙofar Gabas ya yi gyare-gyare.
El siguiente era Sadoc, hijo de Imer, que trabajaba frente a su casa, y el siguiente era Semaías, hijo de Secanías, el guardia de la Puerta Oriental.
30 Biye da shi, Hananiya ɗan Shelemiya, da Hanun, ɗa na shida na Zalaf, suka gyara wani sashe. Biye da su, Meshullam ɗan Berekiya ya yi gyare-gyaren ɗaura da wurin zamansa.
A continuación estaban Hananías, hijo de Selemías, y Hanún, sexto hijo de Zalaf, que se encargaba de la reparación. El siguiente fue Mesulam, hijo de Berequías, que hizo reparaciones frente a donde él vivía.
31 Biye da shi, Malkiya, ɗaya daga cikin masu ƙera zinariya ya yi gyare-gyaren har zuwa gidan masu hidimar haikali da kuma’yan kasuwa, ɗaura da Ƙofar Bincike, har zuwa ɗakin da yake bisa kusurwar.
El siguiente fue Malquías, uno de los orfebres, que hizo reparaciones hasta la casa de los sirvientes del Templo y de los mercaderes, frente a la Puerta de Inspección, y hasta la sala que está sobre la esquina.
32 Maƙeran zinariya da’yan kasuwa suka gyara wani sashi tsakanin ɗakin da yake bisa kusurwa da Ƙofar Tumaki.
Los orfebres y los mercaderes hicieron reparaciones entre la sala que está sobre la esquina y la Puerta de las Ovejas.

< Nehemiya 3 >