< Nehemiya 3 >
1 Eliyashib babban firist da’yan’uwansa firistoci suka tashi suka sāke gina Ƙofar Tumaki. Suka tsarkake ta, suka sa ƙofofinta a wurarensu, suka yi ginin har Hasumiyar Ɗari, wadda suka tsarkake, da kuma Hasumiyar Hananel.
Kwasekusukuma eEliyashibi umpristi omkhulu labafowabo abapristi, bakha isango lezimvu, balingcwelisa, bamisa izivalo zalo; ngitsho, kuze kube semphotshongweni weMeya bawungcwelisa, kuze kube semphotshongweni weHananeli.
2 Mutanen Yeriko kuwa suka kama ginin daga mahaɗin, Zakkur ɗan Imri kuma ya fara ginin biye da su.
Leceleni kwakhe kwakha amadoda eJeriko; leceleni kwakhe kwakha uZakuri indodana kaImri.
3 ’Ya’yan Hassenaya ne suka gina Ƙofar Kifi. Suka kafa ginshiƙan, suka kuma sa ƙofofinta, da sakatunta, da kuma sandunan ƙarfenta a wurarensu.
Lesango lenhlanzi alakha amadodana kaHasenaya; amisa imigubazi yalo, amisa izivalo zalo, amabhawudo alo, leminxibo yalo.
4 Kusa da su kuma, Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz ne ya yi gyare-gyaren. Biye da shi kuma sai Meshullam ɗan Berekiya, ɗan Meshezabel ya yi gyare-gyare. Kusa da shi Zadok ɗan Ba’ana shi ma ya yi gyare-gyare.
Leceleni kwawo kwalungisa uMeremothi indodana kaUriya indodana kaHakozi; leceleni kwabo kwalungisa uMeshulamu indodana kaBerekiya indodana kaMeshezabeli; leceleni kwabo kwalungisa uZadoki indodana kaBahana;
5 Mutanen Tekowa ne suka yi gyare-gyare biye da shi, amma manyan garinsu suka ƙi su sa hannu cikin aikin da shugabanninsu suka bayar.
leceleni kwabo kwalungisa amaThekhowa; kodwa izikhulu zabo kazilethanga intamo yazo emsebenzini weNkosi yazo.
6 Yohiyada ɗan Faseya, da Meshullam ɗan Besodehiya ne suka gyara Ƙofar Yeshana. Suka kafa katakanta, suka sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta.
Lesango elidala balilungisa oJoyada indodana kaPhaseya loMeshulamu indodana kaBesodeya; bamisa imigubazi yalo, bamisa izivalo zalo, lamabhawudo alo, leminxibo yalo.
7 Biye da su, mutanen Gibeyon da Mizfa Melatiya na Gibeyon da Yadon Meronot waɗanda suke ƙarƙashin ikon gwamnan Kewayen Kogin Yuferites ne suka yi gyare-gyaren.
Eceleni kwabo-ke kwalungisa uMelatiya umGibeyoni loJadoni umMeronothi, amadoda eGibeyoni laweMizipa, kuze kube sesihlalweni sobukhosi sombusi wanganeno komfula.
8 Uzziyel ɗan Harhahiya, ɗaya daga cikin masu ƙeran zinariya ne ya yi gyare-gyaren sashe na biye; sai Hananiya, ɗaya daga cikin masu yin turare, ya yi gyare-gyaren biye da wannan. Suka gyara Urushalima har zuwa Katanga Mai Faɗi.
Eceleni kwakhe kwalungisa uUziyeli indodana kaHarihaya, wabakhandi begolide; leceleni kwakhe kwalungisa uHananiya, indodana yabenzi bamakha; batshiya iJerusalema kwaze kwaba semdulini obanzi.
9 Refahiya ɗan Hur, mai mulkin rabin yankin Urushalima, ya yi gyare-gyaren sashe na biye.
Eceleni kwabo-ke kwalungisa uRefaya indodana kaHuri, umbusi wengxenye yesigaba seJerusalema.
10 Kusa da Refahiya, Yedahiya ɗan Harumaf ya yi gyare-gyaren daga gaban gidansa, sai Hattush ɗan Hashabnehiya ya yi gyare-gyaren biye da shi.
Eceleni kwabo-ke kwalungisa uJedaya indodana kaHarumafi lamaqondana lendlu yakhe; leceleni kwakhe kwalungisa uHathushi indodana kaHashabineya.
11 Malkiya ɗan Harim, da Hasshub ɗan Fahat-Mowab ya yi gyare-gyaren wani sashe da kuma Hasumiyar Wurin Gashi.
Isilinganiso sesibili basilungisa oMalikiya indodana kaHarimi loHashubi indodana kaPahathi-Mowabi, kanye lomphotshongo wezithando zomlilo.
12 Shallum ɗan Hallohesh, mai mulkin ɗayan rabin yankin Urushalima ya yi gyare-gyaren sashe na biye tare da taimakon’ya’yansa mata.
Leceleni kwakhe kwalungisa uShaluma indodana kaHaloheshi, umbusi wengxenye yesigaba seJerusalema, yena lamadodakazi akhe.
13 Hanun da mazaunan Zanowa ne suka gyara Ƙofar Kwari. Suka sāke gina ta suka sa ƙofofinta, da sakatunta, da sandunan ƙarfenta a wurarensu. Suka kuma gyara yadi ɗari biyar na katangar har zuwa Ƙofar Juji.
Isango lesigodi walilungisa uHanuni labahlali beHanowa; balakha, bamisa izivalo zalo, amabhawudo alo, leminxibo yalo, lezingalo eziyinkulungwane emdulini kwaze kwaba sesangweni lomquba.
14 Malkiya ɗan Rekab mai mulkin yankin Bet-Hakkerem ne ya yi gyare-gyaren Ƙofar Juji. Ya sāke gina ta ya kuma sa sakatunta, da sanduna ƙarfenta a wurarensu.
Lesango lomquba walilungisa uMalikiya indodana kaRekabi, umbusi wesabelo seBhethi-Hakerema; walakha, wamisa izivalo zalo, amabhawudo alo, leminxibo yalo.
15 Shallum ɗan Kol-Hoze mai mulkin Mizfa ne ya yi gyare-gyaren Ƙofar Maɓuɓɓuga. Ya sāke gina ta, ya yi mata jinƙa yana sa ƙofofinta, da sakatunta, da kuma sandunan ƙarfenta a wurarensu. Ya kuma gyara katangar tafkin Silowam, ta Lambun Sarki, har zuwa matakalan da suka gangara daga Birnin Dawuda.
Lesango lomthombo walilungisa uShaluna indodana kaKolihoze, umbusi wesigaba seMizipa; yena walakha, walifulela, wamisa izivalo zalo, amabhawudo alo, leminxibo yalo, lomduli wechibi leShela ngasesivandeni senkosi, njalo kwaze kwaba sezikhwelweni ezehla zisuka emzini kaDavida.
16 Gaba da shi, Nehemiya ɗan Azbuk, mai mulkin rabin yankin Bet-Zur ne ya yi gyare-gyaren har zuwa kusa da kaburburan Dawuda, har zuwa haƙaƙƙen tafki da kuma Gidan Jarumawa.
Ngemva kwakhe kwalungisa uNehemiya indodana kaAzibuki, umbusi wengxenye yesigaba seBeti-Zuri, kwaze kwaba maqondana lamangcwaba kaDavida, njalo kwaze kwaba sechibini elalenziwe, njalo kwaze kwaba sendlini yamaqhawe.
17 Biye da shi, Lawiyawa a ƙarƙashin Rehum ɗan Bani ne suka yi gyare-gyaren. Kusa da su, Hashabiya mai mulkin rabin yankin Keyila ne ya yi gyare-gyaren don yankinsa.
Ngemva kwakhe kwalungisa amaLevi, uRehuma indodana kaBani; leceleni kwakhe kwalungisa uHashabhiya, umbusi wengxenye yesigaba seKeyila, esigabeni sakhe.
18 Biye da shi,’yan’uwansu Lawiyawa ne a ƙarƙashin Binnuyi ɗan Henadad, mai mulkin ɗayan rabin yankin Keyila suka yi gyare-gyaren.
Ngemva kwakhe kwalungisa abafowabo, uBavayi indodana kaHenadadi, umbusi wengxenye yesigaba seKeyila.
19 Biye da su, Ezer ɗan Yeshuwa, mai mulkin Mizfa, ya yi gyara wani sashe, daga inda yake fuskantar hawan gidan makamai har zuwa kusurwa.
Njalo kwalungisa eceleni kwakhe uEzeri indodana kaJeshuwa, umbusi weMizipa, esinye isilinganiso maqondana lomqanso wendlu yezikhali, engonsini.
20 Biye da shi, Baruk ɗan Zakkai da ƙwazo ya gyara wani sashe, daga kusurwa zuwa mashigin gidan Eliyashib babban firist.
Ngemva kwakhe kwalungisa ngesivuvu uBharukhi indodana kaZabayi esinye isilinganiso kusukela engonsini kusiya emnyango wendlu kaEliyashibi umpristi omkhulu.
21 Biye da shi, Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz, ya yi gyaran wani sashe, daga mashigin gidan Eliyashib zuwa ƙarshensa.
Ngemva kwakhe uMeremothi indodana kaUriya indodana kaHakozi walungisa esinye isilinganiso kusukela emnyango wendlu kaEliyashibi kuze kube sekucineni kwendlu kaEliyashibi.
22 Firistoci daga kewayen yankin ne suka yi gyare-gyaren biye da shi.
Langemva kwakhe kwalungisa abapristi, amadoda endawo ezigombolozeleyo.
23 Can gaba da su, Benyamin da Hasshub ne suka yi gyare-gyaren a gaban gidansu, biye da su kuwa, Azariya ɗan Ma’asehiya, ɗan Ananiya ne ya yi gyare-gyaren kusa da gidansa.
Ngemva kwakhe kwalungisa oBhenjamini loHashubi maqondana lendlu yabo; ngemva kwakhe kwalungisa uAzariya indodana kaMahaseya indodana kaAnaniya duze lendlu yakhe.
24 Biye da shi, Binnuyi ɗan Henadad ya yi gyaran wani sashe, daga gidan Azariya zuwa kusurwa,
Ngemva kwakhe uBinuwi indodana kaHenadadi walungisa esinye isilinganiso kusukela endlini kaAzariya kusiya engonsini njalo kuze kube sejikweni.
25 sai Falal ɗan Uzai ya yi aiki ɗaura da kusurwa da kuma doguwar hasumiya daga fadar da take bisa kusa da shirayin masu tsaro. Biye da shi, Fedahiya ɗan Farosh
UPalali indodana kaUzayi, maqondana lengonsi lomphotshongo othutsha endlini yenkosi ephezulu esegumeni labalindi. Ngemva kwakhe uPhedaya indodana kaParoshi.
26 da masu hidimar haikali da suke zama a tudun Ofel ne suka yi gyare-gyaren har zuwa wani wuri ɗaura da Ƙofar Ruwa wajen gabas da kuma doguwar hasumiya.
AmaNethini ayehlezi eOfeli kwaze kwaba maqondana lesango lamanzi ngasempumalanga lomphotshongo othutshayo.
27 Biye da su, mutanen Tekowa suka yi gyaran wani sashe, daga babbar doguwar hasumiya zuwa katangar Ofel.
Ngemva kwakhe abeThekhowa balungisa esinye isilinganiso maqondana lomphotshongo omkhulu othutshayo, njalo kwaze kwaba semdulini weOfeli.
28 Daga Ƙofar Doki, firistoci ne suka yi gyare-gyaren, kowanne a gaban gidansa.
Kusukela phezu kwesango lamabhiza kwalungisa abapristi, ngulowo maqondana lendlu yakhe.
29 Biye da su, Zadok ɗan Immer ya yi gyare-gyaren ɗaura da gidansa. Biye da shi, Shemahiya ɗan Shekaniya, mai tsaron Ƙofar Gabas ya yi gyare-gyare.
Ngemva kwakhe kwalungisa uZadoki indodana kaImeri maqondana lendlu yakhe. Njalo ngemva kwakhe kwalungisa uShemaya indodana kaShekaniya, umgcini wesango lempumalanga.
30 Biye da shi, Hananiya ɗan Shelemiya, da Hanun, ɗa na shida na Zalaf, suka gyara wani sashe. Biye da su, Meshullam ɗan Berekiya ya yi gyare-gyaren ɗaura da wurin zamansa.
Ngemva kwakhe kwalungisa oHananiya indodana kaShelemiya loHanuni indodana yesithupha kaZalafi esinye isilinganiso. Ngemva kwakhe kwalungisa uMeshulamu indodana kaBerekiya maqondana lekamelo lakhe.
31 Biye da shi, Malkiya, ɗaya daga cikin masu ƙera zinariya ya yi gyare-gyaren har zuwa gidan masu hidimar haikali da kuma’yan kasuwa, ɗaura da Ƙofar Bincike, har zuwa ɗakin da yake bisa kusurwar.
Ngemva kwakhe kwalungisa uMalikiya indodana yomkhandi wegolide kwaze kwaba sendlini yamaNethini leyabathengi maqondana lesango leMifikhadi, njalo kusiya endlini yengonsi engaphezulu.
32 Maƙeran zinariya da’yan kasuwa suka gyara wani sashi tsakanin ɗakin da yake bisa kusurwa da Ƙofar Tumaki.
Njalo phakathi laphakathi kwendlu yengonsi engaphezulu kuze kube sesangweni lezimvu kwalungisa abakhandi begolide labathengi.