< Nehemiya 2 >

1 A watan Nisan a shekara ta ashirin ta mulkin Sarki Artazerzes, sa’ad aka kawo masa ruwan inabi, sai na karɓa na ba shi. Ban taɓa ɓata fuskata a gabansa ba, sai wannan karo.
Ngenyanga kaNisani ngomnyaka wamatshumi amabili weNkosi u-Athazekisisi, ngesikhathi ephiwa iwayini, ngalithatha iwayini ngalisa enkosini. Ngangingakaze ngivele kuyo ngidanile;
2 Saboda haka sarki ya tambaye ni ya ce, “Me ya sa fuskarka ta ɓaci, ga shi, ba ciwo kake ba? Ba abin da ya kawo wannan, in ba dai kana baƙin ciki ba.” Sai na ji tsoro ƙwarai,
ngakho inkosi yangibuza yathi, “Kungani ubuso bakho bukhanya buhlobile kanje wena ungaguli? Lokhu ngeke kube ngokunye ngaphandle kokudana okusenhliziyweni.” Ngezwa ngisesaba kakhulu,
3 na amsa na ce wa sarki, “Ran sarki yă daɗe! Me zai hana fuskata ta ɓaci, sa’ad da birnin da aka binne kakannina tana zaman kango, aka kuma rushe ƙofofinsa da wuta?”
kodwa ngathi enkosini, “Phila lanini nkosi! Ubuso bami bungayekelelani na ukuhloba njengoba idolobho lapho okulele khona okhokho selingamanxiwa nje, lamasango alo atshiswa ngomlilo na?”
4 Sai sarki ya ce mini, “Me kake so?” Sai na yi addu’a ga Allah na sama,
Inkosi yathi kimi, “Pho ufunani?” Ngasengikhuleka kuNkulunkulu wezulwini,
5 na kuwa ba wa sarki amsa, na ce, “In ya gamshi sarki, in kuma bawanka ya sami tagomashi a idonka, bari ka aike ni in tafi ƙasar Yahuda, birnin da aka binne kakannina, domin in sāke gina shi.”
yikho ngasengiyiphendula inkosi ngathi, “Aluba kungaba yikuthanda kwenkosi njalo nxa inceku yakho ifumene umusa emehlweni ayo, kayingithumele kulelodolobho elikoJuda lapho okwambelwa khona okhokho ukuze ngiyolakha kakutsha.”
6 Sai sarki, a lokacin sarauniya da tana zama kusa da shi, ya tambaye ni, ya ce, “Kwana nawa tafiyar za tă ɗauke ka, kuma yaushe za ka dawo?” Ya gamshi sarki ya aike ni; saboda haka na shirya lokaci.
Inkosi eyayihlezi lendlovukazi eceleni kwayo yangibuza yathi, “Uhambo lwakho luzathatha isikhathi esingakanani, njalo uzabuya nini?” Inkosi yathanda ukuthi ngihambe; yikho ngamisa isikhathi.
7 Na kuma ce masa, “In ya gamshi sarki, zai yi kyau in sami wasiƙu zuwa ga gwamnonin Kewayen Kogin Yuferites, domin su tanada kāriya har sai na isa Yahuda?
Ngaphinde ngathi kuyo, “Nxa kuyikuthanda kwenkosi, ngicela izincwadi ziye kubabusi bangaphetsheya kweYufrathe, ukwenzela ukuthi bangivikele ohanjweni lwami ngize ngiyefika koJuda?
8 A kuma ba ni wasiƙa zuwa ga Asaf, sarkin daji, yă ba ni katako don yin ƙofofin kagara na kusa da fadar haikali da kuma don katangar birni, da na wurin da zan zauna?” Sarki kuwa ya ba ni abin da na roƙa, gama Allah yana tare da ni.
Njalo ngicela incwadi eya ku-Asafi, umphathi wegusu lenkosi, yikho ezanginika izigodo zokwenza izinsika zamasango esigodlo eduzane lethempeli lezomduli wedolobho kanye lezendlu engizahlala kuyo.” Kwathi ngoba isandla somusa sikaNkulunkulu wami sasiphezu kwami, inkosi yazamukela izicelo zami.
9 Saboda haka na tafi wurin gwamnonin Kewayen Kogin Yuferites, na ba su wasiƙun sarki. Sarki kuma ya aika da hafsoshin mayaƙa da kuma mahayan dawakai tare da ni.
Yikho ngasengisiya kubabusi bangaphetsheya kweYufrathe ngabapha izincwadi zenkosi. Inkosi yayingiphe futhi abalawuli bebutho kanye lamabutho amabhiza ukuba bangiphelekezele.
10 Da Sanballat mutumin Horon da Tobiya wakilin ƙasar Ammon suka ji cewa wani ya zo domin yă ƙarfafa zaman lafiyar mutanen Isra’ila, sai suka damu ƙwarai.
Kwathi ukuba uSanibhalathi umHoroni loThobhiya umʼAmoni owayeyinduna bekuzwa lokhu, bakhathazeka kakhulu ukuthi ukhona owayeselande ukuzathuthukisa inhlalo yaba-Israyeli.
11 Sai na je Urushalima, bayan na zauna a can na kwanaki uku,
Ngaya eJerusalema, kwathi sengihlale khona insuku ezintathu
12 sai na fita da dare tare da mutane kalila. Ban faɗa wa wani abin da Allahna ya sa a zuciyata in yi don Urushalima ba. Ba waɗansu dabbobi kuma tare da ni, sai dai dabbar da na hau.
ngaphuma kusebusuku ngilamadoda ambalwa. Ngangingazange ngitshele muntu ngalokho uNkulunkulu wami ayekubeke enhliziyweni yami ngeJerusalema. Ngangingelanyamazana ngaphandle kwaleyo engangiyigadile.
13 Da dare na fita ta Ƙofar Kwari wajen Rijiyar Dila da Ƙofar Juji, ina dudduba katangar Urushalima waɗanda aka rushe da kuma ƙofofinta waɗanda aka ƙone da wuta.
Ebusuku ngaphuma ngeSango leSigodi ngaqonda uMthombo weKhanka leSango loBulongwe, ngihlola imiduli yeJerusalema, eyayibhidliziwe, kanye lamasango ayo ayetshiswe ngomlilo.
14 Sa’an nan na ci gaba zuwa wajen Ƙofar Maɓuɓɓuga da kuma Tafkin Sarki, amma babu isashen wuri saboda abin da na hau yă bi;
Ngaqhubeka sengiqonde eSangweni loMthombo leSiziba Senkosi, kodwa kwakungelantshukuntshu yokudlula ubabhemi wami engangimgadile;
15 saboda haka na haura ta kwarin da dad dare, ina dudduba katangar. A ƙarshe, na juya na sāke shiga ta Ƙofar Kwari.
yikho ngasengikhwela ngesigodi kusebusuku, ngihlola umduli. Ekucineni ngaphenduka ngangena ngeSango leSigodi.
16 Shugabanni ba su san inda na tafi, ko abin da nake yi ba, domin ban riga na faɗa wa Yahudawa, ko firistoci, ko manyan gari, ko shugabanni, ko sauran waɗanda za su yi aiki, kome ba.
Izinduna kazizange zikwazi ukuthi ngangiye ngaphi lokuthi ngangisenzani, ngoba ngangivele ngingakatsho lutho kubaJuda loba kubaphristi loba ezikhulwini loba ezinduneni loba lakubobani ababezakwenza umsebenzi.
17 Sai na ce musu, “Kun ga matsalar da muke ciki, yadda Urushalima ta zama kango, an kuma ƙone ƙofofinta da wuta. Ku zo mu sāke gina katangar Urushalima, ba za mu ƙara shan kunya ba.”
Ngasengisithi kubo, “Liyalubona uhlupho esiphakathi kwalo: iJerusalema selingamanxiwa nje, lamasango alo atshisiwe ngomlilo. Wozani, siwakhe kutsha umduli weJerusalema ukuze singabi silokhu sihlaziswa.”
18 Na kuma faɗa musu game da yadda alherin Allahna yake tare da ni da kuma abin da sarki ya faɗa mini. Suka amsa, suka ce, “Mu tashi, mu kama gini.” Sai suka fara wannan aiki mai kyau.
Ngaphinda ngabatshela ngesandla somusa sikaNkulunkulu wami kimi lokuthi inkosi yayitheni kimi. Baphendula bathi, “Kasiqaliseni ukwakha.” Yikho bahle bawuqalisa umsebenzi lo omuhle.
19 Amma sa’ad da Sanballat mutumin Horon da Tobiya wakilin ƙasar Ammon da kuma Geshem mutumin Arab suka ji game da wannan, sai suka yi mana ba’a suka kuma yi mana dariya. Suka ce, “Me kuke tsammani kuke yi? Kuna so ku yi wa sarki tawaye ne?”
Kodwa kwathi ukuba uSanibhalathi umHoroni, loThobhiya induna yomʼAmoni loGeshemi umArabhu bekuzwa lokho, basichithoza basihleka. Babuza bathi, “Kuyini lokhu elikwenzayo. Selihlamukele inkosi na?”
20 Na amsa musu na ce, “Allah na sama zai ba mu nasara. Mu bayinsa za mu tashi mu fara gini, amma game da ku kam, ba ku da rabo cikin Urushalima, ba ku da wani hakki ko wani abin tunawa.”
Ngabaphendula ngokuthi, “UNkulunkulu wasezulwini uzasiphumelelisa. Thina izinceku zakhe sesiqalisa ukwakha kutsha, kodwa lina, kalilasabelo eJerusalema, loba imfanelo loba lungelo bani lomdabuko wenu.”

< Nehemiya 2 >