< Nehemiya 13 >

1 A wannan rana aka karanta Littafin Musa da ƙarfi a kunnuwan mutane aka kuma sami an rubuta cewa kada a karɓi mutumin Ammon ko mutumin Mowab cikin taron Allah,
در همان روز، وقتی تورات موسی برای قوم اسرائیل خوانده می‌شد، این مطلب را در آن یافتند که عمونی‌ها و موآبی‌ها هرگز نباید وارد جماعت قوم خدا شوند.
2 domin ba su taryi Isra’ila da abinci da ruwa ba amma suka yi hayar Bala’am don yă kira la’ana a kansu. (Amma Allahnmu, ya mai da la’anar ta zama albarka.)
این دستور بدان سبب بود که آنها با نان و آب از بنی‌اسرائیل استقبال نکردند، بلکه بلعام را اجیر نمودند تا ایشان را لعنت کند، ولی خدای ما لعنت او را به برکت تبدیل کرد.
3 Sa’ad da mutane suka ji wannan doka, sai suka ware daga Isra’ila duk waɗanda suke na baƙon zuriya.
وقتی این قسمت خوانده شد، قوم اسرائیل افراد بیگانه را از جماعت خود جدا ساختند.
4 Kafin wannan, an sa Eliyashib firist yă lura da ɗakuna ajiyar gidan Allahnmu. Yana da dangantaka na kurkusa da Tobiya,
الیاشیب کاهن که انباردار انبارهای خانهٔ خدا و دوست صمیمی طوبیا بود،
5 ya kuma tanada masa babban ɗakin da dā ake ajiyar hadayun hatsi da turare da kayayyaki haikali, da kuma zakan hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai da aka umarta don Lawiyawa, mawaƙa da kuma matsaran ƙofofi, da kuma sadakoki domin firistoci.
یکی از اتاقهای بزرگ انبار را به طوبیا داده بود. این اتاق قبلاً انبار هدایای آردی، بخور، ظروف خانهٔ خدا، ده‌یک غله، شراب و روغن زیتون بود. این هدایا متعلق به لاویان، دستهٔ سرایندگان و نگهبانان بود. هدایای مخصوص کاهنان نیز در این اتاق نگهداری می‌شد.
6 Amma yayinda dukan wannan yake faruwa, ba ni a Urushalima, gama a shekara ta talatin da biyu na Artazerzes sarkin Babilon na dawo wurin sarki. A wani lokaci daga baya na nemi izininsa
در این موقع من در اورشلیم نبودم، چون در سال سی و دوم سلطنت اردشیر، پادشاه پارس، که بر بابِل حکومت می‌کرد، من نزد او رفته بودم. پس از مدتی دوباره از او اجازه خواستم تا به اورشلیم بازگردم.
7 sai na koma zuwa Urushalima. A nan na ji game da mugun abin da Eliyashib ya aikata da ya tanada wa Tobiya ɗaki a filayen gidan Allah.
وقتی به اورشلیم رسیدم و از این کار زشت الیاشیب باخبر شدم که در خانهٔ خدا برای طوبیا اتاقی فراهم کرده بود
8 Na ɓace rai ƙwarai na kuma zubar da dukan kayan gidan Tobiya daga ɗakin.
بسیار ناراحت شدم و اسباب و اثاثیه او را از اتاق بیرون ریختم.
9 Na umarta a tsarkake ɗakunan, sa’an nan na mayar da kayan gidan Allah a cikin ɗakunan, tare da hadayun hatsi da kuma turare.
سپس دستور دادم اتاق را تطهیر کنند و ظروف خانهٔ خدا، هدایای آردی و بخور را به آنجا بازگردانند.
10 Na kuma ji cewa sassan da ake ba wa Lawiyawa ba a ba su ba, cewa kuma dukan Lawiyawa da mawaƙan da suke da hakkin hidima sun koma gonakinsu.
در ضمن فهمیدم دستهٔ سرایندگان خانهٔ خدا و سایر لاویان، اورشلیم را ترک گفته و به مزرعه‌های خود بازگشته بودند، زیرا مردم سهمشان را به ایشان نمی‌دادند.
11 Sai na tsawata wa shugabanni na kuma tambaye su na ce, “Me ya sa aka ƙyale gidan Allah?” Sa’an nan na kira su gaba ɗaya na sa su a wuraren aikinsu.
پس سران قوم را توبیخ کرده، گفتم: «چرا از خانهٔ خدا غافل مانده‌اید؟» سپس تمام لاویان را جمع کرده، ایشان را دوباره در خانهٔ خدا سر خدمت گذاشتم.
12 Dukan Yahuda suka kawo zakan hatsi, sabon ruwan inabi da mai cikin ɗakunan ajiya.
سپس مردم یهودا بار دیگر ده‌یک غله، شراب و روغن زیتون خود را به انبارهای خانهٔ خدا آوردند.
13 Na sa Shelemiya firist, Zadok marubuci, da wani Balawe mai suna Fedahiya su lura da ɗakunan ajiya na kuma sa Hanan ɗan Zakkur, ɗan Mattaniya ya zama mataimakinsu, domin an ɗauka waɗannan mutane amintattu ne. Aka ba su hakkin raban kayayyaki wa’yan’uwansu.
سپس شلمیای کاهن و فدایای لاوی و صادوق را که معلم شریعت بودند مأمور نگهداری انبارها نمودم، و حانان (پسر زکور، نوه متنیا) را هم معاون ایشان تعیین کردم، زیرا همهٔ این اشخاص مورد اعتماد مردم بودند. مسئولیت ایشان تقسیم سهمیه بین لاویان بود.
14 Ka tuna da ni saboda wannan, ya Allahna, kuma kada ka shafe abin da na yi da aminci domin gidan Allahna da kuma hidimarsa.
ای خدای من، کارهای مرا به یاد آور و خدماتی را که برای خانهٔ تو کرده‌ام فراموش نکن.
15 A waɗannan kwanaki, na ga mutane a Yahuda suna matse ruwan inabi a ranar Asabbaci suna kuma kawo hatsi suna labta su a kan jakuna, tare da ruwan inabi,’ya’yan inabi, ɓaure da kaya iri-iri. Suna kuma kawowa dukan wannan cikin Urushalima a ranar Asabbaci. Saboda haka na gargaɗe su a kan sayar da abinci a wannan rana.
در آن روزها در یهودا عده‌ای را دیدم که در روز شَبّات در چرخشت، انگور له می‌کردند و عده‌ای دیگر غله و شراب و انگور و انجیر و چیزهای دیگر، بار الاغ می‌نمودند تا به اورشلیم ببرند و بفروشند. پس به ایشان اخطار کردم که در روز شَبّات این کار را نکنند.
16 Mutane daga Taya waɗanda suke zama a Urushalima suna shigar da kifi da kaya iri-iri na’yan kasuwa suna kuma sayar da su a Urushalima a ranar Asabbaci wa mutanen Yahuda.
بعضی از اهالی صور نیز که در اورشلیم ساکن بودند در روز شَبّات ماهی و کالاهای گوناگون می‌آوردند و در اورشلیم به یهودیان می‌فروختند.
17 Sai na tsawata wa manyan Yahuda na ce musu, “Wanda irin mugun abu ke nan kuke yi, kuna ƙazantar da ranar Asabbaci?
آنگاه سران یهودا را توبیخ کرده، گفتم: «این چه کار زشتی است که انجام می‌دهید؟ چرا روز شَبّات را بی‌حرمت می‌کنید؟
18 Kakanninku ba su yi irin waɗannan abubuwa ba, har Allahnmu ya kawo dukan masifun nan a kanmu da kuma a kan wannan birni? Yanzu kuna tsokanar fushi mai yawa a kan Isra’ila ta wurin ƙazantar da Asabbaci.”
آیا برای همین کار نبود که خدا اجدادتان را تنبیه کرد و این شهر را ویران نمود؟ و حال، خود شما هم شَبّات را بی‌حرمت می‌کنید و باعث می‌شوید غضب خدا بر اسرائیل شعله‌ورتر شود.»
19 Sa’ad da inuwar yamma ya fāɗo a ƙofofin Urushalima kafin Asabbaci, na umarta a rufe ƙofofi kuma kada a buɗe sai Asabbaci ya wuce. Na kafa waɗansu mutanena a ƙofofin don kada a shigo da wani kaya a ranar Asabbaci.
سپس دستور دادم دروازه‌های شهر اورشلیم را از غروب آفتاب روز جمعه ببندند و تا غروب روز شَبّات باز نکنند. چند نفر از افراد خود را فرستادم تا دم دروازه‌ها نگهبانی بدهند و نگذارند روز شَبّات چیزی برای فروش به شهر بیاورند.
20 Sau ɗaya ko biyu,’yan kasuwa da masu sayar da kowane irin kaya suka kwana waje da Urushalima.
تاجران و فروشندگان یکی دو بار، جمعه‌ها، بیرون اورشلیم، شب را به سر بردند.
21 Amma na ja kunnensu na ce, “Me ya sa kuke kwana kusa da katanga? In kuka ƙara yin haka, zan kama ku.” Daga wannan lokaci har zuwa gaba ba su ƙara zuwa a ranar Asabbaci ba.
ولی من ایشان را تهدید کرده، گفتم: «اینجا چه می‌کنید، چرا شب را پشت دیوار به سر می‌برید؟ اگر بار دیگر این کار را بکنید، متوسل به زور می‌شوم.» از آن روز به بعد، دیگر روزهای شَبّات نیامدند.
22 Sai na umarci Lawiyawa su tsarkake kansu su kuma tafi su yi tsaron ƙofofi don a kiyaye ranar Asabbaci da tsarki. Ka tuna da ni saboda wannan shi ma, ya Allahna, ka nuna mini jinƙai bisa ga madawwamiyar ƙaunarka.
سپس به لاویان دستور دادم خود را تطهیر کنند و دم دروازه‌ها نگهبانی بدهند تا تقدس روز شَبّات حفظ شود. ای خدای من، این کار مرا به یاد آور و برحسب محبت بی‌پایانت به من رحم کن.
23 Ban da haka, a waɗannan kwanakin na ga mutanen Yahuda waɗanda suka auri mata daga Ashdod, Ammon da Mowab.
در آن روزها عده‌ای از یهودیان را دیدم که از قومهای اشدودی، موآبی و عمونی برای خود زنان گرفته بودند
24 Rabin’ya’yansu suna yaren Ashdod ko kuwa wani yare na waɗansu mutane, ba su kuwa san yadda za su yi Yahudanci ba.
و نصف فرزندانشان به زبان اشدودی یا سایر زبانها صحبت می‌کردند و زبان عبری را نمی‌فهمیدند.
25 Na tsawata musu na kuma kira la’ana a kansu. Na bugi waɗansu mutane na kuma ja gashin kansu. Na sa suka yi rantsuwa da sunan Allah na ce, “Kada ku ba da’ya’yanku mata aure ga’ya’yansu maza, ba kuwa za ku auri’ya’yansu mata wa’ya’yanku maza ko wa kanku ba.
پس با والدین آنها دعوا کردم، ایشان را لعنت کردم، زدم و موی سرشان را کندم و در حضور خدا قسم دادم که نگذارند فرزندانشان با غیریهودیان ازدواج کنند.
26 Ba don aure-aure irin waɗannan ne Solomon sarkin Isra’ila ya yi zunubi ba? A cikin yawancin al’ummai babu sarki kamar sa. Allahnsa ya ƙaunace shi, Allah kuma ya mai da shi sarki a kan dukan Isra’ila, amma duk da haka baren mata suka rinjaye shi ga zunubi.
سپس گفتم: «آیا این همان گناهی نیست که سلیمان پادشاه مرتکب شد؟ سلیمان در میان پادشاهان دنیا نظیر نداشت. خدا او را دوست می‌داشت و او را پادشاه تمام اسرائیل ساخت؛ ولی با وجود این، همسران بیگانهٔ سلیمان، او را به بت‌پرستی کشانیدند!
27 Yanzu za mu ji cewa ku ma kuna yin duk wannan mugunta kuna zama marasa aminci ga Allahnmu ta wurin auren baren mata?”
حال که شما زنان بیگانه برای خود گرفته و به خدای خویش خیانت کرده‌اید، خیال می‌کنید ما این شرارت شما را تحمل خواهیم کرد؟»
28 Ɗaya daga cikin’ya’yan Yohiyada maza, ɗan Eliyashib babban firist, surukin Sanballat mutumin Horon ne. Na kuwa kore shi daga wurina.
یکی از پسران یهویاداع (پسر الیاشیب کاهن اعظم) دختر سنبلط حورونی را به زنی گرفته بود، پس مجبور شدم او را از اورشلیم بیرون کنم.
29 Ka tuna da su, ya Allahna, domin sun ƙazantar da aikin firist da kuma alkawarin aikin firist da na Lawiyawa.
ای خدای من، کارهای آنها را فراموش نکن، چون به مقام کاهنی و عهد و پیمان کاهنان و لاویان توهین کرده‌اند.
30 Saboda haka na tsarkake firistoci da Lawiyawa daga kowane baƙon abu, na kuma ba su aikinsu, kowa ga aikinsa.
پس قوم خدا را از بیگانه‌ها جدا کردم و برای کاهنان و لاویان وظیفه تعیین نمودم تا هر کس بداند چه باید بکند.
31 Na kuma yi tanadi don sadakokin itace a ƙayyadaddun lokuta, da kuma don nunan fari. Ka tuna da ni da alheri, ya Allahna.
ترتیبی دادم تا به موقع برای مذبح هیزم بیاورند و نوبر محصولات را جمع‌آوری کنند. ای خدای من، مرا به یاد آور و برکت ده.

< Nehemiya 13 >