< Nehemiya 13 >
1 A wannan rana aka karanta Littafin Musa da ƙarfi a kunnuwan mutane aka kuma sami an rubuta cewa kada a karɓi mutumin Ammon ko mutumin Mowab cikin taron Allah,
Paa den samme Dag blev læst i Mose Bog for Folkets Øren; og der blev fundet skrevet i den, at en Ammonit og Moabit maatte ikke komme i Guds Forsamling indtil evig Tid,
2 domin ba su taryi Isra’ila da abinci da ruwa ba amma suka yi hayar Bala’am don yă kira la’ana a kansu. (Amma Allahnmu, ya mai da la’anar ta zama albarka.)
fordi de ikke kom Israels Børn i Møde med Brød og med Vand, men lejede Bileam imod dem til at forbande dem, enddog vor Gud vendte den Forbandelse til en Velsignelse.
3 Sa’ad da mutane suka ji wannan doka, sai suka ware daga Isra’ila duk waɗanda suke na baƙon zuriya.
Og det skete, der de hørte Loven, da fraskilte de alle de fremmede fra Israel.
4 Kafin wannan, an sa Eliyashib firist yă lura da ɗakuna ajiyar gidan Allahnmu. Yana da dangantaka na kurkusa da Tobiya,
Og Eliasib, Præsten, som var sat over vor Guds Hus's Kamre, var tilforn bleven nær besvogret med Tobia.
5 ya kuma tanada masa babban ɗakin da dā ake ajiyar hadayun hatsi da turare da kayayyaki haikali, da kuma zakan hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai da aka umarta don Lawiyawa, mawaƙa da kuma matsaran ƙofofi, da kuma sadakoki domin firistoci.
Og han gjorde ham et stort Kammer, hvor de tilforn lagde Madofferet, Virakken og Karrene og Tienden af Kornet, Mosten og Olien, som var befalet at give Leviterne og Sangerne og Portnerne, og Afgiften til Præsterne.
6 Amma yayinda dukan wannan yake faruwa, ba ni a Urushalima, gama a shekara ta talatin da biyu na Artazerzes sarkin Babilon na dawo wurin sarki. A wani lokaci daga baya na nemi izininsa
Men under alt dette var jeg ikke i Jerusalem; thi i Artakserkses's, Kongen af Babels, to og tredivte Aar, kom jeg til Kongen, og efter at et Aars Tid var til Ende, begærede jeg igen Orlov af Kongen.
7 sai na koma zuwa Urushalima. A nan na ji game da mugun abin da Eliyashib ya aikata da ya tanada wa Tobiya ɗaki a filayen gidan Allah.
Og jeg kom til Jerusalem, og jeg lagde Mærke til det onde, som Eliasib havde gjort for Tobias Skyld, at han havde gjort ham et Kammer i Guds Hus's Forgaarde.
8 Na ɓace rai ƙwarai na kuma zubar da dukan kayan gidan Tobiya daga ɗakin.
Og det gjorde mig meget ondt, og jeg kastede alt Tobias Bohave ud af Kammeret.
9 Na umarta a tsarkake ɗakunan, sa’an nan na mayar da kayan gidan Allah a cikin ɗakunan, tare da hadayun hatsi da kuma turare.
Og jeg bød, saa rensede de Kamrene, og jeg bragte igen Guds Hus's Kar, Madofferet og Virakken derhen.
10 Na kuma ji cewa sassan da ake ba wa Lawiyawa ba a ba su ba, cewa kuma dukan Lawiyawa da mawaƙan da suke da hakkin hidima sun koma gonakinsu.
Og jeg fik at vide, at Afgiften til Leviterne ikke blev dem given, saa at Leviterne og Sangerne, som skulde gøre Gerningen, vare bortflyede, hver til sin Ager.
11 Sai na tsawata wa shugabanni na kuma tambaye su na ce, “Me ya sa aka ƙyale gidan Allah?” Sa’an nan na kira su gaba ɗaya na sa su a wuraren aikinsu.
Da trættede jeg med Forstanderne og sagde: Hvorfor er Guds Hus forladt? Og jeg samlede dem og beskikkede dem paa deres Sted.
12 Dukan Yahuda suka kawo zakan hatsi, sabon ruwan inabi da mai cikin ɗakunan ajiya.
Da bragte al Juda Tiende af Kornet og Mosten og Olien til Forraadshusene.
13 Na sa Shelemiya firist, Zadok marubuci, da wani Balawe mai suna Fedahiya su lura da ɗakunan ajiya na kuma sa Hanan ɗan Zakkur, ɗan Mattaniya ya zama mataimakinsu, domin an ɗauka waɗannan mutane amintattu ne. Aka ba su hakkin raban kayayyaki wa’yan’uwansu.
Og jeg satte til Skatgemmere over Forraadshusene Selemia, Præsten, og Zadok, Skriveren, og Pedaja af Leviterne, og for at gaa dem til Haande Hanan, en Søn af Sakur, der var en Søn af Matthanja; thi de vare ansete for tro, og dem paalaa det at dele ud til deres Brødre.
14 Ka tuna da ni saboda wannan, ya Allahna, kuma kada ka shafe abin da na yi da aminci domin gidan Allahna da kuma hidimarsa.
Min Gud! kom mig i Hu for dette, og udslet ikke mine Kærlighedsgerninger, som jeg har gjort imod min Guds Hus og i hans Tjeneste!
15 A waɗannan kwanaki, na ga mutane a Yahuda suna matse ruwan inabi a ranar Asabbaci suna kuma kawo hatsi suna labta su a kan jakuna, tare da ruwan inabi,’ya’yan inabi, ɓaure da kaya iri-iri. Suna kuma kawowa dukan wannan cikin Urushalima a ranar Asabbaci. Saboda haka na gargaɗe su a kan sayar da abinci a wannan rana.
I de samme Dage saa jeg i Juda dem, som traadte Vinperser om Sabbaten og førte Neg ind og lagde dem paa Asener, ja og Vin, Druer og Figen og alle Haande Byrder og førte det til Jerusalem paa Sabbatens Dag, og jeg vidnede imod dem, paa den Dag, de solgte Spise.
16 Mutane daga Taya waɗanda suke zama a Urushalima suna shigar da kifi da kaya iri-iri na’yan kasuwa suna kuma sayar da su a Urushalima a ranar Asabbaci wa mutanen Yahuda.
I den boede og nogle Tyrier, som førte Fisk og alle Haande Varer ind, og de solgte dem paa Sabbaten til Judas Børn og i Jerusalem.
17 Sai na tsawata wa manyan Yahuda na ce musu, “Wanda irin mugun abu ke nan kuke yi, kuna ƙazantar da ranar Asabbaci?
Da trættede jeg med de ypperste i Juda, og jeg sagde til dem: Hvad er dette for en ond Ting, som I gøre, at vanhellige Sabbatens Dag?
18 Kakanninku ba su yi irin waɗannan abubuwa ba, har Allahnmu ya kawo dukan masifun nan a kanmu da kuma a kan wannan birni? Yanzu kuna tsokanar fushi mai yawa a kan Isra’ila ta wurin ƙazantar da Asabbaci.”
Gjorde ej eders Fædre saa, og vor Gud førte al denne Ulykke over os og over denne Stad? Og I føre mere Vrede over Israel ved at vanhellige Sabbaten.
19 Sa’ad da inuwar yamma ya fāɗo a ƙofofin Urushalima kafin Asabbaci, na umarta a rufe ƙofofi kuma kada a buɗe sai Asabbaci ya wuce. Na kafa waɗansu mutanena a ƙofofin don kada a shigo da wani kaya a ranar Asabbaci.
Og det skete, saasnart det blev mørkt i Jerusalems Porte henimod Sabbaten, da bød jeg, saa bleve Portene lukkede, og jeg bød, at de ikke skulde oplade dem før efter Sabbaten, og jeg beskikkede nogle af mine Tjenere ved Portene, at ingen Byrde skulde komme ind paa Sabbatens Dag.
20 Sau ɗaya ko biyu,’yan kasuwa da masu sayar da kowane irin kaya suka kwana waje da Urushalima.
Da bleve Kræmmerne og de, som solgte alle Haande Varer, om Natten uden for Jerusalem, en Gang eller to.
21 Amma na ja kunnensu na ce, “Me ya sa kuke kwana kusa da katanga? In kuka ƙara yin haka, zan kama ku.” Daga wannan lokaci har zuwa gaba ba su ƙara zuwa a ranar Asabbaci ba.
Da vidnede jeg for dem og sagde til dem: Hvorfor bleve I om Natten tværs over for Muren? gøre I det anden Gang, da skal jeg lægge Haand paa eder; fra den Tid kom de ikke om Sabbaten.
22 Sai na umarci Lawiyawa su tsarkake kansu su kuma tafi su yi tsaron ƙofofi don a kiyaye ranar Asabbaci da tsarki. Ka tuna da ni saboda wannan shi ma, ya Allahna, ka nuna mini jinƙai bisa ga madawwamiyar ƙaunarka.
Og jeg sagde til Leviterne, at de skulde rense sig og komme at tage Vare paa Portene for at hellige Sabbatens Dag. Min Gud! kom mig og i Hu for dette, og spar mig efter din megen Miskundhed!
23 Ban da haka, a waɗannan kwanakin na ga mutanen Yahuda waɗanda suka auri mata daga Ashdod, Ammon da Mowab.
Jeg saa ogsaa i de samme Dage, at Jøderne lode asdoditiske, ammonitiske, moabitiske Hustruer bo hos sig.
24 Rabin’ya’yansu suna yaren Ashdod ko kuwa wani yare na waɗansu mutane, ba su kuwa san yadda za su yi Yahudanci ba.
Og Halvdelen af deres Børn talte Asdoditisk, og de forstode ikke at tale jødisk; men de talte efter hvert sit Folks Tungemaal.
25 Na tsawata musu na kuma kira la’ana a kansu. Na bugi waɗansu mutane na kuma ja gashin kansu. Na sa suka yi rantsuwa da sunan Allah na ce, “Kada ku ba da’ya’yanku mata aure ga’ya’yansu maza, ba kuwa za ku auri’ya’yansu mata wa’ya’yanku maza ko wa kanku ba.
Og jeg trættede med dem og forbandede dem og slog nogle af dem og rev Haar af dem; og jeg tog en Ed af dem ved Gud: I skulle ikke give eders Døtre til deres Sønner og ej tage af deres Døtre til eders Sønner, eller til eder selv.
26 Ba don aure-aure irin waɗannan ne Solomon sarkin Isra’ila ya yi zunubi ba? A cikin yawancin al’ummai babu sarki kamar sa. Allahnsa ya ƙaunace shi, Allah kuma ya mai da shi sarki a kan dukan Isra’ila, amma duk da haka baren mata suka rinjaye shi ga zunubi.
Har ikke Salomo, Israels Konge, syndet i disse Ting? enddog der ikke var en Konge som han iblandt de mange Folkeslag, og han var sin Gud kær, og Gud satte ham til Konge over al Israel; og dog kom de fremmede Kvinder ham til at synde.
27 Yanzu za mu ji cewa ku ma kuna yin duk wannan mugunta kuna zama marasa aminci ga Allahnmu ta wurin auren baren mata?”
Skulde vi da høre det om eder, at I gøre alt dette store Onde, saa at I forsynde eder imod vor Gud ved at lade fremmede Kvinder bo hos eder?
28 Ɗaya daga cikin’ya’yan Yohiyada maza, ɗan Eliyashib babban firist, surukin Sanballat mutumin Horon ne. Na kuwa kore shi daga wurina.
Og en blandt Sønnerne af Jojada, Eliasib, Ypperstepræstens Søn, var bleven Sanballats, Horonitens, Svigersøn; derfor drev jeg ham fra mig.
29 Ka tuna da su, ya Allahna, domin sun ƙazantar da aikin firist da kuma alkawarin aikin firist da na Lawiyawa.
Kom dem i Hu, min Gud! fordi de havde besmittet Præstedømmet, ja Præstedømmets og Leviternes Pagt.
30 Saboda haka na tsarkake firistoci da Lawiyawa daga kowane baƙon abu, na kuma ba su aikinsu, kowa ga aikinsa.
Saa rensede jeg dem fra alt fremmed; og jeg beskikkede Præsternes og Leviternes Vagter, hver til sin Gerning,
31 Na kuma yi tanadi don sadakokin itace a ƙayyadaddun lokuta, da kuma don nunan fari. Ka tuna da ni da alheri, ya Allahna.
og til at sørge for Gaven af Veddet til bestemte Tider og for Førstegrøderne. Kom mig i Hu, min Gud! til det gode.