< Nehemiya 13 >

1 A wannan rana aka karanta Littafin Musa da ƙarfi a kunnuwan mutane aka kuma sami an rubuta cewa kada a karɓi mutumin Ammon ko mutumin Mowab cikin taron Allah,
V ten den čteno jest v knize Mojžíšově, tak že lid slyšeti mohl. I nalezeno v ní napsáno, že nemá vjíti Ammonitský a Moábský do shromáždění Božího až na věky,
2 domin ba su taryi Isra’ila da abinci da ruwa ba amma suka yi hayar Bala’am don yă kira la’ana a kansu. (Amma Allahnmu, ya mai da la’anar ta zama albarka.)
Proto že nevyšli proti synům Izraelským s chlebem a s vodou, ale najali ze mzdy proti nim Baláma, aby jim zlořečil, ačkoli obrátil Bůh náš to zlořečení v požehnání.
3 Sa’ad da mutane suka ji wannan doka, sai suka ware daga Isra’ila duk waɗanda suke na baƙon zuriya.
Stalo se pak, když slyšeli zákon, že odmísili všecky přimíšené od Izraele.
4 Kafin wannan, an sa Eliyashib firist yă lura da ɗakuna ajiyar gidan Allahnmu. Yana da dangantaka na kurkusa da Tobiya,
Ale před tím Eliasib kněz, správce komory domu Boha našeho, spříznil se s Tobiášem.
5 ya kuma tanada masa babban ɗakin da dā ake ajiyar hadayun hatsi da turare da kayayyaki haikali, da kuma zakan hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai da aka umarta don Lawiyawa, mawaƙa da kuma matsaran ƙofofi, da kuma sadakoki domin firistoci.
Kterémuž udělal pokoj veliký, kdež prvé skládali dary, kadidlo a nádoby, a desátky z obilé, mstu a oleje nového, nařízené Levítům a zpěvákům i vrátným, též i obět kněžím.
6 Amma yayinda dukan wannan yake faruwa, ba ni a Urushalima, gama a shekara ta talatin da biyu na Artazerzes sarkin Babilon na dawo wurin sarki. A wani lokaci daga baya na nemi izininsa
Ale když se to vše dálo, nebyl jsem v Jeruzalémě. Nebo léta třidcátého druhého Artaxerxa krále Babylonského přišel jsem k králi, a po přeběhnutí let, vyžádán jsem na králi.
7 sai na koma zuwa Urushalima. A nan na ji game da mugun abin da Eliyashib ya aikata da ya tanada wa Tobiya ɗaki a filayen gidan Allah.
Když jsem pak přišel do Jeruzaléma, srozuměl jsem tomu zlému, co učinil Eliasib pro Tobiáše, udělav mu pokoj v síních domu Božího.
8 Na ɓace rai ƙwarai na kuma zubar da dukan kayan gidan Tobiya daga ɗakin.
Což mi se velmi nelíbilo. Protož vyházel jsem všecko nádobí domu Tobiášova ven z toho pokoje.
9 Na umarta a tsarkake ɗakunan, sa’an nan na mayar da kayan gidan Allah a cikin ɗakunan, tare da hadayun hatsi da kuma turare.
A rozkázal jsem očistiti ty pokoje. I vnesl jsem tam zase nádoby domu Božího, dary a kadidlo.
10 Na kuma ji cewa sassan da ake ba wa Lawiyawa ba a ba su ba, cewa kuma dukan Lawiyawa da mawaƙan da suke da hakkin hidima sun koma gonakinsu.
Potom dověděv se, že dílové Levítům nebyli dáváni, a že rozběhli se jeden každý na svou rolí, Levítové i zpěváci vedoucí práci,
11 Sai na tsawata wa shugabanni na kuma tambaye su na ce, “Me ya sa aka ƙyale gidan Allah?” Sa’an nan na kira su gaba ɗaya na sa su a wuraren aikinsu.
Protož domlouval jsem se na starší, řka: Proč jest opuštěn dům Boží? A shromáždiv je, postavil jsem je na místě jejich.
12 Dukan Yahuda suka kawo zakan hatsi, sabon ruwan inabi da mai cikin ɗakunan ajiya.
A všecken Juda přinášeli desátky obilé, mstu a oleje nového do skladů.
13 Na sa Shelemiya firist, Zadok marubuci, da wani Balawe mai suna Fedahiya su lura da ɗakunan ajiya na kuma sa Hanan ɗan Zakkur, ɗan Mattaniya ya zama mataimakinsu, domin an ɗauka waɗannan mutane amintattu ne. Aka ba su hakkin raban kayayyaki wa’yan’uwansu.
A ustanovil jsem úředníky nad sklady: Selemiáše kněze, a Sádocha učitele, a Pedaiáše z Levítů, přidav k nim Chanana syna Zakurova, syna Mattaniášova; nebo za věrné jmíni byli. A ti měli rozdělovati bratřím svým.
14 Ka tuna da ni saboda wannan, ya Allahna, kuma kada ka shafe abin da na yi da aminci domin gidan Allahna da kuma hidimarsa.
Budiž pamětliv na mne, Bože můj, pro to, a nevyhlazuj dobrodiní mých, kteráž jsem prokázal k domu Boha svého i k službám jeho.
15 A waɗannan kwanaki, na ga mutane a Yahuda suna matse ruwan inabi a ranar Asabbaci suna kuma kawo hatsi suna labta su a kan jakuna, tare da ruwan inabi,’ya’yan inabi, ɓaure da kaya iri-iri. Suna kuma kawowa dukan wannan cikin Urushalima a ranar Asabbaci. Saboda haka na gargaɗe su a kan sayar da abinci a wannan rana.
V těch dnech viděl jsem v Judstvu, ani tlačí presem v sobotu, a přinášejí snopy, kteréž nakládali na osly, též víno, hrozny, fíky i všeliká břemena, a snášejí v den sobotní do Jeruzaléma. I domlouval jsem jim v ten den, když prodávali potravu.
16 Mutane daga Taya waɗanda suke zama a Urushalima suna shigar da kifi da kaya iri-iri na’yan kasuwa suna kuma sayar da su a Urushalima a ranar Asabbaci wa mutanen Yahuda.
Tyrští také, kteříž bydlili v něm, nosili ryby i všelijaké koupě, a prodávali v sobotu synům Juda, a to v Jeruzalémě.
17 Sai na tsawata wa manyan Yahuda na ce musu, “Wanda irin mugun abu ke nan kuke yi, kuna ƙazantar da ranar Asabbaci?
Protož jsem domlouval starším Judským, a řekl jsem jim: Jaká jest to nepravost, kterouž činíte, poškvrňujíce dne sobotního?
18 Kakanninku ba su yi irin waɗannan abubuwa ba, har Allahnmu ya kawo dukan masifun nan a kanmu da kuma a kan wannan birni? Yanzu kuna tsokanar fushi mai yawa a kan Isra’ila ta wurin ƙazantar da Asabbaci.”
Zdaliž jsou tak nečinili otcové vaši? Pročež Bůh náš přivedl na nás všecko toto zlé, i na toto město, a vy přidáváte hněvivosti na Izraele, poškvrňujíce soboty.
19 Sa’ad da inuwar yamma ya fāɗo a ƙofofin Urushalima kafin Asabbaci, na umarta a rufe ƙofofi kuma kada a buɗe sai Asabbaci ya wuce. Na kafa waɗansu mutanena a ƙofofin don kada a shigo da wani kaya a ranar Asabbaci.
Když tedy byly v stínu brány Jeruzalémské před sobotou, rozkázal jsem zavříti brány, a rozkázal jsem, aby jich neotvírali až po sobotě. K tomu i z služebníků svých některé postavil jsem v bráně, aby náklad nebyl vezen do města v sobotu.
20 Sau ɗaya ko biyu,’yan kasuwa da masu sayar da kowane irin kaya suka kwana waje da Urushalima.
Protož zůstali kupci a prodavači všelijakých věcí prodajných vně před Jeruzalémem, jednou i podruhé.
21 Amma na ja kunnensu na ce, “Me ya sa kuke kwana kusa da katanga? In kuka ƙara yin haka, zan kama ku.” Daga wannan lokaci har zuwa gaba ba su ƙara zuwa a ranar Asabbaci ba.
I osvědčil jsem se jim, řka jim: Proč zůstáváte přes noc naproti zdi? Učiníte-li to více, vztáhnu ruku na vás. Od té chvíle nepřicházeli v sobotu.
22 Sai na umarci Lawiyawa su tsarkake kansu su kuma tafi su yi tsaron ƙofofi don a kiyaye ranar Asabbaci da tsarki. Ka tuna da ni saboda wannan shi ma, ya Allahna, ka nuna mini jinƙai bisa ga madawwamiyar ƙaunarka.
Rozkázal jsem pak Levítům, aby se očistili, a přijdouce, ostříhali bran, a světili den sobotní. Také i v tom pamatuj na mne, Bože můj, a buď mi milostiv podlé množství milosrdenství svého.
23 Ban da haka, a waɗannan kwanakin na ga mutanen Yahuda waɗanda suka auri mata daga Ashdod, Ammon da Mowab.
V těch dnech spatřil jsem také Židy, kteříž byli pojali ženy Azotské, Ammonitské a Moábské,
24 Rabin’ya’yansu suna yaren Ashdod ko kuwa wani yare na waɗansu mutane, ba su kuwa san yadda za su yi Yahudanci ba.
An synové jejich mluvili od polu Azotsky, a neuměli mluviti Židovsky, ale podlé jazyku každého toho lidu.
25 Na tsawata musu na kuma kira la’ana a kansu. Na bugi waɗansu mutane na kuma ja gashin kansu. Na sa suka yi rantsuwa da sunan Allah na ce, “Kada ku ba da’ya’yanku mata aure ga’ya’yansu maza, ba kuwa za ku auri’ya’yansu mata wa’ya’yanku maza ko wa kanku ba.
Protož domlouval jsem jim, a zlořečil jsem jim, a některé z nich bil jsem a rval, přísahou je zavazuje skrze Boha, řka: Budete-li dávati dcery své synům jejich, aneb bráti dcery jejich synům svým neb sobě, zlořečení budete.
26 Ba don aure-aure irin waɗannan ne Solomon sarkin Isra’ila ya yi zunubi ba? A cikin yawancin al’ummai babu sarki kamar sa. Allahnsa ya ƙaunace shi, Allah kuma ya mai da shi sarki a kan dukan Isra’ila, amma duk da haka baren mata suka rinjaye shi ga zunubi.
Zdaliž tím nezhřešil Šalomoun král Izraelský? Ješto ve mnohých národech nebylo krále jemu podobného, kterýž byl milý Bohu svému, tak že ustanovil jej Bůh králem nade vším Izraelem, však i toho k hříchu přivedly ženy cizozemky.
27 Yanzu za mu ji cewa ku ma kuna yin duk wannan mugunta kuna zama marasa aminci ga Allahnmu ta wurin auren baren mata?”
A vám zdali povolíme, abyste se dopouštěli všeho toho zlého velikého, a přestupovali proti Bohu svému, pojímajíce ženy cizozemky?
28 Ɗaya daga cikin’ya’yan Yohiyada maza, ɗan Eliyashib babban firist, surukin Sanballat mutumin Horon ne. Na kuwa kore shi daga wurina.
Z synů pak Joiady syna Eliasiba, kněze nejvyššího, jeden byl zeť Sanballata Choronského, kteréhož jsem zahnal od sebe.
29 Ka tuna da su, ya Allahna, domin sun ƙazantar da aikin firist da kuma alkawarin aikin firist da na Lawiyawa.
Budiž pamětliv na to, Bože můj, proti těm, kteříž poškvrňují kněžství, a smlouvy kněžské i Levítské.
30 Saboda haka na tsarkake firistoci da Lawiyawa daga kowane baƙon abu, na kuma ba su aikinsu, kowa ga aikinsa.
Protož jsem je vyčistil od všelikého cizozemce, a ustanovil jsem zase třídy kněžím a Levítům, jednomu každému v práci jeho,
31 Na kuma yi tanadi don sadakokin itace a ƙayyadaddun lokuta, da kuma don nunan fari. Ka tuna da ni da alheri, ya Allahna.
I nošení dříví k obětem časy uloženými, též i prvotin. Budiž pamětliv na mne, Bože můj, k mému dobrému.

< Nehemiya 13 >