< Nehemiya 12 >

1 Waɗannan su ne firistoci da Lawiyawa waɗanda suka komo tare da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da kuma Yeshuwa. Serahiya, Irmiya, Ezra,
Or ce sont ici les Sacrificateurs et les Lévites qui montèrent avec Zorobabel, fils de Salathiel, et avec Jésuah, [savoir]: Séraja, Jérémie, Esdras,
2 Amariya, Malluk, Hattush
Amaria, Malluc, Hattus,
3 Shekaniya, Rehum, Meremot,
Sécania, Réhum, Mérémoth,
4 Iddo, Ginneton, Abiya,
Hiddo, Guinnethoï, Abija,
5 Miyamin, Mowadiya, Bilga,
Mijamin, Mahadia, Bilga,
6 Shemahiya, Yohiyarib, Yedahiya,
Sémahia, Jojarib, Jédahia,
7 Sallu, Amok, Hilkiya da Yedahiya. Waɗannan su ne shugabannin firistoci da’yan’uwansu a kwanakin Yeshuwa.
Sallu, Hamok, Hilkija, Jédahia. Ce furent là les principaux des Sacrificateurs, et de leurs frères, du temps de Jésuah.
8 Lawiyawan su ne Yeshuwa, Binnuyi, Kadmiyel, Sherebiya, Yahuda, da kuma Mattaniya, wanda tare da’yan’uwansa yake lura da waƙoƙin godiya.
Et quant aux Lévites, il y avait Jésuah, Binnui, Kadmiel, Sérebia, Juda, et Mattania, qui était commis sur les louanges, lui et ses frères.
9 Bakbukiya da Unni,’yan’uwansu sun tsaya ɗaura da su a hidimomi.
Et Bakbukia, et Hunni, leurs frères, étaient vis-à-vis d'eux en leurs charges.
10 Yeshuwa ne mahaifin Yohiyakim, Yohiyakim shi ne mahaifin Eliyashib, Eliyashib shi ne mahaifin Yohiyada,
Or Jésuah engendra Jojakim, et Jojakim engendra Eliasib, et Eliasib engendra Jojadah,
11 Yohiyada shi ne mahaifin Yonatan, Yonatan kuma mahaifin Yadduwa.
Et Jojadah engendra Jonathan, et Jonathan engendra Jadduah.
12 A kwanakin Yohiyakim, waɗannan su ne shugabannin iyalan firistoci, na iyalin Serahiya, Merahiya; na iyalin Irmiya, Hananiya;
Et ceux-ci au temps de Jojakim étaient Sacrificateurs, Chefs des pères; pour Séraja, Méraja; pour Jérémie, Hanania;
13 na iyalin Ezra, Meshullam; na iyalin Amariya, Yehohanan;
Pour Esdras, Mésullam; pour Amaria, Johanan;
14 na iyalin Malluk, Yonatan; na iyalin Shebaniya, Yusuf;
Pour Mélicu, Jonathan; pour Sébania, Joseph;
15 na iyalin Harim, Adna; na iyalin Merahiyot, Helkai;
Pour Harim, Hadna; pour Mérajoth, Helkaï;
16 na iyalin Iddo, Zakariya; na iyalin Ginneton, Meshullam;
Pour Hiddo, Zacharie; pour Guinnethon, Mésullam;
17 na iyalin Abiya, Zikri; na iyalin Miniyamin da na Mowadiya, Filtai;
Pour Abija, Zicri; pour Minjamin et Mohadia, Piltaï;
18 na iyalin Bilga, Shammuwa; na iyalin Shemahiya, Yehonatan;
Pour Bilga, Sammuah; pour Sémahia, Jonathan;
19 na iyalin Yohiyarib, Mattenai; na iyalin Yedahiya, Uzzi;
Pour Jojarib, Matténaï; pour Jédahia, Huzi;
20 na iyalin Sallu, Kallai; na iyalin Amok, Eber;
Pour Sallaï, Kallaï; pour Hamok, Héber;
21 na iyalin Hilkiya, Hashabiya; na iyalin Yedahiya, Netanel.
Pour Hilkija, Hasabia; pour Jédahia, Nathanaël.
22 Shugabannin iyalin Lawiyawa a kwanakin Eliyashib, Yohiyada, Yohanan da Yadduwa, da kuma na firistoci, an rubuta su a zamanin mulkin Dariyus mutumin Farisa.
Quant aux Lévites, les chefs de leurs pères, du temps d'Eliasib, Jojadah, Johanan et Jadduah sont enregistrés avec les Sacrificateurs, jusqu'au règne de Darius de Perse.
23 Shugabannin iyali cikin zuriyar Lawi har zuwa lokacin Yohanan ɗan Eliyashib, an rubuta su a cikin littafin tarihi.
De sorte que les enfants de Lévi Chefs des pères ont été enregistrés au Livre des Chroniques, jusqu'au temps de Johanan, [petit-]fils d'Eliasib.
24 Shugabannin Lawiyawa kuwa su ne Hashabiya, Sherebiya, Yeshuwa ɗan Kadmiyel, da’yan’uwansu, waɗanda suka tsaya ɗaura da su don su yi yabo da kuma godiya, sashe ɗaya kan ba da amsa ga ɗaya sashen, kamar yadda Dawuda mutumin Allah ya umarta.
Les Chefs donc des Lévites furent Hasabia, Sérebia, et Jésuah, fils de Kadmiel, et leurs frères étaient vis-à-vis d'eux, pour louer et célébrer [le Nom de Dieu], selon le commandement de David, homme de Dieu, un rang correspondant à l'autre.
25 Mattaniya, Bakbukiya, Obadiya, Meshullam, Talmon da Akkub su ne matsaran ƙofofi waɗanda suka yi tsaron ɗaukan ajiya a ƙofofi.
Mattania, Bakbukia et Hobadia, Mésullam, Talmon, et Hakkub avaient la charge des portiers qui faisaient la garde dans les assemblées des portes.
26 Sun yi hidima a kwanakin Yohiyakim ɗan Yeshuwa, ɗan Yozadak, kuma a kwanakin Nehemiya gwamna da kuma na Ezra firist da kuma marubuci.
Ceux-là furent du temps de Jojakim, fils de Jésuah, fils de Jotsadak, et du temps de Néhémie le Gouverneur, et d'Esdras Sacrificateur et Scribe.
27 A keɓewar katangar Urushalima, an nemi Lawiyawa daga inda suke zama aka kawo su Urushalima don su yi bikin miƙawa da farin ciki da waƙoƙin godiya da kuma kiɗin kuge, garaya da molo.
Or en la dédicace de la muraille de Jérusalem, on envoya quérir les Lévites de tous leurs lieux, pour les faire venir à Jérusalem, afin qu'on célébrât la dédicace avec joie, par des actions de grâces, et par des cantiques sur des cymbales, des musettes, et des violons.
28 Aka kuma tattara mawaƙa su ma daga yankin kewayen Urushalima, daga ƙauyukan Netofawa,
On assembla donc ceux qui étaient de la race des chantres, tant de la campagne des environs de Jérusalem, que des bourgades des Nétophathiens.
29 daga Bet-Gilgal, da kuma daga wuraren Geba da Azmawet, gama mawaƙan sun gina wa kansu ƙauyuka kewaye da Urushalima.
Et du lieu de Guilgal, et des territoires de Guébah et d'Hazmaveth; car les chantres s'étaient bâti des bourgades aux environs de Jérusalem.
30 Sa’ad da firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu da tsarki, sai suka tsarkake mutane, ƙofofi da kuma katanga.
Ainsi les Sacrificateurs et les Lévites se purifièrent, ils purifièrent [aussi] le peuple, les portes, et la muraille.
31 Sai na sa shugabannin Yahuda suka haura zuwa bisan katangar. Na kuma sa manyan ƙungiyoyi biyu na mawaƙa su miƙa godiya. Ɗaya ya haura zuwa bisan katangar zuwa dama, wajen Ƙofar Juji.
Puis je fis monter les principaux de Juda sur la muraille, et j'établis deux grandes bandes qui devaient chanter les louanges [de Dieu], et le chemin [de l'une] était à la droite, sur la muraille tendant vers la porte de la fiente.
32 Hoshahiya da rabin shugabannin Yahuda kuwa suka bi su,
Et après eux marchait Hosahia, avec la moitié des principaux de Juda;
33 tare da Azariya, Ezra, Meshullam,
[savoir] Hazaria, Esdras, Mésullam,
34 Yahuda, Benyamin, Shemahiya, Irmiya,
Juda, Benjamin, Sémahia et Jérémie;
35 da waɗansu firistoci kuma da ƙahoni, da kuma Zakariya ɗan Yonatan, ɗan Shemahiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mikahiya, ɗan Zakkur, ɗan Asaf,
Et quelques-uns d'entre les enfants des Sacrificateurs avec les trompettes. Puis Zacharie fils de Jonathan, fils de Sémahia, fils de Mattania, fils de Micaja, fils de Zaccur, fils d'Asaph,
36 da’yan’uwansa, Shemahiya, Azarel, Milalai, Gilalai, Ma’ai, Netanel, Yahuda da Hanani, tare da kayan kiɗi da Dawuda mutumin Allah ya umarta. Ezra malamin Doka ya jagoranci jerin gwanon.
Et ses frères, Sémahia, Hazaréel, Milalaï, Guilalaï, Mahaï, Nathanaël, Juda, et Hanani, avec les instruments des cantiques de David, homme de Dieu; et Esdras le cribe marchait devant eux.
37 A Ƙofar Maɓuɓɓuga suka ci gaba kai tsaye suka haura matakalan Birnin Dawuda a kan hawa zuwa katangar suka wuce a bisa gidan Dawuda zuwa Ƙofar Ruwa wajen gabas.
Et ils vinrent vers la porte de la fontaine qui était vis-à-vis d'eux, et montèrent aux degrés de la cité de David, par la montée de la muraille, depuis la maison de David, jusqu'à la porte des eaux, vers l'orient.
38 Ƙungiyar mawaƙa ta biyu suka yi jerin gwano a ɗaya gefen. Na bi su a bisan katangar, tare da rabin mutanen, muka wuce Hasumiya Tanderu zuwa Katanga Mai Faɗi,
Et la seconde bande de ceux qui chantaient les louanges [de Dieu], allait à l'opposite, et j'allais après elle, avec [l'autre] moitié du peuple, allant sur la muraille, par-dessus la tour des fours, jusqu'à la muraille large;
39 bisa Ƙofar Efraim, Ƙofar Yeshana, Ƙofar Kifi, Hasumiyar Hananel da kuma Hasumiya ɗari, har zuwa Ƙofar Tumaki. A Ƙofar Matsara suka tsaya.
Et vers la porte d'Ephraïm, et vers la porte vieille, et vers la porte des poissons, [vers] la tour de Hananéel, et [vers] la tour de Méah, jusqu'à la porte du bercail, et ils s'arrêtèrent vers la porte de la prison.
40 Ƙungiyoyin mawaƙa biyu da suka yi godiya suka ɗauki wurarensu a gidan Allah, haka ma ni, tare da rabin shugabanni,
Puis les deux bandes de ceux qui chantaient les louanges [de Dieu], s'arrêtèrent dans la maison de Dieu. [Je m'arrêtai] aussi avec la moitié des magistrats qui étaient avec moi;
41 da kuma firistoci, Eliyakim, Ma’asehiya, Miniyamin, Mikahiya, Eliyohenai, Zakariya da Hananiya tare da ƙahoninsu,
Et les Sacrificateurs, Eliakim, Mahaséja, Minjamin, Micaja, Eliohénaï, Zacharie, et Hanania, avec les trompettes;
42 haka ma Ma’asehiya, Shemahiya, Eleyazar, Uzzi, Yehohanan, Malkiya, Elam da Ezer. Mawaƙan suka rera waƙoƙi a ƙarƙashin kulawar Yezrahiya.
Et Mahaséja, Sémahia, Elhaza, Huzi, Johanan, Malkija, Hélam et Hézer. Puis les chantres, desquels Jizrahia avait la charge, firent retentir [leur voix.]
43 A rana ta uku kuma suka miƙa manyan hadayu, suna farin ciki domin Allah ya ba su farin ciki mai girma. Mata da yara suka yi farin ciki su ma. An ji ƙarar farin ciki da ake yi a Urushalima daga nesa.
On offrit aussi en ce jour-là de grands sacrifices, et on se réjouit, parce que Dieu leur avait donné une grande [matière] de joie: même les femmes et les enfants se réjouirent; et la joie de Jérusalem fut entendue de loin.
44 A lokacin an naɗa mutane su lura da ɗakunan ajiya don sadakoki, nunan fari da kuma zakka. Daga gonakin garuruwan da suke kewaye za su kawo sassan da Dokar ta umarta zuwa ɗakunan ajiya domin firistoci da Lawiyawa, gama Yahuda ya ji daɗin aikin firistoci da Lawiyawa.
Et on établit en ce jour-là des hommes sur les chambres des trésors, des oblations, des prémices et des dîmes; pour rassembler du territoire des villes les portions ordonnées par la Loi aux Sacrificateurs et aux Lévites; car Juda fut dans la joie à cause des Sacrificateurs et des Lévites, qui se trouvaient là;
45 Sun yi hidimar Allahnsu da kuma hidimar tsarkakewa, kamar yadda mawaƙa da matsaran ƙofofi suka yi, bisa ga umarnin Dawuda da ɗansa Solomon.
Parce qu'ils avaient gardé la charge qui leur avait été donnée de la part de leur Dieu, et la charge de la purification. [On établit] aussi des chantres, et des portiers, selon le commandement de David, et de Salomon, son fils.
46 Gama tun dā, a kwanakin Dawuda da Asaf, akwai masu bi da mawaƙa da kuma na waƙoƙin yabo da na godiya ga Allah.
Car autrefois, du temps de David et d'Asaph, on avait établi des Chefs des chantres, et des cantiques de louange, et d'action de grâces à Dieu.
47 Saboda haka a kwanakin Zerubbabel da Nehemiya, dukan Isra’ila suka ba da sashe na kowace rana domin mawaƙa da matsaran ƙofofi. Suka kuma keɓe sashe don sauran Lawiyawa, Lawiyawan kuma suka keɓe sashe don zuriyar Haruna.
C'est pourquoi tous les Israélites du temps de Zorobabel, et du temps de Néhémie, donnaient les portions des chantres et des portiers, [savoir], ce qu'il fallait chaque jour, et les consacraient aux Lévites, et les Lévites les consacraient aux enfants d'Aaron.

< Nehemiya 12 >