< Nehemiya 12 >
1 Waɗannan su ne firistoci da Lawiyawa waɗanda suka komo tare da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da kuma Yeshuwa. Serahiya, Irmiya, Ezra,
Voici les sacrificateurs et les Lévites qui montèrent avec Zorobabel, fils de Shealthiel, et avec Josué: Seraia, Jérémie, Esdras,
2 Amariya, Malluk, Hattush
Amaria, Malluch, Hattush,
3 Shekaniya, Rehum, Meremot,
Shecania, Rehum, Meremoth,
5 Miyamin, Mowadiya, Bilga,
Mijamin, Maadia, Bilga,
6 Shemahiya, Yohiyarib, Yedahiya,
Shemaia, Joiarib, Jedaiah,
7 Sallu, Amok, Hilkiya da Yedahiya. Waɗannan su ne shugabannin firistoci da’yan’uwansu a kwanakin Yeshuwa.
Sallu, Amok, Hilkiah et Jedaiah. Tels étaient les chefs des prêtres et de leurs frères, du temps de Josué.
8 Lawiyawan su ne Yeshuwa, Binnuyi, Kadmiyel, Sherebiya, Yahuda, da kuma Mattaniya, wanda tare da’yan’uwansa yake lura da waƙoƙin godiya.
Les Lévites étaient: Josué, Binnui, Kadmiel, Shérébia, Juda, et Matthania, qui était chargé des chants d'action de grâces, lui et ses frères.
9 Bakbukiya da Unni,’yan’uwansu sun tsaya ɗaura da su a hidimomi.
Bakbukiah et Unno, leurs frères, étaient également près d'eux, selon leurs fonctions.
10 Yeshuwa ne mahaifin Yohiyakim, Yohiyakim shi ne mahaifin Eliyashib, Eliyashib shi ne mahaifin Yohiyada,
Jeshua engendra Joiakim; Joiakim engendra Eliashib; Eliashib engendra Joiada;
11 Yohiyada shi ne mahaifin Yonatan, Yonatan kuma mahaifin Yadduwa.
Joiada engendra Jonathan; Jonathan engendra Jaddua.
12 A kwanakin Yohiyakim, waɗannan su ne shugabannin iyalan firistoci, na iyalin Serahiya, Merahiya; na iyalin Irmiya, Hananiya;
Du temps de Jojakim, il y eut des prêtres, chefs de famille de leurs pères: de Seraja, Meraja; de Jérémie, Hanania;
13 na iyalin Ezra, Meshullam; na iyalin Amariya, Yehohanan;
d'Esdras, Meshullam; d'Amaria, Jehohanan;
14 na iyalin Malluk, Yonatan; na iyalin Shebaniya, Yusuf;
de Malluchi, Jonathan; de Shebania, Joseph;
15 na iyalin Harim, Adna; na iyalin Merahiyot, Helkai;
de Harim, Adna; de Meraioth, Helkaï;
16 na iyalin Iddo, Zakariya; na iyalin Ginneton, Meshullam;
d'Iddo, Zacharie; de Ginnethon, Meshullam;
17 na iyalin Abiya, Zikri; na iyalin Miniyamin da na Mowadiya, Filtai;
d'Abija, Zichri; de Miniamin, de Moadia, Piltai;
18 na iyalin Bilga, Shammuwa; na iyalin Shemahiya, Yehonatan;
de Bilga, Shammua; de Shemaia, Jehonathan;
19 na iyalin Yohiyarib, Mattenai; na iyalin Yedahiya, Uzzi;
de Jojarib, Mattenai; de Jedaia, Uzzi;
20 na iyalin Sallu, Kallai; na iyalin Amok, Eber;
de Sallai, Kallai; d'Amok, Eber;
21 na iyalin Hilkiya, Hashabiya; na iyalin Yedahiya, Netanel.
de Hilkiah, Hashabiah; de Jedaiah, Nethanel.
22 Shugabannin iyalin Lawiyawa a kwanakin Eliyashib, Yohiyada, Yohanan da Yadduwa, da kuma na firistoci, an rubuta su a zamanin mulkin Dariyus mutumin Farisa.
Quant aux Lévites, aux jours d'Eliaschib, de Jojada, de Jochanan et de Jaddua, on enregistra les chefs de famille; les prêtres aussi, sous le règne de Darius le Perse.
23 Shugabannin iyali cikin zuriyar Lawi har zuwa lokacin Yohanan ɗan Eliyashib, an rubuta su a cikin littafin tarihi.
Les fils de Lévi, chefs de famille, furent inscrits dans le livre des chroniques, jusqu'à l'époque de Johanan, fils d'Eliashib.
24 Shugabannin Lawiyawa kuwa su ne Hashabiya, Sherebiya, Yeshuwa ɗan Kadmiyel, da’yan’uwansu, waɗanda suka tsaya ɗaura da su don su yi yabo da kuma godiya, sashe ɗaya kan ba da amsa ga ɗaya sashen, kamar yadda Dawuda mutumin Allah ya umarta.
Les chefs des Lévites: Haschabia, Shérébia et Josué, fils de Kadmiel, avec leurs frères près d'eux, pour louer et remercier selon le commandement de David, homme de Dieu, section par section.
25 Mattaniya, Bakbukiya, Obadiya, Meshullam, Talmon da Akkub su ne matsaran ƙofofi waɗanda suka yi tsaron ɗaukan ajiya a ƙofofi.
Mattania, Bakbukiah, Abdias, Meshullam, Talmon et Akkub étaient des gardiens de portes qui surveillaient les entrepôts des portes.
26 Sun yi hidima a kwanakin Yohiyakim ɗan Yeshuwa, ɗan Yozadak, kuma a kwanakin Nehemiya gwamna da kuma na Ezra firist da kuma marubuci.
C'était du temps de Jojakim, fils de Josué, fils de Jotsadak, du temps de Néhémie, le gouverneur, et d'Esdras, le prêtre et le scribe.
27 A keɓewar katangar Urushalima, an nemi Lawiyawa daga inda suke zama aka kawo su Urushalima don su yi bikin miƙawa da farin ciki da waƙoƙin godiya da kuma kiɗin kuge, garaya da molo.
Lors de la dédicace de la muraille de Jérusalem, on chercha les Lévites de tous les lieux où ils se trouvaient, pour les faire venir à Jérusalem afin de célébrer la dédicace dans la joie, tant par des actions de grâces que par des chants, avec des cymbales, des instruments à cordes et des harpes.
28 Aka kuma tattara mawaƙa su ma daga yankin kewayen Urushalima, daga ƙauyukan Netofawa,
Les fils des chantres se rassemblèrent, tant de la plaine qui entoure Jérusalem que des villages des Netophathites;
29 daga Bet-Gilgal, da kuma daga wuraren Geba da Azmawet, gama mawaƙan sun gina wa kansu ƙauyuka kewaye da Urushalima.
aussi de Beth Gilgal et des champs de Guéba et d'Azmaveth, car les chantres s'étaient construit des villages autour de Jérusalem.
30 Sa’ad da firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu da tsarki, sai suka tsarkake mutane, ƙofofi da kuma katanga.
Les prêtres et les lévites se purifièrent; ils purifièrent le peuple, les portes et la muraille.
31 Sai na sa shugabannin Yahuda suka haura zuwa bisan katangar. Na kuma sa manyan ƙungiyoyi biyu na mawaƙa su miƙa godiya. Ɗaya ya haura zuwa bisan katangar zuwa dama, wajen Ƙofar Juji.
Puis je fis monter les princes de Juda sur la muraille, et je désignai deux grandes compagnies qui rendirent grâces et allèrent en procession. L'une marchait à droite sur la muraille, vers la porte des fumiers;
32 Hoshahiya da rabin shugabannin Yahuda kuwa suka bi su,
et après elle, Hoshaiah, avec la moitié des princes de Juda,
33 tare da Azariya, Ezra, Meshullam,
Azaria, Esdras, Meshullam,
34 Yahuda, Benyamin, Shemahiya, Irmiya,
Juda, Benjamin, Shemaiah, Jérémie,
35 da waɗansu firistoci kuma da ƙahoni, da kuma Zakariya ɗan Yonatan, ɗan Shemahiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mikahiya, ɗan Zakkur, ɗan Asaf,
et quelques fils de prêtres avec des trompettes: Zacharie, fils de Jonathan, fils de Schemaeja, fils de Matthania, fils de Michée, fils de Zaccur, fils d'Asaph,
36 da’yan’uwansa, Shemahiya, Azarel, Milalai, Gilalai, Ma’ai, Netanel, Yahuda da Hanani, tare da kayan kiɗi da Dawuda mutumin Allah ya umarta. Ezra malamin Doka ya jagoranci jerin gwanon.
et ses frères, Schemaeja, Azarel, Milalaï, Gilalaï, Maaï, Nethaneel, Juda et Hanani, avec les instruments de musique de David, homme de Dieu; et Esdras, le scribe, était devant eux.
37 A Ƙofar Maɓuɓɓuga suka ci gaba kai tsaye suka haura matakalan Birnin Dawuda a kan hawa zuwa katangar suka wuce a bisa gidan Dawuda zuwa Ƙofar Ruwa wajen gabas.
Par la porte de la source, et droit devant eux, ils montèrent par les escaliers de la ville de David, sur la montée de la muraille, au-dessus de la maison de David, jusqu'à la porte des eaux, à l'orient.
38 Ƙungiyar mawaƙa ta biyu suka yi jerin gwano a ɗaya gefen. Na bi su a bisan katangar, tare da rabin mutanen, muka wuce Hasumiya Tanderu zuwa Katanga Mai Faɗi,
L'autre troupe de ceux qui rendaient grâces alla à leur rencontre, et moi après eux, avec la moitié du peuple, sur le mur au-dessus de la tour des fourneaux, jusqu'à la grande muraille,
39 bisa Ƙofar Efraim, Ƙofar Yeshana, Ƙofar Kifi, Hasumiyar Hananel da kuma Hasumiya ɗari, har zuwa Ƙofar Tumaki. A Ƙofar Matsara suka tsaya.
et au-dessus de la porte d'Ephraïm, et par la vieille porte, et par la porte des poissons, la tour de Hananel, et la tour de Hamméa, jusqu'à la porte des brebis; et ils s'arrêtèrent à la porte de la garde.
40 Ƙungiyoyin mawaƙa biyu da suka yi godiya suka ɗauki wurarensu a gidan Allah, haka ma ni, tare da rabin shugabanni,
Les deux compagnies de ceux qui rendaient grâces dans la maison de Dieu se tinrent debout, moi et la moitié des chefs avec moi,
41 da kuma firistoci, Eliyakim, Ma’asehiya, Miniyamin, Mikahiya, Eliyohenai, Zakariya da Hananiya tare da ƙahoninsu,
et les prêtres, Eliakim, Maaséja, Miniamin, Micaeja, Elioénaï, Zacharie et Hanania, avec des trompettes,
42 haka ma Ma’asehiya, Shemahiya, Eleyazar, Uzzi, Yehohanan, Malkiya, Elam da Ezer. Mawaƙan suka rera waƙoƙi a ƙarƙashin kulawar Yezrahiya.
et Maaséja, Schemaeja, Éléazar, Uzzi, Johanan, Malkija, Élam et Ézer. Les chantres chantaient à haute voix, avec Jizrachia, leur chef.
43 A rana ta uku kuma suka miƙa manyan hadayu, suna farin ciki domin Allah ya ba su farin ciki mai girma. Mata da yara suka yi farin ciki su ma. An ji ƙarar farin ciki da ake yi a Urushalima daga nesa.
Ils offrirent ce jour-là de grands sacrifices, et ils se réjouirent, car Dieu les avait comblés d'une grande joie; les femmes et les enfants se réjouirent aussi, de sorte que la joie de Jérusalem se fit entendre jusqu'au loin.
44 A lokacin an naɗa mutane su lura da ɗakunan ajiya don sadakoki, nunan fari da kuma zakka. Daga gonakin garuruwan da suke kewaye za su kawo sassan da Dokar ta umarta zuwa ɗakunan ajiya domin firistoci da Lawiyawa, gama Yahuda ya ji daɗin aikin firistoci da Lawiyawa.
Ce jour-là, des hommes furent désignés pour surveiller les salles destinées aux trésors, aux offrandes ondulées, aux prémices et aux dîmes, afin d'y recueillir, selon les champs des villes, les portions fixées par la loi pour les prêtres et les lévites; car Juda se réjouissait pour les prêtres et pour les lévites qui faisaient le service.
45 Sun yi hidimar Allahnsu da kuma hidimar tsarkakewa, kamar yadda mawaƙa da matsaran ƙofofi suka yi, bisa ga umarnin Dawuda da ɗansa Solomon.
Ils accomplissaient le devoir de leur Dieu et le devoir de la purification, de même que les chantres et les portiers, selon le commandement de David et de Salomon, son fils.
46 Gama tun dā, a kwanakin Dawuda da Asaf, akwai masu bi da mawaƙa da kuma na waƙoƙin yabo da na godiya ga Allah.
Car du temps de David et d'Asaph, il y avait un chef des chantres, et des chants de louange et d'action de grâce à Dieu.
47 Saboda haka a kwanakin Zerubbabel da Nehemiya, dukan Isra’ila suka ba da sashe na kowace rana domin mawaƙa da matsaran ƙofofi. Suka kuma keɓe sashe don sauran Lawiyawa, Lawiyawan kuma suka keɓe sashe don zuriyar Haruna.
Tout Israël, du temps de Zorobabel et du temps de Néhémie, donna les portions des chantres et des portiers, selon les besoins de chaque jour; on mit à part ce qui était pour les Lévites, et les Lévites mirent à part ce qui était pour les fils d'Aaron.