< Nehemiya 12 >
1 Waɗannan su ne firistoci da Lawiyawa waɗanda suka komo tare da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da kuma Yeshuwa. Serahiya, Irmiya, Ezra,
Følgende er Præsterne og Leviter, der drog op med Zerubbabel, Sjealtiels Søn, og Jesua: Seraja, Jirmeja, Ezra,
2 Amariya, Malluk, Hattush
Amarja, Malluk, Hattusj.
3 Shekaniya, Rehum, Meremot,
Sjekanja, Harim, Meremot,
5 Miyamin, Mowadiya, Bilga,
Mijjamin, Ma'adja, Bilga,
6 Shemahiya, Yohiyarib, Yedahiya,
Sjemaja, Jojarib, Jedaja,
7 Sallu, Amok, Hilkiya da Yedahiya. Waɗannan su ne shugabannin firistoci da’yan’uwansu a kwanakin Yeshuwa.
Sallu, Amok, Hilkija og Jedaja. Det var Overhovederne for Præsterne og deres Brødre paa Jesuas Tid.
8 Lawiyawan su ne Yeshuwa, Binnuyi, Kadmiyel, Sherebiya, Yahuda, da kuma Mattaniya, wanda tare da’yan’uwansa yake lura da waƙoƙin godiya.
Leviterne: Jesua, Binnuj, Kadmiel, Sjerebja, Juda, Mattanja, der sammen med sine Brødre forestod Lovsangen,
9 Bakbukiya da Unni,’yan’uwansu sun tsaya ɗaura da su a hidimomi.
medens Bakbukja og Unni sammen med deres Brødre stod over for dem efter deres Afdelinger.
10 Yeshuwa ne mahaifin Yohiyakim, Yohiyakim shi ne mahaifin Eliyashib, Eliyashib shi ne mahaifin Yohiyada,
Jesua avlede Jojakim, Jojakim avlede Eljasjib, Eljasjib avlede Jojada,
11 Yohiyada shi ne mahaifin Yonatan, Yonatan kuma mahaifin Yadduwa.
Jojada avlede Johanan, og Johanan avlede Jaddua.
12 A kwanakin Yohiyakim, waɗannan su ne shugabannin iyalan firistoci, na iyalin Serahiya, Merahiya; na iyalin Irmiya, Hananiya;
Paa Jojakims Tid var Overhovederne for Præsternes Fædrenehuse følgende: Meraja for Seraja, Hananja for Jirmeja,
13 na iyalin Ezra, Meshullam; na iyalin Amariya, Yehohanan;
Mesjullam for Ezra, Johanan for Amarja,
14 na iyalin Malluk, Yonatan; na iyalin Shebaniya, Yusuf;
Jonatan for Malluk, Josef for Sjebanja,
15 na iyalin Harim, Adna; na iyalin Merahiyot, Helkai;
Adna for Harim, Helkaj for Merajot,
16 na iyalin Iddo, Zakariya; na iyalin Ginneton, Meshullam;
Zekarja for Iddo, Mesjullam for Ginneton,
17 na iyalin Abiya, Zikri; na iyalin Miniyamin da na Mowadiya, Filtai;
Zikri for Abija, .... for Minjamin, Piltaj for Ma'adja,
18 na iyalin Bilga, Shammuwa; na iyalin Shemahiya, Yehonatan;
Sjammua for Bilga, Jonatan for Sjemaja,
19 na iyalin Yohiyarib, Mattenai; na iyalin Yedahiya, Uzzi;
Mattenaj for Jojarib, Uzzi for Jedaja,
20 na iyalin Sallu, Kallai; na iyalin Amok, Eber;
Kallaj for Sallu, Eber for Amok,
21 na iyalin Hilkiya, Hashabiya; na iyalin Yedahiya, Netanel.
Hasjabja for Hilkija og Netan'el for Jedaja.
22 Shugabannin iyalin Lawiyawa a kwanakin Eliyashib, Yohiyada, Yohanan da Yadduwa, da kuma na firistoci, an rubuta su a zamanin mulkin Dariyus mutumin Farisa.
Leviterne: .... . I Eljasjibs, Jojadas, Johanans og Jadduas Dage optegnedes Overhovederne for Fædrenehusene og Præsterne indtil Perseren Darius's Regering.
23 Shugabannin iyali cikin zuriyar Lawi har zuwa lokacin Yohanan ɗan Eliyashib, an rubuta su a cikin littafin tarihi.
Af Levis Efterkommere optegnedes Overhovederne for Fædrenehusene i Krønikebogen ned til Johanans, Eljasjibs Søns, Dage.
24 Shugabannin Lawiyawa kuwa su ne Hashabiya, Sherebiya, Yeshuwa ɗan Kadmiyel, da’yan’uwansu, waɗanda suka tsaya ɗaura da su don su yi yabo da kuma godiya, sashe ɗaya kan ba da amsa ga ɗaya sashen, kamar yadda Dawuda mutumin Allah ya umarta.
Og Leviternes Overhoveder var: Hasjabja, Sjerebja, Jesua, Binnuj, Kadmiel og deres Brødre, der stod over for dem for at synge Lovsangen og Takkesangen efter den Guds Mand Davids Bud, den ene Afdeling efter den anden;
25 Mattaniya, Bakbukiya, Obadiya, Meshullam, Talmon da Akkub su ne matsaran ƙofofi waɗanda suka yi tsaron ɗaukan ajiya a ƙofofi.
og Mattanja, Bakbukja og Obadja, Mesjullam, Talmon og Akkub var Dørvogtere og holdt Vagt ved Portenes Forraadskamre.
26 Sun yi hidima a kwanakin Yohiyakim ɗan Yeshuwa, ɗan Yozadak, kuma a kwanakin Nehemiya gwamna da kuma na Ezra firist da kuma marubuci.
Disse var Overhoveder paa Jojakims Tid, en Søn af Jesua, en Søn af Jozadak, og paa Statholderen Nehemias's og Præsten Ezra den Skriftlærdes Tid.
27 A keɓewar katangar Urushalima, an nemi Lawiyawa daga inda suke zama aka kawo su Urushalima don su yi bikin miƙawa da farin ciki da waƙoƙin godiya da kuma kiɗin kuge, garaya da molo.
Da Jerusalems Mur skulde indvies, opsøgte man Leviterne alle Vegne, hvor de boede, og bragte dem til Jerusalem, for at de skulde fejre Indvielsen med Fryd og Takkesang, med Sang, Cymbler, Harper og Citre.
28 Aka kuma tattara mawaƙa su ma daga yankin kewayen Urushalima, daga ƙauyukan Netofawa,
Da samledes Sangerne fra Egnen om Jerusalem og fra Netofatiternes Landsbyer,
29 daga Bet-Gilgal, da kuma daga wuraren Geba da Azmawet, gama mawaƙan sun gina wa kansu ƙauyuka kewaye da Urushalima.
fra Bet-Gilgal, fra Gebas og Azmavets Marker; thi Sangerne havde bygget sig Landsbyer rundt om Jerusalem.
30 Sa’ad da firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu da tsarki, sai suka tsarkake mutane, ƙofofi da kuma katanga.
Da Præsterne og Leviterne havde renset sig, rensede de Folket, Portene og Muren.
31 Sai na sa shugabannin Yahuda suka haura zuwa bisan katangar. Na kuma sa manyan ƙungiyoyi biyu na mawaƙa su miƙa godiya. Ɗaya ya haura zuwa bisan katangar zuwa dama, wajen Ƙofar Juji.
Saa lod jeg Judas Øverster stige op paa Muren og opstillede to store Lovprisningstog. Det ene drog til højre oven paa Muren ad Møgporten til,
32 Hoshahiya da rabin shugabannin Yahuda kuwa suka bi su,
og med det fulgte Hosjaja og den ene Halvdel af Judas Øverster;
33 tare da Azariya, Ezra, Meshullam,
dernæst nogle af Præsterne med Trompeter, Azarja, Ezra, Mesjullam,
34 Yahuda, Benyamin, Shemahiya, Irmiya,
Juda, Benjamin, Sjemaja og Jirmeja;
35 da waɗansu firistoci kuma da ƙahoni, da kuma Zakariya ɗan Yonatan, ɗan Shemahiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mikahiya, ɗan Zakkur, ɗan Asaf,
endvidere Zekarja, en Søn af Jonatan, en Søn af Sjemaja, en Søn af Mattanja, en Søn af Mika, en Søn af Zakkur, en Søn af Asaf,
36 da’yan’uwansa, Shemahiya, Azarel, Milalai, Gilalai, Ma’ai, Netanel, Yahuda da Hanani, tare da kayan kiɗi da Dawuda mutumin Allah ya umarta. Ezra malamin Doka ya jagoranci jerin gwanon.
og hans Brødre Sjemaja, Azar'el, Milalaj, Gilalaj, Ma'aj, Netan'el, Juda, Hanani med den Guds Mand Davids Musikinstrumenter, med Ezra den Skriftlærde i Spidsen;
37 A Ƙofar Maɓuɓɓuga suka ci gaba kai tsaye suka haura matakalan Birnin Dawuda a kan hawa zuwa katangar suka wuce a bisa gidan Dawuda zuwa Ƙofar Ruwa wajen gabas.
og de gik over Kildeporten; derpaa gik de lige ud op ad Trinene til Davidsbyen, ad Opgangen paa Muren oven for Davids Palads hen til Vandporten mod Øst.
38 Ƙungiyar mawaƙa ta biyu suka yi jerin gwano a ɗaya gefen. Na bi su a bisan katangar, tare da rabin mutanen, muka wuce Hasumiya Tanderu zuwa Katanga Mai Faɗi,
Det andet Lovprisningstog, hvor jeg og den anden Halvdel af Folkets Øverster var med, drog til venstre oven paa Muren, over Ovntaarnet til den brede Mur
39 bisa Ƙofar Efraim, Ƙofar Yeshana, Ƙofar Kifi, Hasumiyar Hananel da kuma Hasumiya ɗari, har zuwa Ƙofar Tumaki. A Ƙofar Matsara suka tsaya.
og videre over Efraimsporten, den gamle Port, Fiskeporten, Hanan'eltaarnet og Meataarnet til Faareporten og stillede sig op i Fængselsporten.
40 Ƙungiyoyin mawaƙa biyu da suka yi godiya suka ɗauki wurarensu a gidan Allah, haka ma ni, tare da rabin shugabanni,
Derpaa stillede de to Lovprisningstog sig op i Guds Hus, jeg sammen med Halvdelen af Øversterne
41 da kuma firistoci, Eliyakim, Ma’asehiya, Miniyamin, Mikahiya, Eliyohenai, Zakariya da Hananiya tare da ƙahoninsu,
og Præsterne Eljakim, Ma'aseja, Minjamin, Mika, Eljoenaj, Zekarja, Hananja med Trompeter,
42 haka ma Ma’asehiya, Shemahiya, Eleyazar, Uzzi, Yehohanan, Malkiya, Elam da Ezer. Mawaƙan suka rera waƙoƙi a ƙarƙashin kulawar Yezrahiya.
endvidere Ma'aseja, Sjemaja, El'azar, Uzzi, Johanan, Malkija, Elam og Ezer. Og Sangerne stemte i, ledede af Jizraja.
43 A rana ta uku kuma suka miƙa manyan hadayu, suna farin ciki domin Allah ya ba su farin ciki mai girma. Mata da yara suka yi farin ciki su ma. An ji ƙarar farin ciki da ake yi a Urushalima daga nesa.
Paa den Dag ofrede de store Slagtofre og var glade, thi Gud havde bragt dem stor Glæde; ogsaa Kvinderne og Børnene var glade; og Glæden i Jerusalem hørtes langt bort.
44 A lokacin an naɗa mutane su lura da ɗakunan ajiya don sadakoki, nunan fari da kuma zakka. Daga gonakin garuruwan da suke kewaye za su kawo sassan da Dokar ta umarta zuwa ɗakunan ajiya domin firistoci da Lawiyawa, gama Yahuda ya ji daɗin aikin firistoci da Lawiyawa.
Paa den Dag indsattes der Mænd til at have Tilsyn med de Kamre, der brugtes til Forraadene, Offerydelserne, Førstegrøden og Tienden, for i dem at opsamle de i Loven foreskrevne Afgifter til Præsterne og Leviterne fra de forskellige Bymarker, thi Juda glædede sig over Præsterne og Leviterne, der gjorde Tjeneste;
45 Sun yi hidimar Allahnsu da kuma hidimar tsarkakewa, kamar yadda mawaƙa da matsaran ƙofofi suka yi, bisa ga umarnin Dawuda da ɗansa Solomon.
og disse tog Vare paa, hvad der var at varetage for deres Gud og ved Renselsen, ligesom ogsaa Sangerne og Dørvogterne gjorde deres Gerning efter Davids og hans Søn Salomos Bud.
46 Gama tun dā, a kwanakin Dawuda da Asaf, akwai masu bi da mawaƙa da kuma na waƙoƙin yabo da na godiya ga Allah.
Thi allerede paa Davids Tid var Asaf Leder for Sangerne og for Lov— og Takkesangene til Gud.
47 Saboda haka a kwanakin Zerubbabel da Nehemiya, dukan Isra’ila suka ba da sashe na kowace rana domin mawaƙa da matsaran ƙofofi. Suka kuma keɓe sashe don sauran Lawiyawa, Lawiyawan kuma suka keɓe sashe don zuriyar Haruna.
Hele Israel gav paa Zerubbabels og Nehemias's Tid Afgifter til Sangerne og Dørvogterne, efter som det krævedes Dag for Dag; og de gav Leviterne Helliggaver, og Leviterne gav Arons Sønner Helliggaver.