< Nehemiya 11 >

1 To, fa, shugabannin mutane suka zauna a Urushalima, sauran mutanen kuma suka jefa ƙuri’a don su kawo mutum ɗaya daga kowane mutum goma don su zauna a Urushalima, birni mai tsarki, yayinda sauran tara suka zauna a garuruwansu.
Och öfverstarna för folket bodde i Jerusalem; men det andra folket kastade lott derom, att af tio skulle en del draga till Jerusalem, den helga staden, till att bo der, och nio delar i städerna.
2 Sai mutane suka yaba wa dukan mutanen da suka ba da kansu da yardar rai su zauna a Urushalima.
Och folket välsignade alla de män, som friviljoge voro till att bo i Jerusalem.
3 Waɗannan su ne shugabannin yankuna waɗanda suka zauna a Urushalima (ko da yake waɗansu Isra’ilawa, da firistoci, da Lawiyawa, da ma’aikatan haikali, da zuriyar bayin Solomon, suka yi zama a cikin garuruwan Yahuda, kowanne a mallakarsa cikin garuruwa dabam-dabam,
Desse äro hufvuden i landskapen, de som i Jerusalem bodde; men i Juda städer bodde hvar och en på sina ägor, som i deras städer voro; nämliga Israel, Presterna, Leviterna, Nethinim och Salomos tjenares barn.
4 yayinda sauran mutane daga Yahuda da Benyamin suka zauna a Urushalima). Daga zuriyar Yahuda akwai, Atahiya ɗan Uzziya, ɗan Zakariya, ɗan Amariya, ɗan Shefatiya, ɗan Mahalalel, wani zuriyar Ferez;
Och i Jerusalem bodde någre af Juda barn, och BenJamin. Af Juda barn: Athaja, Ussia son, Zacharia sons, Amaria sons, Sephatja sons, Mahalaleels sons, af Parez barn;
5 da Ma’asehiya ɗan Baruk, ɗan Kol-Hoze, ɗan Hazahiya, ɗan Adahiya, ɗan Yohiyarib, ɗan Zakariya, zuriyar Shela.
Och Maaseja, Baruchs son. CholHose sons, Hasaja sons, Adaja sons, Jojaribs sons, Zacharia sons, Siloni sons.
6 Zuriyar Ferez waɗanda suka zauna a Urushalima sun kai ɗari huɗu da sittin da takwas, dukansu kuwa muhimman mutane ne.
All Parez barn, som i Jerusalem bodde, voro fyrahundrad åtta och sextio dugelige män.
7 Daga zuriyar Benyamin akwai, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Yowed, ɗan Fedahiya, ɗan Kolahiya, ɗan Ma’asehiya, ɗan Itiyel, ɗan Yeshahiya,
Desse äro BenJamins barn: Sallu, Mesullams son, Joeds sons, Pedaja sons, Kolaja sons, Maasesa sons, Ithiels sons, Jesaja sons.
8 da mabiyansa, Gabbai da Sallai, mutum 928.
Och efter honom Gabbai, Sallia, niohundrad åtta och tjugu.
9 Yowel ɗan Zikri ne babban shugabansu, Yahuda kuma ɗan Hassenuwa, ya shugabanci Yanki na Biyu na birni.
Och Joel, Sichri son, var deras föreståndare; och Juda, Hasuna son, öfver den andra delen i stadenom.
10 Daga firistoci akwai, Yedahiya ɗan Yohiyarib, da Yakin,
Af Presterna bodde: Jedaja, Jojaribs son, Jachin.
11 da Serahiya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, mai lura da abubuwa a cikin gidan Allah,
Seraja, Hilkia son, Mesullams sons, Zadoks sons, Merajoths sons, Ahitobs sons, var Förste i Guds hus.
12 tare da’yan’uwansu waɗanda suke aiki domin haikali, su 822 ne. Akwai kuma Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Felaliya, ɗan Amzi, ɗan Zakariya, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya,
Och deras bröder, som i husena skaffa hade, voro åttahundrad två och tjugu. Och Adaja, Jerohams son, Pelalja sons, Amzi sons, Zacharia sons, Pashurs sons, Malchija sons,
13 da’yan’uwansa waɗanda suke shugabannin iyalai, su 242. Sai kuma Amashsai ɗan Azarel, ɗan Ahzai, ɗan Meshillemot, ɗan Immer,
Och hans bröder öfverstar ibland fäderna, voro tuhundrad två och fyratio; och Amassai, Asareels son, Ahsai sons, Mesillemoths sons, Immers sons,
14 da’yan’uwansa, su 128 ne muhimman mutane. Babban shugabansu shi ne Zabdiyel ɗan Haggedolim.
Och deras bröder, väldige män, voro hundrade åtta och tjugu; och deras föreståndare var Sabdiel, Gedolims son.
15 Daga Lawiyawa kuwa akwai, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, ɗan Bunni,
Af Leviterna: Semaja, Hasubs son, Asrikams sons, Hasabia sons, Bunni sons;
16 da Shabbetai, da kuma Yozabad, biyu cikin shugabanni Lawiyawa waɗanda suke da nawayar aiki waje da gidan Allah.
Och Sabbethai, och Josabad af Leviternas öfverstar, uti de ärende, som utantill voro vid Guds hus;
17 Sai kuma Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zabdi, ɗan Asaf, shugaban da yake bi da hidimar godiya da kuma addu’a. Sai Bakbukiya, na biyu a cikin’yan’uwansa; da Abda ɗan Shammuwa, ɗan Galal, ɗan Yedutun.
Och Matthania, Micha son, Sabdi sons, Assaphs sons, den hufvudet var till att begynna tacksägelse i bönene; och Bakbukia den andre ibland sina bröder; och Abda, Sammua son, Galals sons, Jeduthuns sons.
18 Lawiyawan da suke cikin birni mai tsarki sun kai 284.
Alle Leviterna i dem helga stadenom voro tuhundrad fyra och åttatio.
19 Matsaran ƙofofi kuwa su ne, Akkub, da Talmon, da’yan’uwansu waɗanda suke tsaron ƙofofi, su 172 ne.
Och dörravaktarena, Akkub och Talmon, och deras bröder, som vid dörrarna vaktade, voro hundrade två och sjutio.
20 Sauran Isra’ilawa tare da firistoci, da Lawiyawa sun kasance a dukan garuruwan Yahuda, kowanne a mallakar kakansa.
Men de andre Israel, Prester och Leviter, voro uti alla Juda städer, hvar och en i sinom arfvedel.
21 Ma’aikatan haikali sun zauna a kan tudun Ofel. Ziha, da Gishfa ne suke lura da su.
Och de Nethinim bodde i Ophel; och Ziha, och Gispa hörde till de Nethinim.
22 Babban shugaban Lawiyawa a Urushalima shi ne Uzzi ɗan Bani, ɗan Hashabiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mika. Uzzi yana ɗaya daga zuriyar Asaf, waɗanda suke mawaƙan da suke da nawayar hidima a gidan Allah.
Föreståndaren öfver de Leviter i Jerusalem var Ussi, Bani son, Hasabia sons, Mattania sons, Micha sons. Utaf Assaphs barn voro sångare vid tjensten i Guds hus;
23 Mawaƙa sun bi umarnan sarki, a kan abin da za su yi kowace rana.
Förty Konungens bud var öfver dem, att sångarena skulle handla troliga, hvar och en på den dag, som honom borde.
24 Fetahahiya ɗan Meshezabel, ɗaya daga zuriyar Zera ɗan Yahuda ne, wakilin sarki cikin dukan al’amuran da suka shafi mutane.
Och Petahja, Mesesabeels son, af Serahs barn, Juda sons, var i Konungens stad i all ärende till folket.
25 Game da ƙauyukan da filayensu, waɗansu mutanen Yahuda suka zauna a Kiriyat Arba da ƙauyukanta, da Dibon da ƙauyukanta, da Yekabzeyel da ƙauyukanta.
Och Juda barn, som ute voro på bygdene i sin land, bodde somlige i KiriathArba, och i dess döttrom, och i Dibon, och i dess döttrom, och i Kabzeel, och dess döttrom.
26 Akwai su kuma a Yeshuwa, da Molada, da Bet-Felet,
Och i Jesua, Molada, BethPhalet,
27 da Hazar Shuwal, da Beyersheba da ƙauyukanta.
HazarSual, BerSeba, och dess döttrom,
28 Akwai su a Ziklag, da Mekona da ƙauyukanta.
Och i Ziklag, och Mechona, och dess döttrom,
29 Suna nan kuma a En Rimmon, da Zora, da Yarmut,
Och i EnRimmon, Sarega, Jarmuth,
30 da Zanowa, da Adullam da ƙauyukansu, da Lakish da gonakinta, da kuma Azeka da ƙauyukanta. Saboda haka sun yi zama tun daga Beyersheba har zuwa Kwarin Hinnom.
Sanoah, Adullam, och dess döttrom; i Lachis, och på dess mark; i Aseka, och i dess döttrom. Och de lägrade sig, allt ifrå BerSeba intill Hinnoms dal.
31 Zuriyar mutanen Benyamin daga Geba sun zauna a Mikmash, da Aiya, da Betel da ƙauyukanta,
Men BenJamins barn af Geba bodde i Michmas, Aija, BethEl och dess döttrar,
32 da Anatot, da Nob, da Ananiya,
Och i Anathoth, Nob, Anania,
33 da Hazor, da Rama, da Gittayim,
Hazor, Rama, Gittaim,
34 da Hadid, da Zeboyim, da Neballat,
Hadid, Zeboim, Neballat,
35 da Lod, da Ono, da kuma a Kwarin Masu sana’a.
Lod, Ono, i timberdalenom.
36 Waɗansu gundumomin Lawiyawan Yahuda sun zauna a Benyamin.
Och somlige Leviterna, som del hade i Juda, bodde ibland BenJamin.

< Nehemiya 11 >