< Nehemiya 11 >

1 To, fa, shugabannin mutane suka zauna a Urushalima, sauran mutanen kuma suka jefa ƙuri’a don su kawo mutum ɗaya daga kowane mutum goma don su zauna a Urushalima, birni mai tsarki, yayinda sauran tara suka zauna a garuruwansu.
Os príncipes do povo viviam em Jerusalém. O resto do povo também lançou sortes para trazer um de dez para morar em Jerusalém, a cidade santa, e nove partes nas outras cidades.
2 Sai mutane suka yaba wa dukan mutanen da suka ba da kansu da yardar rai su zauna a Urushalima.
O povo abençoou todos os homens que voluntariamente se ofereceram para morar em Jerusalém.
3 Waɗannan su ne shugabannin yankuna waɗanda suka zauna a Urushalima (ko da yake waɗansu Isra’ilawa, da firistoci, da Lawiyawa, da ma’aikatan haikali, da zuriyar bayin Solomon, suka yi zama a cikin garuruwan Yahuda, kowanne a mallakarsa cikin garuruwa dabam-dabam,
Now estes são os chefes da província que viviam em Jerusalém; mas nas cidades de Judá, todos viviam em sua posse em suas cidades - Israel, os sacerdotes, os levitas, os servos do templo e os filhos dos servos de Salomão.
4 yayinda sauran mutane daga Yahuda da Benyamin suka zauna a Urushalima). Daga zuriyar Yahuda akwai, Atahiya ɗan Uzziya, ɗan Zakariya, ɗan Amariya, ɗan Shefatiya, ɗan Mahalalel, wani zuriyar Ferez;
Some dos filhos de Judá e dos filhos de Benjamim viviam em Jerusalém. dos filhos de Judá: Ataías, filho de Uzias, filho de Zacarias, filho de Amarias, filho de Sefatias, filho de Maalalel, dos filhos de Perez;
5 da Ma’asehiya ɗan Baruk, ɗan Kol-Hoze, ɗan Hazahiya, ɗan Adahiya, ɗan Yohiyarib, ɗan Zakariya, zuriyar Shela.
e Maaséias, filho de Baruque, filho de Colhozeh, filho de Hazaías, filho de Adaías, filho de Joiaribe, filho de Zacarias, filho de Silonita.
6 Zuriyar Ferez waɗanda suka zauna a Urushalima sun kai ɗari huɗu da sittin da takwas, dukansu kuwa muhimman mutane ne.
Todos os filhos de Perez que viviam em Jerusalém eram quatrocentos e sessenta e oito homens valentes.
7 Daga zuriyar Benyamin akwai, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Yowed, ɗan Fedahiya, ɗan Kolahiya, ɗan Ma’asehiya, ɗan Itiyel, ɗan Yeshahiya,
Estes são os filhos de Benjamim: Sallu, filho de Meshullam, filho de Joede, filho de Pedaías, filho de Colaías, filho de Maaséias, filho de Itiel, filho de Jesaías.
8 da mabiyansa, Gabbai da Sallai, mutum 928.
Depois dele, Gabbai e Sallai, novecentos e vinte e oito.
9 Yowel ɗan Zikri ne babban shugabansu, Yahuda kuma ɗan Hassenuwa, ya shugabanci Yanki na Biyu na birni.
Joel, filho de Zicri, foi seu superintendente; e Judá, filho de Hassenuah, foi o segundo sobre a cidade.
10 Daga firistoci akwai, Yedahiya ɗan Yohiyarib, da Yakin,
Dos sacerdotes: Jedaías, filho de Joiaribe, Jachin,
11 da Serahiya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, mai lura da abubuwa a cikin gidan Allah,
Seraías, filho de Hilquias, filho de Mesulão, filho de Zadoque, filho de Meraiote, filho de Aitube, o governante da casa de Deus,
12 tare da’yan’uwansu waɗanda suke aiki domin haikali, su 822 ne. Akwai kuma Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Felaliya, ɗan Amzi, ɗan Zakariya, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya,
e seus irmãos que fizeram o trabalho da casa, oitocentos e vinte e dois; e Adaías, filho de Jeroham, filho de Pelalia, filho de Amzi, filho de Zacarias, filho de Pashur, filho de Malchijah,
13 da’yan’uwansa waɗanda suke shugabannin iyalai, su 242. Sai kuma Amashsai ɗan Azarel, ɗan Ahzai, ɗan Meshillemot, ɗan Immer,
e seus irmãos, chefes de família dos pais, duzentos e quarenta e dois; e Amashsai, filho de Azarel, filho de Ahzai, filho de Meshillemoth, filho de Immer,
14 da’yan’uwansa, su 128 ne muhimman mutane. Babban shugabansu shi ne Zabdiyel ɗan Haggedolim.
e seus irmãos, poderosos homens de valor, cento e vinte e oito; e seu superintendente era Zabdiel, filho de Haggedolim.
15 Daga Lawiyawa kuwa akwai, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, ɗan Bunni,
Dos Levitas: Shemaiah, filho de Hasshub, filho de Azrikam, filho de Hashabiah, filho de Bunni;
16 da Shabbetai, da kuma Yozabad, biyu cikin shugabanni Lawiyawa waɗanda suke da nawayar aiki waje da gidan Allah.
e Shabbethai e Jozabad, dos chefes dos levitas, que tinham a supervisão dos negócios externos da casa de Deus;
17 Sai kuma Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zabdi, ɗan Asaf, shugaban da yake bi da hidimar godiya da kuma addu’a. Sai Bakbukiya, na biyu a cikin’yan’uwansa; da Abda ɗan Shammuwa, ɗan Galal, ɗan Yedutun.
e Mattaniah o filho de Mica, o filho de Zabdi, o filho de Asafe, que foi o chefe para iniciar a ação de graças em oração, e Bakbukiah, o segundo entre seus irmãos; e Abda o filho de Shammua, o filho de Galal, o filho de Jeduthun.
18 Lawiyawan da suke cikin birni mai tsarki sun kai 284.
Todos os levitas da cidade santa eram duzentos e oitenta e quatro.
19 Matsaran ƙofofi kuwa su ne, Akkub, da Talmon, da’yan’uwansu waɗanda suke tsaron ƙofofi, su 172 ne.
Moreover os porteiros, Akkub, Talmon, e seus irmãos, que vigiavam os portões, eram cento e setenta e dois.
20 Sauran Isra’ilawa tare da firistoci, da Lawiyawa sun kasance a dukan garuruwan Yahuda, kowanne a mallakar kakansa.
Os resíduos de Israel, dos sacerdotes e dos levitas estavam em todas as cidades de Judá, todos em sua herança.
21 Ma’aikatan haikali sun zauna a kan tudun Ofel. Ziha, da Gishfa ne suke lura da su.
Mas os servos do templo viviam em Ofel; e Ziha e Gishpa estavam sobre os servos do templo.
22 Babban shugaban Lawiyawa a Urushalima shi ne Uzzi ɗan Bani, ɗan Hashabiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mika. Uzzi yana ɗaya daga zuriyar Asaf, waɗanda suke mawaƙan da suke da nawayar hidima a gidan Allah.
O supervisor também dos Levitas em Jerusalém era Uzzi, filho de Bani, filho de Hashabiah, filho de Mattaniah, filho de Mica, dos filhos de Asafe, os cantores, estava encarregado dos negócios da casa de Deus.
23 Mawaƙa sun bi umarnan sarki, a kan abin da za su yi kowace rana.
Pois havia um mandamento do rei a respeito deles, e uma provisão acertada para os cantores, como todos os dias era exigido.
24 Fetahahiya ɗan Meshezabel, ɗaya daga zuriyar Zera ɗan Yahuda ne, wakilin sarki cikin dukan al’amuran da suka shafi mutane.
Pethahiah, filho de Meshezabel, dos filhos de Zerah, filho de Judá, estava às mãos do rei em todos os assuntos relativos ao povo.
25 Game da ƙauyukan da filayensu, waɗansu mutanen Yahuda suka zauna a Kiriyat Arba da ƙauyukanta, da Dibon da ƙauyukanta, da Yekabzeyel da ƙauyukanta.
Quanto às aldeias com seus campos, algumas das crianças de Judá viviam em Kiriath Arba e suas cidades, em Dibon e suas cidades, em Jekabzeel e suas aldeias,
26 Akwai su kuma a Yeshuwa, da Molada, da Bet-Felet,
in Jeshua, em Moladah, Beth Pelet,
27 da Hazar Shuwal, da Beyersheba da ƙauyukanta.
em Hazar Shual, em Beersheba e suas cidades,
28 Akwai su a Ziklag, da Mekona da ƙauyukanta.
em Ziklag, em Meconah e em suas cidades,
29 Suna nan kuma a En Rimmon, da Zora, da Yarmut,
in En Rimmon, em Zorah, em Jarmuth,
30 da Zanowa, da Adullam da ƙauyukansu, da Lakish da gonakinta, da kuma Azeka da ƙauyukanta. Saboda haka sun yi zama tun daga Beyersheba har zuwa Kwarin Hinnom.
Zanoah, Adullam e suas aldeias, Lachish e seus campos, e Azekah e suas cidades. Assim, eles acamparam de Beersheba até o vale de Hinnom.
31 Zuriyar mutanen Benyamin daga Geba sun zauna a Mikmash, da Aiya, da Betel da ƙauyukanta,
As crianças de Benjamin também viveram de Geba em diante, em Michmash e Aija, e em Betel e suas cidades,
32 da Anatot, da Nob, da Ananiya,
at Anathoth, Nob, Ananiah,
33 da Hazor, da Rama, da Gittayim,
Hazor, Ramah, Gittaim,
34 da Hadid, da Zeboyim, da Neballat,
Hadid, Zeboim, Neballat,
35 da Lod, da Ono, da kuma a Kwarin Masu sana’a.
Lod, e Ono, o vale dos artesãos.
36 Waɗansu gundumomin Lawiyawan Yahuda sun zauna a Benyamin.
Dos Levitas, certas divisões em Judah se estabeleceram no território de Benjamin.

< Nehemiya 11 >