< Nehemiya 11 >

1 To, fa, shugabannin mutane suka zauna a Urushalima, sauran mutanen kuma suka jefa ƙuri’a don su kawo mutum ɗaya daga kowane mutum goma don su zauna a Urushalima, birni mai tsarki, yayinda sauran tara suka zauna a garuruwansu.
Et les chefs du peuple habitaient à Jérusalem: et le reste du peuple jeta le sort pour qu’un sur dix vienne habiter à Jérusalem, la ville sainte, et que les neuf [autres] parties [demeurent] dans les villes.
2 Sai mutane suka yaba wa dukan mutanen da suka ba da kansu da yardar rai su zauna a Urushalima.
Et le peuple bénit tous les hommes qui s’offrirent volontairement pour habiter à Jérusalem.
3 Waɗannan su ne shugabannin yankuna waɗanda suka zauna a Urushalima (ko da yake waɗansu Isra’ilawa, da firistoci, da Lawiyawa, da ma’aikatan haikali, da zuriyar bayin Solomon, suka yi zama a cikin garuruwan Yahuda, kowanne a mallakarsa cikin garuruwa dabam-dabam,
Or ce sont ici les chefs de la province qui habitèrent à Jérusalem; mais, dans les villes de Juda, habitèrent, chacun dans sa possession, dans leurs villes, Israël, les sacrificateurs, et les lévites, et les Nethiniens, et les fils des serviteurs de Salomon.
4 yayinda sauran mutane daga Yahuda da Benyamin suka zauna a Urushalima). Daga zuriyar Yahuda akwai, Atahiya ɗan Uzziya, ɗan Zakariya, ɗan Amariya, ɗan Shefatiya, ɗan Mahalalel, wani zuriyar Ferez;
Et à Jérusalem habitèrent des fils de Juda, et des fils de Benjamin. – Des fils de Juda: Athaïa, fils d’Ozias, fils de Zacharie, fils d’Amaria, fils de Shephatia, fils de Mahalaleël, d’entre les fils de Pérets;
5 da Ma’asehiya ɗan Baruk, ɗan Kol-Hoze, ɗan Hazahiya, ɗan Adahiya, ɗan Yohiyarib, ɗan Zakariya, zuriyar Shela.
et Maascéïa, fils de Baruc, fils de Col-Hozé, fils de Hazaïa, fils d’Adaïa, fils de Joïarib, fils de Zacharie, d’entre les Shilonites.
6 Zuriyar Ferez waɗanda suka zauna a Urushalima sun kai ɗari huɗu da sittin da takwas, dukansu kuwa muhimman mutane ne.
Tous les fils de Pérets qui habitèrent à Jérusalem: 468 hommes vaillants.
7 Daga zuriyar Benyamin akwai, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Yowed, ɗan Fedahiya, ɗan Kolahiya, ɗan Ma’asehiya, ɗan Itiyel, ɗan Yeshahiya,
– Et ce sont ici les fils de Benjamin: Sallu, fils de Meshullam, fils de Joëd, fils de Pedaïa, fils de Kolaïa, fils de Maascéïa, fils d’Ithiel, fils d’Ésaïe;
8 da mabiyansa, Gabbai da Sallai, mutum 928.
et après lui, Gabbaï, Sallaï: 928;
9 Yowel ɗan Zikri ne babban shugabansu, Yahuda kuma ɗan Hassenuwa, ya shugabanci Yanki na Biyu na birni.
et Joël, fils de Zicri, était préposé sur eux, et Juda, fils d’Hassenua, en second, sur la ville.
10 Daga firistoci akwai, Yedahiya ɗan Yohiyarib, da Yakin,
Des sacrificateurs: Jedahia, [fils de] Joïarib, Jakin;
11 da Serahiya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, mai lura da abubuwa a cikin gidan Allah,
Seraïa, fils de Hilkija, fils de Meshullam, fils de Tsadok, fils de Meraïoth, fils d’Akhitub, prince de la maison de Dieu;
12 tare da’yan’uwansu waɗanda suke aiki domin haikali, su 822 ne. Akwai kuma Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Felaliya, ɗan Amzi, ɗan Zakariya, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya,
et leurs frères qui faisaient les travaux de la maison: 822. Et Adaïa, fils de Jerokham, fils de Pelalia, fils d’Amtsi, fils de Zacharie, fils de Pashkhur, fils de Malkija,
13 da’yan’uwansa waɗanda suke shugabannin iyalai, su 242. Sai kuma Amashsai ɗan Azarel, ɗan Ahzai, ɗan Meshillemot, ɗan Immer,
et ses frères, chefs des pères: 242. Et Amassaï, fils d’Azareël, fils d’Akhzaï, fils de Meshillémoth, fils d’Immer;
14 da’yan’uwansa, su 128 ne muhimman mutane. Babban shugabansu shi ne Zabdiyel ɗan Haggedolim.
et leurs frères, hommes forts et vaillants: 128; et Zabdiel, fils de Guedolim, était préposé sur eux.
15 Daga Lawiyawa kuwa akwai, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, ɗan Bunni,
Et des lévites: Shemahia, fils de Hashub, fils d’Azrikam, fils de Hashabia, fils de Bunni;
16 da Shabbetai, da kuma Yozabad, biyu cikin shugabanni Lawiyawa waɗanda suke da nawayar aiki waje da gidan Allah.
et Shabthaï et Jozabad, d’entre les chefs des lévites, [préposés] sur l’ouvrage extérieur de la maison de Dieu;
17 Sai kuma Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zabdi, ɗan Asaf, shugaban da yake bi da hidimar godiya da kuma addu’a. Sai Bakbukiya, na biyu a cikin’yan’uwansa; da Abda ɗan Shammuwa, ɗan Galal, ɗan Yedutun.
et Matthania, fils de Michée, fils de Zabdi, fils d’Asaph, le chef, qui entonnait la louange à la prière, et Bakbukia, le second d’entre ses frères, et Abda, fils de Shammua, fils de Galal, fils de Jeduthun.
18 Lawiyawan da suke cikin birni mai tsarki sun kai 284.
Tous les lévites dans la ville sainte: 284.
19 Matsaran ƙofofi kuwa su ne, Akkub, da Talmon, da’yan’uwansu waɗanda suke tsaron ƙofofi, su 172 ne.
Et les portiers, Akkub, Talmon, et leurs frères, qui étaient de garde aux portes, 172.
20 Sauran Isra’ilawa tare da firistoci, da Lawiyawa sun kasance a dukan garuruwan Yahuda, kowanne a mallakar kakansa.
Et le reste d’Israël, les sacrificateurs, [et] les lévites, [habitèrent] dans toutes les villes de Juda, chacun dans son héritage.
21 Ma’aikatan haikali sun zauna a kan tudun Ofel. Ziha, da Gishfa ne suke lura da su.
Et les Nethiniens habitèrent Ophel; et Tsikha et Guishpa étaient [préposés] sur les Nethiniens.
22 Babban shugaban Lawiyawa a Urushalima shi ne Uzzi ɗan Bani, ɗan Hashabiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mika. Uzzi yana ɗaya daga zuriyar Asaf, waɗanda suke mawaƙan da suke da nawayar hidima a gidan Allah.
Et celui qui était préposé sur les lévites à Jérusalem était Uzzi, fils de Bani, fils de Hashabia, fils de Matthania, fils de Michée, des fils d’Asaph, les chantres pour l’œuvre de la maison de Dieu.
23 Mawaƙa sun bi umarnan sarki, a kan abin da za su yi kowace rana.
Car c’était le commandement du roi à leur égard, et il y avait un fixe pour les chantres, pour chaque jour ce qu’il fallait.
24 Fetahahiya ɗan Meshezabel, ɗaya daga zuriyar Zera ɗan Yahuda ne, wakilin sarki cikin dukan al’amuran da suka shafi mutane.
Et Pethakhia, fils de Meshézabeël, des fils de Zérakh, fils de Juda, était auprès du roi pour toutes les affaires du peuple.
25 Game da ƙauyukan da filayensu, waɗansu mutanen Yahuda suka zauna a Kiriyat Arba da ƙauyukanta, da Dibon da ƙauyukanta, da Yekabzeyel da ƙauyukanta.
Et pour ce qui est des hameaux de leurs campagnes, [quelques-uns] des fils de Juda habitèrent à Kiriath-Arba et dans les villages de son ressort, et à Dibon et dans les villages de son ressort, et à Jekabtsëel et dans ses hameaux,
26 Akwai su kuma a Yeshuwa, da Molada, da Bet-Felet,
et à Jéshua, et à Molada, et à Beth-Péleth,
27 da Hazar Shuwal, da Beyersheba da ƙauyukanta.
et à Hatsar-Shual, et à Beër-Shéba et dans les villages de son ressort,
28 Akwai su a Ziklag, da Mekona da ƙauyukanta.
et à Tsiklag, et à Mecona et dans les villages de son ressort,
29 Suna nan kuma a En Rimmon, da Zora, da Yarmut,
et à En-Rimmon, et à Tsorha, et à Jarmuth,
30 da Zanowa, da Adullam da ƙauyukansu, da Lakish da gonakinta, da kuma Azeka da ƙauyukanta. Saboda haka sun yi zama tun daga Beyersheba har zuwa Kwarin Hinnom.
Zanoakh, Adullam et leurs hameaux, Lakis et ses campagnes, Azéka et les villages de son ressort; et ils demeurèrent depuis Beër-Shéba jusqu’à la vallée de Hinnom.
31 Zuriyar mutanen Benyamin daga Geba sun zauna a Mikmash, da Aiya, da Betel da ƙauyukanta,
Et les fils de Benjamin [s’établirent], depuis Guéba, [à] Micmash, et Aïa, et Béthel et les villages de son ressort,
32 da Anatot, da Nob, da Ananiya,
Anathoth, Nob, Anania,
33 da Hazor, da Rama, da Gittayim,
Hatsor, Rama, Guitthaïm,
34 da Hadid, da Zeboyim, da Neballat,
Hadid, Tseboïm, Neballath,
35 da Lod, da Ono, da kuma a Kwarin Masu sana’a.
Lod et Ono, la vallée des artisans.
36 Waɗansu gundumomin Lawiyawan Yahuda sun zauna a Benyamin.
Et d’entre les Lévites, il y eut des divisions de Juda [qui s’établirent] en Benjamin.

< Nehemiya 11 >